Duk wanda ya haka rijiyar burtsatse a Lekki ruwan masai yake sha – Gwamnatin Legas
Published: 6th, August 2025 GMT
Gwamnatin jihar Legas ta yi gargadin cewa akwai yiwuwar duk wanda yake haka rijiyar burtsatse a unguwar masu hannu da shuni ta Lekki da ke jihar, ruwan masai yake sha.
Babban Sakatare a ofishin da ke kula da magudanun ruwa da tsaftar ruwan sha a jihar, Mahmood Adegbite ne ya bayyana haka yayin wani taron masu ruwa da tsaki kan samar da ruwan sha a jihar a kwanakin baya.
Mahmood ya kuma ce gurbataccen ruwan sha a unguwar zai iya haifar da barazanar lafiya matukar ba a bi hanyoyin da suka dace wajen tsaftace shi ba.
Ya ce, “Game da batun kula da tsaftar muhalli kuwa, zan iya cewa duk wanda ya haka burtsatse a yankin unguwar Lekki, watakila yana shan ruwan da zan iya kira da ruwan masai ne.
“Amma idan muka yi kokari wajen sarrafa dattin da yake fitowa daga yankin kamar yadda muke yunkurin yi a yanzu haka, za mu dakile duk wata cuta da za ta iya yaduwa sanadiyyar rashin tsafta,” in ji shi.
Sai dai ya ce akwai jan aiki a gaban jihar wajen magance matsalar ambaliyar ruwa, yana mai cewa ko a watan da ya gabata sai da aka samu ambaliyar a wasu sassan jihar, sabanin a watan Agustan da aka saba gani a shekarun baya.
“Maganar gaskiya a bangaren ambaliya, duk da muna namijin kokari wajen magance ta, amma har yanzu akwai jan aiki a gabanmu kafin mu iya magance matsalar baki daya,” in ji Babban Sakataren.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamnatin Legas
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Zamfara Ta Nemi Karin Tallafi Ga ‘Yan Gudun Hijira
Gwamnatin Jihar Zamfara ta roki Hukumar Raya Kasashen Waje ta Kasa (FCDO), Premier Urgence Internationale (PUI), da sauran masu ruwa da tsaki da su kara tallafa wa ‘yan gudun hijirar da ke jihar.
Kwamishinan Bada Agaji na Jiha Alhaji Salisu Musa Tsafe ne ya yi wannan kiran a lokacin da yake jawabi ga mahalarta taron na kwana guda kan shirin ceton rayuka da karfafawa da kuma juriya (LEARP) wanda kungiyar FCDO ta dauki nauyin shiryawa a Abuja.
A wata sanarwa dauke da sa hannun Daraktan Yada Labarai na Ma’aikatar, Bashir Kabiru Ahmad, Kwamishinan ya bayyana cewa a halin yanzu jihar na karbar dubban ‘yan gudun hijira daga al’ummomi sama da 1,008 a fadin kananan hukumomin 14, kamar yadda aka gani a cikin rajistar zamantakewa na jihar.
Alhaji Musa Tsafe ya bayyana cewa, tallafin da ake bukata ya hada da bangarorin Rayuwa, Karfafawa, samun tallafin Kudi da Manufofi da sauran abubuwan da za a iya yi da nufin rage radadin halin da ‘yan gudun hijira ke ciki a jihar.
Alhaji Tsafe ya yabawa abokan aikin raya kasa bisa yadda suke ci gaba da tallafawa ‘yan gudun hijira da sauran marasa galihu a Zamfara.
A cewarsa, aikin da aka tsara domin aiwatar da shi da kungiyar Premier Urgence International (PUI) za ta yi zai kasance muhimmin taimako ga al’ummar jihar Zamfara.
Ya bayyana taron a matsayin wani ci gaba a kokarin jihar na inganta rayuwar ‘yan gudun hijira da marasa galihu musamman mata da yara.
Alhaji Tsafe ya tabbatarwa da abokan huldar cewa jihar Zamfara karkashin Gwamna Dauda Lawal ta samar da tsarin siyasa da samar da yanayin da kungiyoyin agaji ke gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.
REL/AMINU DALHATU.