‘Za a yi ambaliyar kwana 5 a jihohi 19 na Najeriya’
Published: 6th, August 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen cewa za a tafka mamakon ruwan sama na tsawon kwana biyar da zai iya haifar da ambaliyar ruwa a wurare 76 da ke jihohi 19 a Najeriya.
Cibiyar Gargadi kan Ambaliya ta Kasa da ke Ma’aikatar Muhalli ta kasa ce ya yi gargadin ranar Talata, inda ta bukaci dukkan masu ruwa da tsaki da ma sauran jama’a da su dauki mataki.
Gargadin na zuwa ne ’yan kwanaki bayan samun wata mummunar ambaliyar a jihohin Legas da Filato da Anambra da Delta.
Kwamishina ya yi murabus kan ƙarbar belin dillalin ƙwayoyi a Kano Ruftawar gini ta kashe uwa da ’ya’yanta 5 a KatsinaAna has ashen samun mamakon ruwan saman ne daga daga biyar zuwa tar aga watan Agustan 2025.
Yankunan jihohin da za a iya samun ambaliyar a cewar cibiyar sun hada da Kano (Bebeji, Gezawa, Gwarzo, Birni da Kewaye, Karaye, Tundun-wada, Wudil, Kunchi); Kebbi (Bagudo, Birnin-Kebbi, Bunza, Gwandu, Jega, Kalgo, Kamba, Kangiwa, Shanga, Ribah, Sakaba, Saminaka, Yelwa, Gauri-Banza); Neja (Kontagora, Rijau, Ringim); Filato (Mangu); Taraba (Donga, Takum); Jigawa (Diginsa, Gumel, Dutse, Gwaram, Hadejia, Miga); Yobe (Machina, Potiskum); Zamfara (Anka); Sakkwato (Sakkwato, Wamakko); Borno (Biu); da kuma Gombe (Bajoga).
Sauran wuraren sun hada da Akwa-Ibom (Edor, Eket, Ikom, Oron, Upenekang); Bauchi (Tafawa-Balewa, Azare, Jama’are, Kari, Misau, Jama’a); Ebonyi (Abakaliki, Echara, Ezilo); Kuros Riba (Ogoja Edor, Obubra); Nasarawa (Keana, Keffi, Wamba); Binuwai (Agaku, Buruku, Gboko, Igumale, Ito, Katsina-Ala, Ugba, Vande-Ikya); Kaduna (Jaji, Kafancha, Birnin-Gwari, Zaria) sai kuma a jihar Katsina (Bindawa, Bakori, Daura, Funtua).
Ambaliyar ruwa dai ta zama wata babbar annoba da ke faruwa a Najeriya a kowacce shekara inda takan lalata dukiyoyin da ma rasa rayukwan jama’a.
Ko a bara, akalla jihohi 31 ne aka samu rahoton ambaliyar ruwa wacce ta kai ga rasa rayukan mutane da dama tare da shafar mutum miliyan daya da dubu 200.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ambaliya
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan Sandan Legas sun ayyana neman Sowore ruwa a jallo
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Legas ta ayyana ɗan gwagwarmaya kuma tsohon ɗan takarar shugaban kasa, Omoyele Sowore, a matsayin wanda take nema ruwa a jallo.
Wannan mataki da rundunar ta ɗauka na zuwa ne bayan zargin Sowore da yunƙurin ta da zaune tsaye da kawo hargitsi da sunan zanga-zanga a Jihar Legas.
Kano Pillars ta koma ƙarshen teburin Gasar Firimiyar Nijeriya An rantsar da Samia Suluhu Hassan a wa’adin mulki na biyu a TanzaniyaKwamishinan ‘yan sandan jihar, Olorundare Jimoh, ya bayyana cewa tun da fari rundunar ta gargaɗi Sowore kan kada ya jagoranci wata zanga-zanga da aka gudanar kan wani rusau da hukumomi suka gudanar a yankin Oworonshoki na jihar.
Sai dai rundunar ta bayyana cewa Sowore ya yi wa gargaɗin nata kunnen-uwar-shegu, inda ya shirya mutane suka fita tituna domin gudanar da zanga-zanga duk da cewa shi bai halarta ba.
Ana iya tuna cewa dai, Sowore, wanda shi ne jagoran “Take It Back Movement”, ya yi barazanar gudanar da zanga-zanga a makonnin baya domin nuna adawa da rusa gidajen da gwamnati ta yi da sunan shirin sabunta birni a Jihar Legas.