Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya bayyana cikakken goyon bayan rundunar ‘yan sanda ga Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano wajen tabbatar da kiyaye dabi’u da yakar munanan halaye a cikin al’umma.

CP Bakori ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar wayar da kai da Sakatare na Hukumar, Abba El-Mustapha, ya kai tare da tawagarsa zuwa hedikwatar rundunar ‘yan sandan Kano.

A yayin ganawar, CP Bakori ya yaba da jagorancin hukumar, musamman kokarin da El-Mustapha ke yi wajen tsara harkokin masana’antar Kannywood da kuma kare tarbiyya ta hanyar sa ido mai tsauri.

Ya tabbatar da ci gaba da hadin gwiwa tsakanin rundunar da hukumar, musamman wajen dakile cin zarafi da amfani da kafafen sada zumunta wajen yada munanan abubuwa da kuma kare mutuncin jama’a.

“Rundunar ‘yan sanda a Kano za ta ci gaba da aiki kafada da kafada da hukumar domin tabbatar da doka da oda da kuma kare tarbiyya a  kananan hukumomi 44 na jihar.” In ji CP Bakori.

A nasa jawabin, Shugaban Hukumar Tace Fina-finai, Abba El-Mustapha, ya taya CP Bakori murna bisa sabon nadin da aka masa, tare da jaddada bukatar hadin gwiwa mai karfi tsakanin ‘yan sanda da hukumar.

Ya ce tsaftace fina-finai da sauran abubuwan da ke shafar kafafen watsa labarai ba zai yiwu ba sai da goyon bayan hukumomin tsaro.

“Muna daraja hadin gwiwarmu da rundunar ‘yan sanda, wanda hakan ya taimaka mana wajen tabbatar da bin ka’ida da kare dabi’u a  jihar Kano.” In ji El-Mustapha.

Ya kuma gode wa kwamishinan bisa kyakkyawar tarba da kuma jajircewarsa wajen goyon bayan aikin hukumar, yana mai jaddada kudirin hukumar na ci gaba da sa ido a kafafen watsa labarai da fina-finai, daidai da al’adu da dabi’un al’ummar Kano.

 

Khadijah Aliyu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Jinjinawa Al’ummar Iran Kan Namijin Kokarinsu

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Al’ummar Iran sun dakile shirin ‘yan sahayoniyya a yakin kwanaki 12

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Al’ummar Iran sun dakile shirin yahudawan sahayoniyya a yakin kwanaki 12 da aka kwashe ana gwabzawa. A lokacin da yake halartar taron manema labarai da kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Ismail Baqa’i ya gudanar a yau Litinin, Araqchi ya ce: Na farko dai ya zama wajibi a gare shi ya girmama dukkanin shahidai: shahidan juyin juya halin Musulunci, shahidan tsaro mai alfarma (1980-1988), da dukkanin shahidan da suka sadaukar da rayuwarsu wajenkare kasa, tun farko-farko har zuwa yau, musamman ‘yan jaridu da shahida yakin matsorata masu wuce gona da iri na yakin kwanaki 12.”

Ministan harkokin wajen kasar ya kara da cewa: Babu shakka wannan yaki zai kasance daya daga cikin abubuwan da ba za a taba mantawa da shi ba a tarihin Iran na yau da kullum, yakin da gwamnatin ‘yan sahayoniyya masu laifi tare da goyon baya da hadin gwiwar manyan kasashen duniya da sauran su suka kaddamar na wuce gona da iri kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran tare da fatan cimma munanan manufofinsu da wani harin ba-zata cikin kankanin lokaci, to sai dai al’ummar Iran sun sake tabbatar cewa sun yi tsayin daka tare da zage dantse babu abin da zai kawar da su kan azamarsu, saboda mutane suna ne da saiwoyinsu suka shimfiɗa a cikin kasa sama da dubban shekaru, saiwoyin suke kara karfi kowace rana, ƙasar da ta wanzu saboda sadaukarwa, da tsayin daka, da Imani.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Iran Ko Da Zata Sake Tattaunawa Da Amurka Zata Kasance Dauke Da Makamai Cikin Shirin August 4, 2025 Rahotonni Sun Bayyana Cewa; Agajin Jin kai Da Ake Wurga Ta Sama A Gaza Tamkar Digon Ruwa Ne August 4, 2025 Wa’adin Da Shugaban Amurka Ya Gindaya Na Kawo Karshen Yaki A Ukraine Ya Karato Ba Tare Da Alamun Karewarsa Ba August 4, 2025 Sojojin Somaliya Sun halaka Mayakan Kungiyar Al-Shabab Fiye Da Hamsin A Kudu Maso Yammacin Mogadishu August 4, 2025 Pakisatan: Iran Ce Madogara Ga Al-ummar Musulmi August 4, 2025 Wakilin Hukumar FAO A Iran Yace Sauyin Yanayi Ya shafi Dukkan Yankin August 4, 2025 Malamai A Najeriya Suna Goyon Bayan Iran A Yadda Take Fuskantar HKI August 4, 2025 Shugaban Kasar Lebanon Ya Yi Alkawalin Adalci Ga Wadanda Feshewar Beirut Ta Shafa August 4, 2025 Iran Ta Ce Ba Wani Ma’aikacin Hukumar IAEA A Kasar A Halin Yanzu August 4, 2025 Pezeshkian ya yaba da irin goyon bayan da Pakistan ta baiwa Iran a lokacin yaki August 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jihar Zamfara: ‘Yan Sanda 390 Sun Sami Karin Girma
  • Batun Ceto Wanda Ake Zargi Da Kwaya: Kwamishinan Kano Ya Yi Murabus
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Hadin Kai Tsakanin Cibiyoyi  Na Tabbatar Da Karfi Da Ci gaba
  • An soka wa jami’in Sibil Difens wuka har lahira a Jigawa
  • An Zargin Akantan jihar Nasarawa Da Shiga Harkokin Siyasa
  • Gwamnatin Kano ta karɓi rahoton binciken Kwamishinan da ya yi belin Danwawu
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Jinjinawa Al’ummar Iran Kan Namijin Kokarinsu
  • Gwamnan Kano Ya Kaddamar da Shirin Dashen Bishiyoyi
  • Gwamnatin Jigawa Ta Dauki Manyan Matakan Kare Jihar Daga Ambaliyar Ruwa