Aminiya:
2025-09-24@11:19:53 GMT

An shafe wata 8 ana mulki babu mataimakin gwamna a Taraba

Published: 7th, August 2025 GMT

Mataimakin Gwamnan Jihar Taraba, Alhaji Aminu Alkali, ya yi ɓatan dabo inda ya shafe tsawon watanni takwas ba tare da an gan shi ba.

Alkali, na fama da rashin lafiya tun a bara wanda hakan ya sa bai sake bayyana a bainar jama’a ba.

Majalisa ta buƙaci ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi a Bauchi Gwamna ya yi wa iyalan ’yan wasan Kano da suka rasu a hatsari goma ta arziki

An fara kula da lafiyarsa a Asibitin Ƙasa da ke Abuja, daga baya aka kai shi ƙasar Masar domin ci gaba da jinya.

Gwamna Agbu Kefas, ya naɗa Emmanuel Lawson, ɗaya daga cikin mataimakansa, domin taimakawa wajen gudanar da ayyukan ofishin mataimakin gwamnan.

A wata wasiƙa da Sakataren Gwamnatin Jiha ya sanya wa hannu, an ce naɗin zai taimaka wajen tabbatar da ingantaccen shugabanci.

Sai dai wasu na ganin Lawson bai cancanci riƙe wannan ofishi ba saboda ba zaɓar shi aka yi ba.

Gwamnati ta ce yana murmurewa

Gwamnatin jihar ta bayyana cewa Alhaji Aminu Alkali na murmurewa daga ciwon shanyewar ɓarin jiki da ya shafi lafiyarsa da yanayin maganarsa.

Kwamishinan Lafiya na jihar, Bordiya Buma, ya kai masa ziyara a watan Maris kuma ya ce yana samun sauƙi.

“Muna farin ciki da samun sauƙi da yake yi kuma muna fatan zai dawo nan ba da jimawa ba.”

Sai dai har yanzu bai dawo bakin aiki ba.

Wasu rahotanni na cewa yana Abuja yana ci gaba da jinya, wasu kuma na cewa yana zaune a wani gida a unguwar Wuse.

A gefe guda kuma, ma’aikatansa sun ce ba sa ganinsa ba.

’Yan adawa na neman ba’asi

Wasu ‘yan siyasa da jama’a suna buƙatar gwamnati ta bayyana gaskiyar halin da mataimakin gwamnan jihar ke ciki.

“Mutanen Taraba suna da ‘yancin sanin inda mataimakin gwamna yake da halin da lafiyarsa ke ciki,” in ji Alhaji Hassan Jika Ardo, tsohon shugaban jam’iyyar APC a jihar.

Ya ce gwamnati ta daina wasa da hankalin jama’a a kan batun da dokar ƙasa ta bayyana a fili.

Dalilin da ya sa ba a sauke shi ba

Sashe na 189 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya bayyana cewa za a iya tsige mataimakin gwamna ne kawai idan kwamitin likitoci ya tabbatar cewa ba shi da ƙoshin lafiyar da zai iya kataɓus.

Wannan na buƙatar ƙuri’a daga kashi biyu bisa uku na majalisar zartarwa ta jihar.

Har yanzu ba a ɗauki wannan matakin ba.

Siyasa ta hana a ɗauki mataki

Wasu majiyoyi sun ce ana matsa wa gwamnan jihar lamba kan ya sauke mataimakin nasa, amma yana tsoron kada hakan ya rushe tsarin rabon madafun iko tsakanin yankunan jihar.

Sauya mataimakin gwamnan na iya janyo rikicin siyasa a jihar.

An taɓa fuskantar irin wannan rikici a Taraba

A shekarar 2012, Gwamna Danbaba Suntai, ya yi hatsarin jirgin sama kuma bai samu sauƙi ba na tsawon watanni.

Rikici ya ɓarke saboda ba a bayyana halin da yake ciki ba, kuma bai miƙa wa majalisa wasiƙar cewa ba zai iya ci gaba da aiki ba.

Wannan ya janyo rikici da rarrabuwar kawuna tsakanin masu goyon bayan gwamnan da na mataimakinsa.

Ra’ayoyin lauyoyi sun bambanta

Wasu lauyoyi sun ce lokaci ya yi da gwamnati za ta aiwatar da dokar ƙasa.

“Rashin lafiyar mataimakin gwamna ta shafi ci gaban jihar. Idan ba zai iya aiki ba, ya kamata ya sauka,” in ji lauya mai kare haƙƙin bil’adama, Malachy Ugwumadu.

Amma wani babban lauya, Richard Ahonaruogho (SAN), ya ce jihar ba ta cikin matsala dangane da rashin lafiyarsa.

“Muddin gwamna bai koka cewa ba zai iya aiki ba, babu buƙatar ɗaukar mataki,” in ji shi.

