Kwamishinan ‘Yan Sanda Na Jihar Kano Ya Sha Alwashin Kawar Da Badala A Harkokin Fina-finai
Published: 6th, August 2025 GMT
Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya bayyana cikakken goyon bayan rundunar ‘yan sanda ga Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano wajen tabbatar da kiyaye dabi’u da yakar munanan halaye a cikin al’umma.
CP Bakori ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar wayar da kai da Sakatare na Hukumar, Abba El-Mustapha, ya kai tare da tawagarsa zuwa hedikwatar rundunar ‘yan sandan Kano.
A yayin ganawar, CP Bakori ya yaba da jagorancin hukumar, musamman kokarin da El-Mustapha ke yi wajen tsara harkokin masana’antar Kannywood da kuma kare tarbiyya ta hanyar sa ido mai tsauri.
Ya tabbatar da ci gaba da hadin gwiwa tsakanin rundunar da hukumar, musamman wajen dakile cin zarafi da amfani da kafafen sada zumunta wajen yada munanan abubuwa da kuma kare mutuncin jama’a.
“Rundunar ‘yan sanda a Kano za ta ci gaba da aiki kafada da kafada da hukumar domin tabbatar da doka da oda da kuma kare tarbiyya a kananan hukumomi 44 na jihar.” In ji CP Bakori.
A nasa jawabin, Shugaban Hukumar Tace Fina-finai, Abba El-Mustapha, ya taya CP Bakori murna bisa sabon nadin da aka masa, tare da jaddada bukatar hadin gwiwa mai karfi tsakanin ‘yan sanda da hukumar.
Ya ce tsaftace fina-finai da sauran abubuwan da ke shafar kafafen watsa labarai ba zai yiwu ba sai da goyon bayan hukumomin tsaro.
“Muna daraja hadin gwiwarmu da rundunar ‘yan sanda, wanda hakan ya taimaka mana wajen tabbatar da bin ka’ida da kare dabi’u a jihar Kano.” In ji El-Mustapha.
Ya kuma gode wa kwamishinan bisa kyakkyawar tarba da kuma jajircewarsa wajen goyon bayan aikin hukumar, yana mai jaddada kudirin hukumar na ci gaba da sa ido a kafafen watsa labarai da fina-finai, daidai da al’adu da dabi’un al’ummar Kano.
Khadijah Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma
Dakta Bukar ya bayyana wannan hadin gwiwar a matsayin abu mai muhimmanci wanda yazo a kan gaba wajen karfafa wayar da kan jama’a game da rawar da sahihan bayanai suke takawa wajen tsara ci gaba da samar da manufofi masu tushe , da dorewar cigaban kasa.
Dakta Bukar, ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa da kafafen yada labarai wajen isar da bayanan Hukumar ga al’umma.
A cikin jawabinsa, Kwamishinan yada labarai Malam Ahmed Maiyaki, ya yaba da wannan shiri tare da tabbatar da cikakken goyon bayan Ma’aikatarsa ga manufofin Hukumar.
Yace samar da sahihan da kafa gwamnati mai wacce da dogara da adalci yana daga cikin manifofi da kudirorin gwamnatin jihar Kaduna wanda hakan zai taiama wajen kawo ci gaba ga al’umma baki daya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA