UEFA: Inter Milan Ta Yi Wa Barcelona Kancal
Published: 7th, May 2025 GMT
Wannan nasara da Inter Milan ta samu ya sa ta kai wasan karshe na gasar Zakarun Turai a karo na biyu cikin shekaru 3, a shekarar 2023 Manchester City ta doke Inter Milan a wasan karshe na gasar, wannan rashin nasara da Barcelona ta yi ya bata mata burinta na lashe gasar a karon farko cikin shekaru 10.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Makon Kiwon Lafiyar Uwa da Ɗa ya Samu Gagarumar Nasara a Karamar Hukumar Gwarzo
Shirin Makon Kiwon Lafiyar Uwa da Ɗa (MNCH) a Karamar Hukumar Gwarzo ta Jihar Kano ya samu gagarumar nasara, inda mata da yara da dama suka amfana da ayyukan kiwon lafiya kyauta iri-iri.
Wannan kamfen na mako guda, wanda Gwamnatin Jihar Kano tare da haɗin gwiwar UNICEF da sauran abokan hulɗa suka tallafa masa, na da nufin inganta lafiyar mata da yara tare da rage mace-macen da za a iya kauce wa ta hanyar samar da dama ga ayyukan kiwon lafiya.
Cibiyoyin lafiya a fadin karamar hukumar, ciki har da Asibitin Gwamnati na Gwarzo da Asibitin ‘Yar Kasuwa, sun bayar da rigakafi kyauta, shawarwari kan abinci mai gina jiki, kulawar haihuwa da sauran muhimman ayyuka na kiwon lafiya.
Jami’in Lafiya a matakin farko na karamar hukumar Gwarzo, Alhaji Sulaiman Abdulqadir Karaye, ya bayyana cewa gwamnatin jiha ta tabbatar da samuwar ingantattun magunguna da kayan aiki.
Ya shawarci mata da masu kula da yara su rika amfana da irin waɗannan damar ta hanyar ziyartar cibiyar kiwon lafiya mafi kusa domin samun ayyuka kyauta.
“Gwamnatin Kano ta bai wa fannin kiwon lafiya muhimmanci ta hanyar tallafi na baya-bayan nan da suka haɗa da na’urar sanyaya allurar rigakafi, janareto da sauran kayan aiki masu muhimmanci,” in ji shi.
Shugaban Asibitin ‘Yar Kasuwa kuma wakilin al’umma a Gwarzo, Salisu Ibrahim, ya bayyana jin daɗinsa kan yawan halartar jama’a.
Ya ce mazauna yankin sun fito sosai domin amfana da ayyukan da aka tanada.
A nata jawabin, jami’ar da ke kula da shirye-shiryen MNCH a karamar hukumar, Hajiya Amina Ado, ta bayyana cewa an gudanar da shirin lafiya cikin nasara a manyan cibiyoyin lafiya tare da wadatattun ma’aikata da kayan aiki.
Ta tabbatar da cewa mata da dama sun halarta, kuma ta yabawa haɗin gwiwar da ke tsakanin masu ruwa da tsaki.
Ɗaya daga cikin masu amfana a Asibitin ‘Yar Kasuwa, Shamsiyya Abubakar, ta yaba wa gwamnatin jiha da ta ƙaramar hukuma bisa samar da magunguna kyauta, inda ta bayyana shirin a matsayin ceton rai ga mata da dama a yankin.
Makon Kiwon Lafiyar Uwa da Ɗa a Jihar Kano na da nufin kai ayyukan lafiya zuwa yankunan da ke da karancin samun kulawa, tare da rage gibin da ke tsakanin mata da yara wajen samun ingantacciyar kulawa.
Khadijah Aliyu