Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82
Published: 6th, August 2025 GMT
Ta sake kafa tarihi bayan da jaridar National Concord mallakar MKO Abiola ta naɗa ta a matsayin editan jaridar ta farko, inda A shekarar 1986, aka ɗaga darajarta zuwa matsayin Manajan Darakta kuma Babban Edita mace ta farko da ta riƙe wannan matsayi a tarihin jaridun Nijeriya.
Ta auri MKO Abiola a shekarar 1981, kuma ta tsaya tsayin daka tare da shi wajen gwagwarmayar siyasarsa da rikicin da ya biyo bayan zaɓen 12 ga watan Yuni, inda ta bayar da gagarumar gudunmawa a fagen jarida, tare da shafe kusan shekaru 30 tana jan ragamar kafafen yaɗa labarai a Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Rasuwa
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15
Babban sakatare na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin wato JKS, kana shugaban kasar, Xi Jinping ya bayar da muhimmin umarni game da binciken ra’ayoyin jama’a masu amfani da shafukan Intanet kan aikin tsara shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15 a kwanan nan, inda ya ce, ya kamata aikin tattara ra’ayoyin jama’a ta yanar gizo wajen tsara shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar na 15 ya samu shigar jama’a sosai, kuma ya kasance wani aiki na dimokuradiyya dake shafar dukkan bangarori.
Jama’a sun yi ta ba da shawarwari tare da gabatar da ra’ayoyi masu muhimmanci, wadanda ya kamata sassan da abin ya shafa su yi nazari a hankali tare da shigar da su cikin tsarin. Kuma dole ne kwamitocin JKS da gwamnatoci a dukkannin matakai su bi tsarin da ya shafi al’umma, su gudanar da bincike mai zurfi kan ra’ayoyin jama’a, da sauraron muryoyinsu, da shigar da hikimominsu cikin tsarin, ta yadda za a samar da hadin gwiwa mai karfi don ingnta zamanintarwa irin ta kasar Sin, da ci gaba da tabbatar da cikar burin jama’a na samun ingantacciyar rayuwa.
Daga ranar 20 ga watan Mayu zuwa ranar 20 ga watan Yunin bana, an fara aikin tattara ra’ayoyin jama’a kan tsara shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar na 15 ta yanar gizo, kuma an bullo da shiri na musamman a shafin intanet na Jaridar People’s Daily, da na kamfanin dillancin labarai na Xinhua, da shafin intanet na babban rukunin gidajen rediyo da talbijin na kasar Sin wato CMG, da kuma kan dandalin “Learning Power”, don neman ra’ayoyin jama’a.
Ya zuwa yanzu, aikin ya sami shawarwarin jama’a masu duba shafin intanet sama da miliyan 3, tare da samar da muhimman bayanai don tsara shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar na 15. (Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp