Hatsarin Mota: Yadda hanyar Lambata ke laƙume rayuka a Neja
Published: 6th, August 2025 GMT
Mutum 22 sun gamu da ajalinsu, yayin da wasu 20 suka jikkata, bayan wata babbar mota da ta yi lodin mutane da dabbobi ta yi hatsari a kan hanyar Lambata zuwa Lapai da ke Jihar Neja.
Hatsarin ya auku ne da safiyar ranar Litinin.
Tinubu ya taya ’yan matan Yobe da suka lashe gasa a Ingila murna Ambaliya ta lalata kauyuka 3 a SakkwatoMotar ta taso daga Kano zuwa Legas ne lokacin da hatarin ya auku da misalin ƙarfe 3 na safe, sakamakon gudun wuce ƙima.
Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC), ta ce dukkanin fasinjojin da ke cikin motar maza ne.
An kai gawarwakin Babban Asibitin Suleja, yayin da aka garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Gwamnati na Lambata.
Daga baya, iyalan wasu daga cikin waɗanda hatsarin ya rutsa da su, sun ɗauke su zuwa wasu cibiyoyin lafiya.
Jama’a sun ce hatsarin mota na ci gaba da zama ruwan dare a hanyar Lambata zuwa Bida, musamman manyan motocin dakon kaya da ke ɗauko mutane da dabbobi a lokaci guda.
Wasu sun ɗora laifi kan lalacewar hanya, gudun wuce ƙima da rashin bin dokokin hanya.
Aƙalla mutum 80 ne suka rasu a wannan hanya cikin shekarar da ta gabata.
Wasu mazauna yankin sun ce hanyar tana hatsari sosai ga ƙananan motoci da masu babura, saboda yawan manyan motoci da ke zirga-zirga a hanyar.
Sun buƙaci gwamnati da ta gyara hanyar, tare da ɗaukar mataki kan direbobi masu ganganci.
Ana ci gaba da aikin gyaran hanyar Lambata-Lapai-Agaie-Bida ƙarƙashin wani shiri na NNPC.
Amma sai an kammala aikin da kuma kafa dokoki masu tsauri kan zirga-zirgar ababen hawa, jama’a na fargabar cewa za a iya ci gaba da salwantar rayuka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hatsarin mota Manyan motoci hanyar Lambata
এছাড়াও পড়ুন:
Jariri ya mutu a bayan uwarsa yayin tsere wa ’yan bindiga a Neja
Wani jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa a yayin da take guje wa harin ’yan bindiga a kauyen Allawa da ke Karamar Hukumar Shiroro a Jihar Neja.
Sarkin yankin Bassa, Bagudu Amos, ne ya bayyana hakan a lokacin taron tattaunawa da mata kan zaman lafiya da kare su daga cin zarafi, mai taken: “Ƙarfafa kariya daga cin zarafin jima’i da na jinsi a Jihar Neja.”
Kungiyar Tunani Initiative, tare da goyon bayan Dorothy Njemanze Foundation da Ford Foundation, ce ta shirya taron domin ƙarfafa mata wajen yaki da cin zarafi da ke ƙara ta’azzara a sakamakon rashin tsaro.
Bagudu Amos ya bayyana cewa mahaifiyar ta yi tafiya mai nisa a kafa da jaririn a bayanta domin tserewa daga harin ’yan bindiga, amma daga bisani ta gano cewa jaririn ya riga ya mutu a bayanta.
Yadda aka kashe jami’an tsaro 53 cikin mako biyu NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen MalabuYa ce lamarin da ya faru a shekarar 2023, na ɗaya daga cikin dimbin abubuwan firgici da mata ’yan gudun hijira ke fuskanta a kullum, inda mafi yawansu ba su da isasshen tallafi ko ƙarfafa gwiwa wajen yaki da cin zarafin jinsi da ke biyo bayan matsalar tsaro.
Shugabar Tunani Initiative, Maryam Mairo Ibrahim, ta nuna damuwarta kan yadda ba a ba wa mata muhimmanci da ya dace wajen shiga cikin harkar sasanta rikice-rikice da zaman lafiya a Jihar Neja. Ta yi kira ga mata da su haɗa kai domin karya shingayen da ke hana su shiga harkokin warware rikice-rikice.
“A Jihar Neja, kamar yadda ake gani a wasu wuraren da ke fama da rashin tsaro, mata su ne mafiya fuskantar ƙuncin hare-haren ’yan bindiga. Idan an kai hari, mafi yawanci maza ake kashewa, sai a bar mata da nauyin sake gina iyali daga farko. Wannan rawar da mata ke takawa ba a ba shi muhimmancin da ya kamata. Wannan shi ne dalilin da ya sa taron ya mayar da hankali kan ƙara bayyana muhimmancin mata a harkar zaman lafiya da kuma yaki da cin zarafi,” in ji ta.
Daraktan Hukumar Kare Hakkokin Dan Adam a Jihar Neja, Ambasada Nuhu Muhammad, ya jaddada muhimmancin samun karin mata a majalisar dokokin jiha da ma ta ƙasa domin samar da dokoki da manufofi da za su amfanar da su.
Mata da suka halarci taron sun yi kira da a tsaurara hukunci kan masu yi wa mata fyade, tare da kira da a haɗa ƙarfi da ƙarfafa juna wajen shawo kan yawaitar cin zarafi musamman a ƙauyuka.
Mahalarta sun kuma jaddada muhimmancin kafa ƙungiyar mata mai ƙarfi guda ɗaya domin tunkarar matsalar cin zarafin mata a Jihar Neja.