Aminiya:
2025-09-24@12:36:57 GMT

Tinubu ya taya ’yan matan Yobe da suka lashe gasa a Ingila murna

Published: 6th, August 2025 GMT

Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya taya daliban nan ’yan mata ‘yan asalin jihar Yobe su uku da suka lashe gasar harshen Turanci da aka yi a birnin Landan na Burtaniya.

A farkon makon nan ne dai Nafisa Abdullahi Aminu da Rukayya Muhammad Fema da kuma Hadiza Kashim Kalli suka zama zakaru a gasar TeenEagle ta 2025 da aka yi a birnin na Landan.

Ambaliya ta lalata kauyuka 3 a Sakkwato Yadda ’yan bindiga suka sace Zamfarawa 150 a cikin kwana 4

A cikin wata sanarwa daga bakin kakakinsa, Bayo Onanuga, ranar Laraba, Shugaba Tinubu ya ce nasarar ’yan matan abin alfahari ce ga Najeriya.

Tinubu ya kuma yaba wa makarantun da daliban suke karatu, inda ya ce nasarar daliban wata alama ce ta kyau da ingancin karatun Najeriya da suke samar da hazikan dalibai da duniya ke alfahari da su.

Shugaban ya kuma yaba wa daliban tare da shawartar su da su ci gaba da mayar da hankali a kan karatunsu, sannan ya yi musu fatan nasara a rayuwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gasar Turanci

এছাড়াও পড়ুন:

Hisbah ta kama masu safarar mata zuwa Saudiyya a Kano

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama gungun wasu mutane da ake zargi da safarar mata zuwa kasar Saudiyya.

Hisbah ta dakile yunkurin mutanen ne a yayin da suke kokarin safarar wasu mata hudu daga jihohin Kano da Jigawa da Yobe, ta hannun wakilansu da ke sassan kasashen Yammacin Afirka?

Mataimakin Babban Kwamnand Hukumar, Dakta Mujahideen Aminudeen, ya ce masu safarar matan sun yaudarin matan da aka ceto cewa za su yi musu biza zuwa kasar Ghana inda daga nan za su wuce da su zuwa Saudiyya domin sama musu ayyukan yi.

An kana daya daga cikin mutanen ne a ranar Lahadi, wanda hakan ya kai ga cafke shugabansu da ake kira Bashir Sani Ibrahim.

Ballon d’Or: Wa zai lashe kyautar 2025? Yadda aka kashe jami’an tsaro 53 cikin mako biyu NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen Malabu

Uku daga cikin matan masu shekaru 30 sn fito ne daga jihohin Kano da Jigawa a yayin da hudun mai shekara 35 da fito daga Jihar Yobe.

Dakta Aminudeen ya bayyana cewa matan sun biya mutanen Naira milian bibbyu, za su ciko Naira miliiyan 1.5 kowannensu domin sama musu biza.

Ya ce, “Wannan shi ne abin da muke ta gargadin mutane a kai — kar a yarda da tafiya ba tare da sanin inda za a kai su ba. Ana yaudarar mutane, ana kwace musu kuɗinsu, kuma da zarar sun isa ƙasashen waje ana tilasta musu shiga harkar karuwanci, fataucin miyagun ƙwayoyi ko kuma tsunduma cikin rayuwar kunci.”

Ya shawarci ’yan Najeriya da su guji irin waɗannan haɗurran tafiya, yana mai jaddada cewa kuɗin da ake ɓatawa wajen irin wannan safarar ya fi dacewa a saka shi a harkokin kasuwanci a gida.

“Da naira miliyan biyu ko uku da rabi, mutum zai iya fara kasuwanci mai kyau a Najeriya maimakon fadawa tarkon waɗannan miyagun dabaru,” in ji shi.

Ya nuna godiya cewa an samu damar dakile wannan yunkuri, yana mai cewa da masu safarar mutanen sun ci nasara, da lallai matan sun ɓace ba tare da sahu ba.

“Mun tattara bayanansu da fasfofonsu muka mika su ga Hukumar Yaƙi da Safarar Mutane (NAPTIP). Za mu ci gaba da sa ido har sai an kammala bincike kan lamarin,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNGA: Yau Shettima zai gabatar da jawabin Najeriya a MDD
  • NAJERIYA A YAU: Abin Da Doka Ya Ce Kan Kisan Jami’an ‘Yan Sanda
  • CORET Ta Yaba Da Nasarar Shirin Ciyarda Daliban Makarantun Makiyaya
  • Hisbah ta kama masu safarar mata zuwa Saudiyya a Kano
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen Malabu
  • Shettima ya tafi New York don halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya
  • Hatsarin mota ya yi ajalin mutum 4, 16 sun jikkata a Yobe
  • Kasashen Ingila Da Canada Da Kuma Australia Sun Bayyana Amincewarsu Da Samuwar Kasar Falasdinu
  • SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook
  • Shettima ya bar Abuja don halartar taron majalisar ɗinkin duniya a New York