‘Za a yi ambaliyar kwana 5 a jihohi 19 na Najeriya’
Published: 6th, August 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen cewa za a tafka mamakon ruwan sama na tsawon kwana biyar da zai iya haifar da ambaliyar ruwa a wurare 76 da ke jihohi 19 a Najeriya.
Cibiyar Gargadi kan Ambaliya ta Kasa da ke Ma’aikatar Muhalli ta kasa ce ya yi gargadin ranar Talata, inda ta bukaci dukkan masu ruwa da tsaki da ma sauran jama’a da su dauki mataki.
Gargadin na zuwa ne ’yan kwanaki bayan samun wata mummunar ambaliyar a jihohin Legas da Filato da Anambra da Delta.
Kwamishina ya yi murabus kan ƙarbar belin dillalin ƙwayoyi a Kano Ruftawar gini ta kashe uwa da ’ya’yanta 5 a KatsinaAna has ashen samun mamakon ruwan saman ne daga daga biyar zuwa tar aga watan Agustan 2025.
Yankunan jihohin da za a iya samun ambaliyar a cewar cibiyar sun hada da Kano (Bebeji, Gezawa, Gwarzo, Birni da Kewaye, Karaye, Tundun-wada, Wudil, Kunchi); Kebbi (Bagudo, Birnin-Kebbi, Bunza, Gwandu, Jega, Kalgo, Kamba, Kangiwa, Shanga, Ribah, Sakaba, Saminaka, Yelwa, Gauri-Banza); Neja (Kontagora, Rijau, Ringim); Filato (Mangu); Taraba (Donga, Takum); Jigawa (Diginsa, Gumel, Dutse, Gwaram, Hadejia, Miga); Yobe (Machina, Potiskum); Zamfara (Anka); Sakkwato (Sakkwato, Wamakko); Borno (Biu); da kuma Gombe (Bajoga).
Sauran wuraren sun hada da Akwa-Ibom (Edor, Eket, Ikom, Oron, Upenekang); Bauchi (Tafawa-Balewa, Azare, Jama’are, Kari, Misau, Jama’a); Ebonyi (Abakaliki, Echara, Ezilo); Kuros Riba (Ogoja Edor, Obubra); Nasarawa (Keana, Keffi, Wamba); Binuwai (Agaku, Buruku, Gboko, Igumale, Ito, Katsina-Ala, Ugba, Vande-Ikya); Kaduna (Jaji, Kafancha, Birnin-Gwari, Zaria) sai kuma a jihar Katsina (Bindawa, Bakori, Daura, Funtua).
Ambaliyar ruwa dai ta zama wata babbar annoba da ke faruwa a Najeriya a kowacce shekara inda takan lalata dukiyoyin da ma rasa rayukwan jama’a.
Ko a bara, akalla jihohi 31 ne aka samu rahoton ambaliyar ruwa wacce ta kai ga rasa rayukan mutane da dama tare da shafar mutum miliyan daya da dubu 200.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ambaliya
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila na ci gaba da ragargaza Birnin Gaza ta sama da ƙasa
Dakarun sojan Isra’ila na ƙara nausawa cikin wani yanki mai cike da jama’a a birnin Gaza, yayin da suke ci gaba da kai farmaki ta ƙasa domin ƙwace iko da babban birnin mafi cunkoson jama’a.
Ana iya ganin yadda hayaƙi ya turnuke sararin samaniya yayin da sojojin ke harba makaman atilare da luguden bama-bamai.
Dubban mutane sun gudu, wasu kuma sun maƙale saboda haɗarin da ke tattare da guduwar. Sama da mutane sittin ne aka ce an kashe a jiya kadai.
Isra’ila ta ce tana gudanar da bincike kan rahotannin da ke cewa dakarunta sun kai hari kan asibitin yara na Gazan.
Ta ce tana son kubutar da mutanenta da Hamas ta rike da su, da kuma fatattakar mayaƙan Hamas 3,000 a wurin da ta bayyana a matsayin “tungar mayaƙan ta ƙarshe”.