Aminiya:
2025-08-06@23:27:07 GMT

Majalisa ta buƙaci ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi a Bauchi

Published: 7th, August 2025 GMT

Majalisar Dokokin Bauchi ta buƙaci ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi a fadin jihar domin haɓaka ci gaba, inganta shugabanci, da kawo sauƙin gudanar da mulki.

Wannan na ƙunshe ne a wani ƙudiri da dan majalisar mai wakiltar mazabar Disina, Sale Hodi Jibir, ya gabatar a yayin zaman da Kakakin Majalisar, Abubakar Y.

Sulaiman, ya jagoranta.

Gwamna ya yi wa iyalan ’yan wasan Kano da suka rasu a hatsari goma ta arziki Ministocin Ghana biyu sun rasu a hatsarin jirgin sama

A cewar Jibir, ƙudurin yana dogaro ne da tanadin kundin tsarin mulki na 1999 wanda ya bai wa majalisun dokokin jihohi damar fara shirin ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi, matuƙar an cika wasu sharuɗa da suka haɗa da goyon bayan kashi biyu bisa uku na mambobin majalisa, da mincewar ƙananan hukumomin da abin ya shafa da kuma gudanar da zaɓen raba gardama.

Jibir ya bayyana cewa ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi zai sauƙaƙa rarraba albarkatu cikin adalci da inganta shugabanci da gudanarwa a matakin ƙasa da ƙarfafa haɗin kan al’umma da ci gaban tattalin arziki.

Ya kuma ce yankuna da dama a Jihar Bauchi sun gabatar da buƙatar a ware musu ƙaramar hukuma, musamman duba da girman yankunansu, yawan al’umma, bambancin al’adu da kuma ƙalubalen gudanar da mulki.

Jibir ya buƙaci a kafa kwamitin wucin gadi na musamman domin tattarawa da tantance buƙatun al’umma, da tuntuɓar sarakunan gargajiya da shugabannin al’umma da nazarce-nazarce kan fadin ƙasa, da yawan jama’a da yanayin tattalin arziki na yankunan da ake neman a samar musu da ƙananan hukumomi.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, ƙudirin wanda ya samu goyon bayan wasu mambobin majalisar da suka buƙaci a gaggauta aiwatar da shi domin amfanin jama’a sun haɗa da Jamilu Umaru Dahiru da Musa Wakili Nakwada da Ibrahim Tanko Burra da Sa’idu Sulaiman Darazo da Dokta Nasiru Ahmed Ala.

A wani ɓangare na zaman, majalisar ta amince da rahoton kwamitinta na ma’aikata, dangane da ƙorafe-ƙorafen rashin biyan ’yan fansho da albashin ma’aikatan ƙananan hukumomi a faɗin jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Bauchi Ƙananan Hukumomi Majalisar Dokokin Bauchi ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Katsina ta amince da sabuwar Dokar Masarautu

Majalisar Dokki ta Jihar Katsina ta amince da sabuwar Dokar Masarautu ta jihar, bayan ta yi wa daftarin dokar karatu na daya har zuwa na uku.

A sabuwar dokar da aka yi wa kwaskwarima, wadda take jiran sa hannun Gwamna Umaru Dikko Radda, gwamnan jihar ne kadai ke da ikon daga darajar sarki.

Kazalika ta ba wa gwamnan jihar kadai ikon zabar masu zabar sarki, sa’annan ta kara yawan da masu zaben sarki daga mutane hudu zuwa biyar.

Kauran Katsina, Galadiman Katsina, ’Yandakan Katsina da Durbi su ne mutum hudu da aka sani a mastayin masu zabar sarki, amma yanzu dokar ta da Marusan Katsina Hakimin Shargalle, sarautar da aka ba wa tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Sanata Hadi Sirika.

Gobara ta cinye gidan hakimi a Bauchi Nafisa ta cancaci kyautar Dala 100,000 da gida da OON —Pantami Ɗaliba ’yar shekara 15 daga Yobe ta lashe Gasar Muhawara ta Duniya

A makon da ya gabata ne masarautar ta ba wa Hadi Siriki wannan sarauta wadda aka dauke ta daga Dutsi, yayin da ita Dutsin kuma aka mayar da Baburtau a matsayin mukamin Hakimin.

Gabanin wannan sabuwar doka a satin da ya gabata ne Masarautar Katsina ta fitar da sunayen wasu hakiman da aka kirkiro a masarautar.

Bayan waccan sanarwa, sai kuma ga kwafin ita wannan doka wadda majalisar ta yi wa karatu na yawo a kafofin sada zumunta.

Kazalika, akwai ’yan Majalisar Masarautun na Katsina da Daura wadanda aka yi wasu canje-canje.

A yanzu ’yan majalisar sun qunshi wakilai biyu da malamai, biyu daga attajiran jihar, wakili daga sashen kungiyoyin matasa. Sauran su ne, wakilin Kwamishinan Kananan Hukumomi, wakili daga Ma’aikatar Masarautu da masu zaben sarki.

Hatta da Sakataren Majalisa za a turo shi ne daga gwamnati maimakon a da sarki ne ke zabar shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna ya yi wa iyalan ’yan wasan Kano da suka rasu a hatsari goma ta arziki
  • An Fara Gudanar Da Juyayin Cikan Shekaru 80 Da Harin Amurka Da Makamin Nukiliya Kan Hiroshima Na Kasar Japan
  • Xizang Ya Cimma Nasarorin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Suka Kafa Tarihi Cikin Shekaru Fiye Da 60
  • Majalisar Katsina ta amince da sabuwar Dokar Masarautu
  • Gobara ta cinye gidan hakimi a Bauchi
  • Gwamna Yusuf Ya Raba takardun daukar Aiki Ga Sabbin Ma’aikatan Gona Su 1 ,038
  • Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC
  • Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 
  • Gwamnan Jihar Kwara Ya Hori Sabbin Matasa Masu Yiwa Kasa Hidima Akan Kishin Kasa