Jama’a sun fara gajiya

Yayin da aka shafe tsawon lokaci babu mataimakin gwamnan, mutane da dama a jihar suna fara nuna damuwa.

Wasu na ganin rashin bayyana gaskiya yana nuna rashin girmama masu kaɗa ƙuri’a.

Yanzu dai idanun mutane sun karkata ne kan gwamnan da majalisar dokokin jihar domin su bayyana gaskiya ko su ɗauki matakin doka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: mataimakin gwamna Rashin lafiya Siyasa Taraba mataimakin gwamnan mataimakin gwamna

এছাড়াও পড়ুন:

Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 

Sanarwar ta ƙara da cewa, Gwamna Lawal ya jaddada cewa tsarin dimokuraɗiyyar Kanada, ƙarfafan tattalin arziƙi, hakar ma’adinai ta hanyar da ta dace, da kuma harkokin kasuwanci masu zaman kansu masu kirkire-kirkire sun sanya ta zama abokiyar haɗin guiwar da ta ta dace ga Afrika.

 

Ya ce, “Idan Afrika za ta cika burinta gaba ɗaya, dole ne mu gane cewa ci gaba ba wai kawai batun manufofin ƙasa bane; yana kuma buƙatar aikace-aikacen matakan jihohi da ƙananan hukumomi.

 

“Yayin da Gwamnatocin Tarayya ke ba da jagorar manufofi, a matakin Jihohi, larduna, da Ƙananan Hukumomi ake fassara alƙawuran kasuwanci, zuba jari da ci gaba zuwa ainihin gaskiya.

 

“Matakan jihohi sune inda manoma ke noma abincin da ke ciyar da ƙasashe, inda aikin haƙar ma’adinai ke yin nasara ko faɗuwa, inda matasa ke neman dama, da inda masu zuba jari ke bukatar tsari mai bayyana, kwanciyar hankali, da dawowa mai adalci. Wannan shi ya sa kasancewata a nan a matsayin Gwamnan Zamfara ba da gangan bane, illa da nufin ƙarfafawa. Yana nuna cewa tashin hankali na Afrika zai samo asali ne daga jihohi da larduna kamar yadda zai fito daga manyan birane.”

 

Gwamnan ya ƙara da cewa gwamnatinsa na canza tsarin mulki a Zamfara da yanayin saka jari don jawo hankalin abokan hulɗa masu gaskiya waɗanda ke da darajar gaskiya, rikon amana, da ci gaba mai ɗorewa.

 

“Noma shi ne ginshiƙin tattalin arziƙinmu. Fiye da kashi 70 na ƙasar mu tana da filin noma, Zamfara na iya zama amfanin gona ga Nijeriya da ma nahiyar Afrika. Muna neman haɗin kai a fannonin injina, ban ruwa, kula da amfanin gona bayan girbi, ajiya, da sarrafa kayan gona. Kwarewar Kanada, haɗe da jajircewar manomanmu, na iya samar da sabon tsarin tsaron abinci ga Afrika.

 

“Baya ga noma, Zamfara na da ma’adinai masu daraja kamar zinariya, lithium, manganese, da granite waɗanda suke da muhimmanci ga sauyin makamashi. Muna ƙoƙarin koyon darasi daga kurakurai na baya, domin tabbatar da cewa arzikin albarkatu ya fassaru zuwa ci gaba, ba wai fitarwa kawai ba. Muna ƙarfafa dokoki, inganta hakar ma’adinai na gaskiya, da tabbatar da amfanin al’umma.”

 

“Ina kira ga abokanmu na Kanada da su duba bayan manyan biranen Afrika zuwa yankuna, gonaki, makarantun, masana’antu, da al’ummomi, inda ainihin haɗin kai zai bunƙasa. Ku ƙarfafa shugabannin Afrika, ciki har da ni, wajen yin garambawul, ƙarfafa mulki, tsayawa kan gaskiya, da gina muhalli mai kyau ga haɗin kai.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wa’adin Mulki Ɗaya Kacal Za Ka Yi — ADC Ga Tinubu
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato
  • Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 
  • Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnan Ribas, Fubara Ya Ziyarci Tinubu A Fadar Gwamnati A Abuja
  • Mataimakin Shugaban BUK Ya Buƙaci ‘Yan Siyasa Da Su Yi Koyi Da Tallafin Karatu Na Barau
  • Sarkin Ruman Katsina ya rasu
  • An rufe sansanin NYSC da kasuwanni saboda rashin tsaro a Kwara
  • Gwamna Kefas Ya Bamu Damar Ƙwatar Mulkin Taraba A 2027 – APC
  • Gwamnan Gombe ya bai wa maharba kyautar motoci da babura don bunƙasa tsaro
  • Babu Wanda Ya Jawo Ra’ayina  Zuwa Masana’antar Kannywood —Umar Hassan (2)