Leadership News Hausa:
2025-08-05@21:27:46 GMT

Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

Published: 5th, August 2025 GMT

Gwamnatin Sin: Gwamnatin Jama’a Domin Jama’a

Sadarwar intanet da lantarki da ruwa da sauran abubuwan bukatun jama’a na yau da kullum sun game baki dayan kasar Sin. Ni ganau ce ba jiyau ba, domin na yi tafiye-tafiye da dama, na shiga kauyukan kasar Sin, kuma cikinsu babu inda na ziyarta da ban ga wadannan abubuwa da na ambata ba.

Idan muka ajiye batun sadarwar intanet a gefe, majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ita ce majalisar koli mai tsara dokoki a kasar, kuma wakilanta na fitowa ne daga dukkan bangarori da yankunan kasar.

Sabanin yadda muka saba gani a kasashenmu inda wakilan jama’a ke tarewa a babban birnin, wakilan jama’a a kasar Sin na komawa ne cikin al’ummominsu, kuma a nan suke tattaro ra’ayoyi da shawarwari da bukatun jama’a.

Yayin da ake bin tsarin demokuradiyya, to ya zama wajibi walwala da kwanciyar hankalin jama’a su zama a kan gaba. Ina da yakinin yadda gwamnatin Sin ke sauraron ra’ayin jama’a da aiki tukuru wajen kyautata rayuwarsu na da nasaba da yadda jama’ar ke da kishin kasa da kokarin tallafawa ayyukan gwamnati. Tsarin demokuradiyyar kasar Sin ya nuna yadda gwamnati ke sauke nauyinta na hidimtawa jama’a da yadda jama’ar suke sauke nauyinsu na ba da gudunmawa ga ci gaban kasa da kishin kasa da kiyaye dokoki.

Hakika irin wannan tsari shi ake kira da ainihin demokuradiyya kuma irinsa ne ya dace da galibin kasashen duniya musamman masu tasowa dake kallon kasar Sin a matsayin a bar koyi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Karrama ‘Yan Wasan Kwallon Kwando Na Mata

Gwamnatin Tarayya ta gabatar da karramawar kasa da kuma tukuicin kudade ga kungiyar kwallon Kwando ta mata ta Najeriya, D’Tigress, bayan nasarar da suka samu a gasar cin kofin kwallon kwando na mata ta FIBA karo na biyar a jere.

 

A wata liyafar karrama su da aka yi a fadar shugaban kasa, mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, mai wakiltar shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa kowane dan wasa zai karbi dala 100,000, yayin da koci da kungiyar kwararru za su samu dala 50,000 kowanne, tare da karramawar kasa ga daukacin kungiyar. Ya kuma yi alkawarin karin tukuicin da zai zo.

 

Shettima ya ce ba wai don murnar nasarar da kungiyar ta samu a cikin shekaru 78-64 ne kawai ba, har ma da sanin tsayin daka, aiki tare, da kuma alfahari da suka kawo wa al’ummar kasar.

 

Ya bayyana wannan nasara a matsayin wata alama ta hadin kai da kuma tabbatar da abin da Najeriya za ta iya cimma idan al’ummarta suka yi aiki tare.

 

Mataimakin shugaban kasar ya yabawa kociyan kungiyar Rena Wakama, wacce ta kafa tarihi a matsayin daya daga cikin mata masu horar da ‘yan wasan kwallon kwando na Afirka, inda ya kira ta a matsayin “masoya kuma abin zaburarwa ga ‘yan mata a fadin Najeriya.”

 

Ya kuma yabawa Amy Okonkwo, ‘Dan wasan da ta fi kowa daraja a gasar, da Ezinne Kalu, wanda ya fi zura kwallaye a wasan karshe, saboda irin gudunmawar da suka bayar wajen samun nasarar kungiyar.

 

Da yake karin haske kan muhimmancin nasarar, Shettima ya jaddada cewa, matan Najeriya a kodayaushe sun kasance abin alfaharin kasa a fagen wasanni daban-daban, tun daga Super Falcons zuwa wasannin guje-guje da tsalle-tsalle, da kuma wasan kwallon kwando.

 

Ya ba da tabbacin cewa a karkashin gwamnatin shugaba Tinubu, za a mayar da wasannin motsa jiki a matsayin wani muhimmin ginshiki na ci gaban kasa—da ilimi, ababen more rayuwa, diflomasiyya, da kuma samar da ayyukan yi ga matasa.

 

Ya kuma yabawa hukumar wasanni ta kasa karkashin Mallam Alabi, da hukumar kwallon kwando ta Najeriya karkashin jagorancin Malam Ahmadu Musa Kida, bisa gyara da jajircewa da suka yi wajen bunkasa hazikan ‘yan wasa da kuma tallafawa ‘yan wasa.

 

Bikin da aka yi a fadar gwamnati ya nuna ba tukuici ne ga D’Tigress ba, har ma da wani sako mai karfi wanda idan aka gane da kuma goyon bayansa, na iya sauya wasannin Najeriya da zaburar da tsararraki.

 

Bello Wakili

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwalejin NDA Ta Ce Jerin Sunayen Da Ke Yawo A Kafafen Sada Zumunci NA Jabu Ne
  • Gwamnatin Tarayya Ta Karrama ‘Yan Wasan Kwallon Kwando Na Mata
  • Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet
  • Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15
  • Gwamnan Jihar Kwara Ya Hori Sabbin Matasa Masu Yiwa Kasa Hidima Akan Kishin Kasa
  • Gwamnatin Sakkwato Za Ta Kashe fiye da Naira Miliyan 200 Wajen Gyara Tashar Talabijin Ta Kasa NTA
  • Gwamnatin Jigawa Ta Dauki Manyan Matakan Kare Jihar Daga Ambaliyar Ruwa
  • Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa
  • Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a