Majalisar Kaduna ta Amince da Kudirin Kula da Lafiyar Kwakwalwa na Jihar
Published: 15th, April 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da kudirin kafa sashen kula da masu fama da matsalar kwakwalwa a jihar ya zama doka.
Dokar za ta samar da kariya da kuma bunkasa ‘yancin masu fama da matsalar kwakwalwa musamman masu tu’ammuli da muggan kwayoyi a fadin jihar Kaduna.
Da yake jagorantar zaman majalisar, shugaban majalisar dokokin jihar kaduna, Yusuf Dahiru Liman ya sanar da amincewa da kudirin wanda aka yiwa lakabi da kudirin kula da lafiya masu fama da cutar kwakwalwa na jihar Kaduna.
Da yake gabatar da rahoto, shugaban kwamitin hadin gwiwa na lafiya da sharia, wanda aka dorawa alhakin yin nazari a kan wannan kudiri, Mr. Haruna Barnabas ya ce sun yi nazarin kudirin sannan sun gano cewa akwai bukatar a karfafa matakan da jihar ke bi wajen kula da masu fama da matsalar kwakwalwa domin bunkasa lafiyar kwakwalwa da magance kalubalen da masu tu’ammuli ke fuskanta a cikin al’umma.
Ya ce sabuwar dokar za ta taimaka wajen sauya suna tare da manufofin Hukumar Yaki da Tu’ammuli da Muggan Kwayoyi ta Jihar Kaduna-KADBUSA zuwa Hukumar Yaki da Tu’ammuli da Muggan Kwayoyi da Kula da Lafiyar Kwakwalwa ta Jihar Kaduna-KADSAMHSA domin ya dace da yadda ake tafiyar da irin wadannan ayyuka a matakin duniya.
A cewar shugaban kwamitin, za ta tabbatar da cewa ana mutunta masu tu’ammuli da muggan kwayoyi, da gyara dabi’un su da kuma sake shigar da su cikin al’amuran al’umma don su bada gudunmuwa mai ma’ana.
A wani labarin kuma, majalisar dokokin jihar Kaduna ta mika wani kudiri dake bukatar kafa Hukumar Kula da Ilimin Manyan Makarantun Sakandare, na 2025.
Kudirin, wanda dan majalisa mai wakiltar birnin Zaria a majalisar dokokin jihar Kaduna, Barrister Mahmud Lawal Isma’ila ya ce kudirin zai inganta tsarin ilimin jihar ya dace da ci gaban zamani.
Ya ce idan aka amince da kudirin ya zama doka, hukumar za ta rika kula da dukkanin manyan makarantun sakandare a fadin jihar, don tabbatar da ganin ana sarrafa kudaden da aka ware ma bangaren ilimi don ganin ya habbaka.
Shamsuddeen Mannir Atiku
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwakwalwa Lafiya jihar Kaduna Jihar Kaduna
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
Rahoton rashin fahimtar da aka fara yadawar, ya biyo bayan taron kwamitin zaman lafiya da kwantar da tarzoma na jihar, wanda Darakta Janar ya jagoranta a ranar 4 ga watan Satumba.
Rashin fahimtar sahihin sakamakon taron ya sa wasu suka rahoto cewa, kwamitin ya dakatar da Malamai daga yin wa’azi.
Sanarwar ta kara da cewa, “Hukumar ba ta da hurumin haramtawa Malaman Addinin Musulunci yin wa’azi sai dai in ya bayyana a fili an taka ƙa’idojin hukumar da ta shimfiɗa”.
A cewar Hukumar, an kira taron ne domin gabatar da fom din rijistar yin wa’azi ko Da’awah da kuma bin tsarin tantancewa.
Ta bayyana shirin a matsayin wani yunkuri na wayar da kan jama’a don “hana rashin fahimtar juna da kuma daƙile yaɗuwar wa’azin yaudara” a faɗin jihar Neja.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp