Gwamna ya yi wa iyalan ’yan wasan Kano da suka rasu a hatsari goma ta arziki
Published: 6th, August 2025 GMT
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayar da kyautar fuloti da kuɗi naira miliyan biyar ga kowane ɗaya daga cikin iyalan tawagar ’yan wasan nan na Kano 22 da suka rasu a wani mummunan haɗarin mota da ya auku a watan Yuni.
Mai bai wa gwamnan shawara kan yaɗa labarai, Ibrahim Adam, ne ya tabbatar da wannan kyauta cikin wani saƙo da ya wallafa a Facebook a wannan Larabar.
“Mai girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bai wa iyalan ’yan wasan da suka rasu fuloti ɗaya da kuma naira miliyan biyar kowannensu,” in ji sanarwar.
Aminiya ta ruwaito cewa, tawagar ’yan wasan da suka rasu ta yi hatsari ne a yayin da suke dawowa daga gasar wasannin ƙasa ta National Sports Festival da aka gudanar a Jihar Ogun.
Tawagar da lamarin ya rutsa da ita ta ƙunshi ’yan wasa, masu horarwa, mataimakansu, jami’an lafiya, direbobi, injiniyoyi da kuma ɗan jarida.
Ajali ya katse musu hanzari ne bayan samun nasarori daban-daban a gasar ta National Sports Festival da suka haɗa da sarƙoƙin zinare 6, azurfa 13 da na tagulla 10 da suka lashe.
Ana iya tuna cewa, mummunan lamarin ya auku ne a garin Dakatsalle da ke ƙaramar hukumar Bebeji, kimanin kilomita 50 daga Kano, a yayin da ya rage ƙiris tawagar ta ƙarasa gida.
Tun a wancan lokaci, jama’a daga ciki da wajen Jihar Kano suka riƙa jimami da bayyana alhini, musamman duba da irin gudummawar da ’yan wasan suka bayar kafin rasuwarsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan wasa Hatsari Jihar Kano da suka rasu
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya bai wa ’yan wasan ƙwallon kwandon mata kyautar Dala dubu 100 da gidaje
Shugaba Bola Tinubu ya bai wa ’yan wasan ƙwallon kwandon mata D’Tigress kyautar Dala dubu 100 da gidaje da lambar girmamawa ta OON, a matsayin karramawa bayan lashe kofin gasar ta bana.
Shugaban ya kuma ba masu horar da ’yan wasan dala 50,000 kowannensu.
Gwamnatin Kano ta karɓi rahoton binciken Kwamishinan da ya yi belin Danwawu WAEC ta saki sakamakon jarabawar 2025Wannan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan shugaban ya ’yan wasan ƙwallon ƙafa mata wata Super Falcons makamanciyar wannan kyautar ta dala 100,000 da lambar girma.
A wannan Litinin din ce tawagar ’yan wasan ƙwallon kwando ta mata ta Nijeriya ta koma ƙasar bayan lashe gasar ƙwallon kwando ta mata ta Afirka, wato Afrobasket.
Tawagar ta D’Tigress ta samu gagarumar tarba daga masoya ƙwallon kwando a Nijeriya, lokacin da suka sauka a filin jirgin sama na Abuja.
Ministar Mata Iman Sulaiman Ibrahim da takwararta ta al’adu, Hannatu Musawa ne suka yi wa tagawar rakiya tun daga birnin Abidjan zuwa Abuja.
A ranar Lahadi ne tawagar D’Tigress ta lashe gasar ƙwallon kwando ta mata ta Afirka, bayan doke Mali da ci 78-64 da aka fafata a Ivory Coast.
Wannan ne karo na bakwai da tawagar Nijeriya ta lashe kofin gasar a tarihi, wanda kuma shi ne na biyar a jere da ta ɗauka.