Gwamnan Kano ya gargaɗi muƙarrabansa bayan murabus ɗin Kwamishina
Published: 6th, August 2025 GMT
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya gargaɗi maƙarrabansa cewa duk wanda ba zai iya sauke nauyin da aka ɗora masa, ya yi murabus.
Wannan gargaɗi na zuwa ne bayan murabus ɗin Kwamishinan Sufuri, Alhaji Ibrahim Namadi, ya yi biyo bayan belin wani da ake zargin dilan miyagun ƙwayoyi, Sulaiman Danwawu.
Wannan lamari ya tayar da ƙura, wanda hakan ya sa Gwamna Abba, ya ɗauki mataki.
A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar, gwamnan ya bayyana rashin jin daɗinsa kan lamarin.
Hakan ta sa ya jaddada buƙatar dukkanin mambobin majalisar da sauran manyan jami’an gwamnati su kasance masu gaskiya da riƙon amana.
“Ba za mu lamunci kowace irin ɗabi’a ta ƙashin kai da za ta ci gaba da lalata ƙimar gwamnatinmu ba,” in ji Gwamnan.
“Dukkanin ma’aikata dole su kasance masu lura da kuma ɗaukar nauyin ayyukansu. Ba ofishinku kawai kuke wakilta ba, kuna wakiltar gwamnatinmu.”
Gwamnan ya ƙara da cewa duk wanda ba zai iya sauke nauyin amanar da aka ɗora masa ba, ya yi murabus da kansa maimakon aikata wani abu da zai ɓata sunan gwamnati.
Ya kuma nanata cewa yaƙi da miyagun ƙwayoyi da sauran munanan ɗabi’u a cikin al’umma yana daga cikin ginshiƙin mulkinsa.
Ya ce duk wanda aka samu yana da hannu kai-tsaye ko a kaikaice wajen taimaka wa masu aikata irin waɗannan laifuka, zai fuskanci hukunci.
“Mun hau mulki da kyakkyawan manufa ta daidaita al’amura, gaskiya da ci gaba a Jihar Kano. Wannan buri ba zai taɓa taɓewa ba,” in ji shi.
Wannan mataki da gwamnan ya ɗauka na zuwa ne a daidai lokacin da matsalar ta’ammali da miyagun ƙwayoyi ke ƙara barazana ga matasa da zaman lafiyar al’umma a jihar.
Gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da adalci, gaskiya da kyakkyawan shugabanci ga al’ummar Jihar Kano.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gargadi Ibrahim Namadi Kwamishina Miyagun ƙwayoyi
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano Ta Aika Dalibai 588 Zuwa Jihohin Arewa 13 A Karkashin Shirin Musanya
Gwamnatin jihar Kano ta aika dalibai 588 zuwa jihohin Arewa 13 a karkashin shirin musayar dalibai na shekarar 2025/2026.
An kai daliban zuwa jihohinsu da suka hada da Adamawa, Bauchi, Gombe, Jigawa, Katsina, Kebbi, Taraba, da Nasarawa. Bugu da kari, an kai dalibai daga Yobe, Kaduna, Sokoto, Borno, da Kwara lafiya zuwa inda suke, yayin da wasu dalibai 78 kuma za a kwashe su zuwa jihohin Neja da Benue a ranar 30 ga Satumba, 2025.
Kano dai na daya daga cikin jihohin Arewa 19 da ke halartar wannan shiri, wanda aka tsara shi domin inganta hadin kan kasa, hadewa da fahimtar al’adu tsakanin jahohin mambobin kungiyar.
Da yake jawabi ga manema labarai bayan tafiyar da daliban, kwamishinan ilimi, Dakta Ali Haruna Makoda, wanda Daraktan sa ido da tantancewa, Auwal Muhammad Mustapha ya wakilta, ya jaddada kudirin gwamnati na tabbatar da tsaro da walwalar daliban.
“Mai girma Gwamna, yana ba mu dukkan kayan aiki da tallafin kudi don saukaka ayyukanmu da kuma tabbatar da cewa an kai daliban jihohinsu lafiya,” inji shi.
Dakta Makoda ya kuma yabawa iyaye da masu ruwa da tsaki bisa hadin kai da goyon bayan da suke bayarwa wajen ganin shirin ya samu nasara.
COV/Khadija Aliyu