Jihar Zamfara: ‘Yan Sanda 390 Sun Sami Karin Girma
Published: 6th, August 2025 GMT
Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Zamfara, CP Ibrahim Balarabe Maikaba, ya kawata jami’ai 390 da aka daga matsayinsu zuwa sabon mukami a rundunar.
An gudanar da bikin kawata jami’an ne a Hedikwatar Rundunar ‘Yan Sanda da ke Gusau, babban birnin jihar.
A cewar sanarwar da mai magana da yawun ‘yan sanda, DSP Yazid Abubakar, ya fitar, Kwamishinan ‘Yan Sanda ya taya sabbin jami’an murna tare da bukatar su tabbatar da cancantarsu da mukaman da aka ba su, ta hanyar rubanya kishin aiki, ladabi da kwarewa a ayyukansu.
Ya jaddada bukatar jami’an da su dage wajen yin aiki da jajircewa da kuma bayar da ingantaccen tsaro ga al’ummar Jihar Zamfara da Najeriya gaba ɗaya.
Daga cikin waɗanda suka sami karin girman akwai CSP Sani Kabiru da CSP Usman M. Nassarawa, waɗanda aka daga zuwa mukamin Mataimakin Kwamishinan ‘Yan Sanda (ACP).
“An daga jami’ai 30 daga matsayin Sifeto zuwa Mataimakin Sufiritandan ‘Yan Sanda (ASP II).” In ji Kwamishinan.
Ya ƙara da cewa, an daga jami’ai 242 daga Sajan zuwa Sufeta, sannan kuma an daga jami’ai 116 daga matsayin Kofur zuwa Sajan.
Da yake magana a madadin sabbin jami’an da aka daga matsayinsu, ACP Usman M. Nassarawa ya nuna godiya sosai ga Sufeto Janar na ‘Yan Sanda da Hukumar Kula da Ayyukan ‘Yan Sanda bisa amincewar da suka nuna a gare su.
Ya yi alkawarin cewa sabbin jami’an za su ci gaba da kiyaye manyan dabi’un aikin ‘yan sanda na Najeriya – wato gaskiya, jajircewa, ƙwarewa da amincewar jama’a – a hidimarsu ga ƙasa.
Daga Aminu Dalhatu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kai hari sakatariyar ’yan jarida ta jihar Yobe
Wasu ’yan bindiga da ba a san ko su waye ba sun kai hari a sakatariyar Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) da ke Damaturu, babban birnin jihar Yobe, da sanyin safiyar Juma’a.
Rahotanni sun ce yayin harin, maharan sun harbi wani jami’in ɗan sanda da ke gadin sakatariyar suka ji masa rauni ƙafa.
An dakatar da shugabannin sakandare 6 a Sakkwato kan zargin cin amanar aiki Amurka ta hau kujerar-na-ƙi kan buƙatar MDD ta tsagaita wuta a GazaLamarin dai ya faru ne da misalin ƙarfe 2:00 na dare, inda maharan suka buɗe wuta.
Shugaban ƙungiyar NUJ reshen jihar, Rajab Ismail Mohammed, ya bayyana harin a matsayin abin tayar da hankali da kuma babbar barazana ga lafiyar ’yan jarida a jihar.
Ya yi kira ga jami’an tsaro da su gaggauta gudanar da bincike kan lamarin tare da gurfanar da maharan a gaban kotu.
Ƙungiyar ta kuma yi kira ga hukumomi da su ƙara ƙaimi wajen samar da tsaro ga ƙwararrun kafafen yaɗa labarai da cibiyoyin yaɗa labarai a faɗin jihar, inda ta jaddada cewa irin waɗannan hare-hare na iya kawo cikas ga ’yancin ’yan jarida da kuma samun damar yin amfani da bayanan jama’a.
Ƙungiyar ta jaddada cewa kare ‘yan jarida na da matuƙar muhimmanci ga ci gaban dimokuraɗiyya da riƙon amanar jama’a.
Yanzu haka dai dan sandan da aka harba na can a sashin gaggawa na asibitin ’yan sanda da ke Damaturu.
Rahotanni sun ce hukumomin ’yan sanda sun fara gudanar da bincike domin gano waɗanda ke da hannu a lamarin.