Aminiya:
2025-09-24@12:44:16 GMT

Majalisa ta buƙaci ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi a Bauchi

Published: 7th, August 2025 GMT

Majalisar Dokokin Bauchi ta buƙaci ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi a fadin jihar domin haɓaka ci gaba, inganta shugabanci, da kawo sauƙin gudanar da mulki.

Wannan na ƙunshe ne a wani ƙudiri da dan majalisar mai wakiltar mazabar Disina, Sale Hodi Jibir, ya gabatar a yayin zaman da Kakakin Majalisar, Abubakar Y.

Sulaiman, ya jagoranta.

Gwamna ya yi wa iyalan ’yan wasan Kano da suka rasu a hatsari goma ta arziki Ministocin Ghana biyu sun rasu a hatsarin jirgin sama

A cewar Jibir, ƙudurin yana dogaro ne da tanadin kundin tsarin mulki na 1999 wanda ya bai wa majalisun dokokin jihohi damar fara shirin ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi, matuƙar an cika wasu sharuɗa da suka haɗa da goyon bayan kashi biyu bisa uku na mambobin majalisa, da mincewar ƙananan hukumomin da abin ya shafa da kuma gudanar da zaɓen raba gardama.

Jibir ya bayyana cewa ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi zai sauƙaƙa rarraba albarkatu cikin adalci da inganta shugabanci da gudanarwa a matakin ƙasa da ƙarfafa haɗin kan al’umma da ci gaban tattalin arziki.

Ya kuma ce yankuna da dama a Jihar Bauchi sun gabatar da buƙatar a ware musu ƙaramar hukuma, musamman duba da girman yankunansu, yawan al’umma, bambancin al’adu da kuma ƙalubalen gudanar da mulki.

Jibir ya buƙaci a kafa kwamitin wucin gadi na musamman domin tattarawa da tantance buƙatun al’umma, da tuntuɓar sarakunan gargajiya da shugabannin al’umma da nazarce-nazarce kan fadin ƙasa, da yawan jama’a da yanayin tattalin arziki na yankunan da ake neman a samar musu da ƙananan hukumomi.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, ƙudirin wanda ya samu goyon bayan wasu mambobin majalisar da suka buƙaci a gaggauta aiwatar da shi domin amfanin jama’a sun haɗa da Jamilu Umaru Dahiru da Musa Wakili Nakwada da Ibrahim Tanko Burra da Sa’idu Sulaiman Darazo da Dokta Nasiru Ahmed Ala.

A wani ɓangare na zaman, majalisar ta amince da rahoton kwamitinta na ma’aikata, dangane da ƙorafe-ƙorafen rashin biyan ’yan fansho da albashin ma’aikatan ƙananan hukumomi a faɗin jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Bauchi Ƙananan Hukumomi Majalisar Dokokin Bauchi ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi

এছাড়াও পড়ুন:

He Lifeng: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Karfafa Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Mai Dorewa Cikin Lumana

Mataimakin firaministan kasar Sin He Lifeng ya gana da tawagar ‘yan majalisar wakilan Amurka karkashin jagorancin Adam Smith a yinin yau Litinin 22 ga wata a birnin Beijing.

He Lifeng ya ce, a ranar 19 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping da shugaba Donald Trump sun yi wata tattaunawa ta wayar tarho, kuma sun cimma muhimmiyar matsaya, tare da samar da jagoranci bisa manyan tsare-tsare don tabbatar da daidaiton dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka a mataki na gaba. Kasashen Sin da Amurka na da sararin yin hadin gwiwa da kuma samun moriyar juna.

Ana sa ran Amurka za ta sa kaimi wajen yin magana da kasar Sin bisa ka’idojin mutunta juna, da zaman lafiya da samun nasara ga ko wane bangare, da kara amincewa da juna, da kawar da shakku, da sa kaimi ga habaka dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka. Ana fatan mambobin majalisar wakilan Amurka za su himmatu wajen samar da hanyoyin zantawa, da inganta tattaunawa da mu’amala, da kuma taka rawar gani wajen ci gaban kasashen biyu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kama Ɗansandan Bogi A Kano
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato
  • Majalisa ta ɗage ranar dawowarta zuwa 7 ga watan Oktoba
  • He Lifeng: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Karfafa Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Mai Dorewa Cikin Lumana
  • An gudanar da bikin ɗaga tutar Falasɗinu a Birtaniya
  • Dalilin da muke goyon bayan Tinubu kan karɓo bashi — Majalisar Wakilai
  • Dalilin da muke goyon bayan tsare-tsaren Tinubu na karɓo bashi — Majalisar Wakilai
  • Mataimakin Shugaban BUK Ya Buƙaci ‘Yan Siyasa Da Su Yi Koyi Da Tallafin Karatu Na Barau
  • Karin ƙananan hukumomi 2 sun yi sulhu da ’yan bindiga a Katsina
  • Mata Ne Ƙashin Bayan Gyaran Duk Wata Al’umma, In Ji  Sheik Shamsudeen