Aminiya:
2025-09-20@20:42:07 GMT

Ambaliya ta lalata kauyuka 3 a Sakkwato

Published: 6th, August 2025 GMT

Akalla magidanta 50 ne ambaliyar ruwa ta raba da muhallansu a kauyuka uku na karamar hukumar Tangaza da ke jihar Sakkwato, sakamakon wani mamakon ruwan sama da aka tafka a yankunan.

Ambaliyar da ta mamaye kauyukan na Tangaza ne da suka hada da Gidan Madi da Baidi da Madarare, kuma ta haifar da rushewar gidaje da lalacewar gonaki da rijiyoyi da sauran su.

Yadda ’yan bindiga suka sace Zamfarawa 150 a cikin kwana 4 Duk wanda ya haka rijiyar burtsatse a Lekki ruwan masai yake sha – Gwamnatin Legas

Mutanen da lamarin ya shafa sun ce suna bukatar agajin gaggawa na abinci da magani da tsaftataccen ruwan sha.

Shugaban karamar hukumar ta Tangaza, Isah Salihu Kalenjeni, ya jagoranci wata tawaga sun ziyarci wuraren da lamarin ya shafa don ganin barnar da ambakiyar ta yi tare da jajanta wa mutanen yankunan.

A yayin ziyarar, Shugaban karamar hukumar ya tabbatar wa mutanen zai sanar da duk wata hukuma da ta dace don kawo masu daukin gaggawa kan halin da suke ciki.

Hukumomi a karamar hukuma da masu bayar da agajin gaggawa sun kuma yi kira wadanda iftila’in ya shafa da su yi aiki tukuru don kare barkewar annobar ciwo ga sauran al’umma.

Aliyu Na Abba daya daga cikin mutanen da ambaliyar ta rusa wa gida da gonaki biyu ya ce yana bukatar hukuma ta tausaya masa halin damuwar da shi da iyalansa suka fada.

Umaima Dan Umaru da ta ke da marayu uku a tare da ita ta ce gonakinsu biyu da suka yi shuka sun lalace sabadiyyar ambaliyar, don haka suna neman agaji.

Ta ce akalla akwai kusan mutum 50 da suka tafka asara a yankin nasu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 9 sun rasu a hatsarin jirgin ruwa a Sakkwato

Mutum tara sun rasu a wani hatsarin jirgin ruwa da ya auku a ƙauyen Zalla Bango, da ke Ƙaramar Hukumar Sabon Birni, a Jihar Sakkwato.

Wani mazaunin yankin ya ce hatsarin ya faru ne bayan sallar Magariba a ranar Alhamis, lokacin da jirgin da ya ɗauki mata, maza da yara, domin tsallaka ruwa saboda hanyar mota ta yanke sakamakon ambaliya.

Wata mata ta haifi ’ya’ya huɗu a Bauchi Kwalara ta kashe mutane 58, wasu sun kamu a Bauchi

Yayin da yake tafiya, jirgin ya bugi wata ƙaramar gada ta nutse a ruwa, lamarin da ya jawo mutuwar mutum tara, yayin da wasu suka samu rauni.

Rahotanni sun ce ba a san adadin mutanen da ke cikin jirgin ba saboda ya ɗauki mutane fiye da kima.

Har yanzu hukumomin agajin gaggawa ba su fitar da wata sanarwa ba kan hatsarin.

A nasa martanin, Sanata Ibrahim Lamiɗo, Sanata mai wakiltar Sakkwato ta Gabas, ya aike da saƙon ta’aziyyarsa ga al’ummar yankin tare da kiran gwamnati da ta ƙara ƙaimi wajen samar da tsaro da gyaran hanya tsakanin Sabon Birni da Goronyo.

Ya ce rashin tsaro da matsalar tituna na jefa mutanen yankin cikin hatsari, tare da jaddada cewa gwamnati na da alhakin kare rayukan jama’a da kuma inganta rayuwarsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 9 sun rasu a hatsarin jirgin ruwa a Sakkwato
  • ’Yan bindiga sun kashe basarake, sun tarwatsa mutane a Sakkwato
  • Miyetti Allah ta roki Gwamntin Kwara da ta sa baki kan rufe Kasuwar Kara da Shugaban Karamar Hukuma Ya Yi
  • Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu
  • Hukumomin Bada Agajin Gaggawa Sun Bada Horo Kan Aikin Ceto A Karamar Hukumar Auyo
  • ’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa
  • SEMA Jigawa Da NEMA Da UNICEF Sun Bada Horo Akan Agajin Gaggawa A Auyo
  • Tinubu Ya Jajantawa Iyalai Wadanda Gobara Ta Shafa A FIRS, UBA Da United Capital
  • An kashe ’yan ta’addan IPOB da yawa a Imo — ’Yan Sanda
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato