Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya bayyana cikakken goyon bayan rundunar ‘yan sanda ga Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano wajen tabbatar da kiyaye dabi’u da yakar munanan halaye a cikin al’umma.

CP Bakori ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar wayar da kai da Sakatare na Hukumar, Abba El-Mustapha, ya kai tare da tawagarsa zuwa hedikwatar rundunar ‘yan sandan Kano.

A yayin ganawar, CP Bakori ya yaba da jagorancin hukumar, musamman kokarin da El-Mustapha ke yi wajen tsara harkokin masana’antar Kannywood da kuma kare tarbiyya ta hanyar sa ido mai tsauri.

Ya tabbatar da ci gaba da hadin gwiwa tsakanin rundunar da hukumar, musamman wajen dakile cin zarafi da amfani da kafafen sada zumunta wajen yada munanan abubuwa da kuma kare mutuncin jama’a.

“Rundunar ‘yan sanda a Kano za ta ci gaba da aiki kafada da kafada da hukumar domin tabbatar da doka da oda da kuma kare tarbiyya a  kananan hukumomi 44 na jihar.” In ji CP Bakori.

A nasa jawabin, Shugaban Hukumar Tace Fina-finai, Abba El-Mustapha, ya taya CP Bakori murna bisa sabon nadin da aka masa, tare da jaddada bukatar hadin gwiwa mai karfi tsakanin ‘yan sanda da hukumar.

Ya ce tsaftace fina-finai da sauran abubuwan da ke shafar kafafen watsa labarai ba zai yiwu ba sai da goyon bayan hukumomin tsaro.

“Muna daraja hadin gwiwarmu da rundunar ‘yan sanda, wanda hakan ya taimaka mana wajen tabbatar da bin ka’ida da kare dabi’u a  jihar Kano.” In ji El-Mustapha.

Ya kuma gode wa kwamishinan bisa kyakkyawar tarba da kuma jajircewarsa wajen goyon bayan aikin hukumar, yana mai jaddada kudirin hukumar na ci gaba da sa ido a kafafen watsa labarai da fina-finai, daidai da al’adu da dabi’un al’ummar Kano.

 

Khadijah Aliyu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Wata mata ta ƙona al’aurar ’yarta da wuta kan zargin maita a Bauchi

Wata mata mazauniyar garin Magama Gumau a Ƙaramar Hukumar Toro, Jihar Bauchi, ta shiga hannun ’yan sanda biyo bayan ƙona al’aurar ’yarta mai shekaru 10 kacal a duniya, kan zargin maita.

Rahotanni sun nuna cewa matar ta yi amfani da cokali ta hanyar sanya shi a wuta ya yi zafi sannan ta umarci ’ya’yanta biyu suka riƙe yarinyar sannan ta ƙona ta.

Janye Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya koma Ribas ’Yan bindiga sun kai hari sakatariyar ’yan jarida ta jihar Yobe

Wannan ya jefa yarinyar cikin mawuyacin hali, inda ta ke fama wahalar yin fitsari da bayan gida.

Bayan lamarin ya faru, maƙwabta sun kai ƙarar matar wajen ’yan sanda.

An garzaya da yarinyar zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH) domin kula da ita.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Bauchi, CSP Mohammed Ahmed Wakil, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce an kama matar da wasu, ciki har da wata mai maganin gargajiya mai suna Fatima Abdullahi, wadda ta karɓi kuɗin matar sannan ta tabbatar mata cewa yarinyar mayya ce.

A cewar rundunar, lamarin ya faru ne ranar 11 ga watan Satumba, 2025.

Tuni Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya bayar da umarnin a gudanar da bincike, tare da tabbatar da adalci.

’Yan sanda sun kuma ja hankalin iyaye da su daina kai yara wajen bokaye, domin hakan na iya jawo ɓarna maimakon samun waraka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Sauya Sunan Ma’aikatar Mata
  • Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Jaddada ‘Yancin Kasar Na Mayar Da Martani Kan Sabawa Doka
  • Wata mata ta ƙona al’aurar ’yarta da wuta kan zargin maita a Bauchi
  • Wata mata ta ƙona farjin ’yarta da wuta kan zargin maita a Bauchi
  • Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025
  • Hukumar Bunkasa Ilimin Manyan Makarantu Ta Shirya Taro Na Musamman Ga Jami’anta
  • An kashe ’yan ta’addan IPOB da yawa a Imo — ’Yan Sanda
  • ‘Yansan Jigawa Sun Tabbatarwa Mafarauta Da ‘Yan Bulala Samun Horo
  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa