Leadership News Hausa:
2025-11-05@08:42:05 GMT

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

Published: 6th, August 2025 GMT

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

Ya ce malamin bai fi Sheikh Ahmad Gumi ba, wanda ya gaza yin zaman sulhu da Turji.

Guyawa, wanda ya daɗe yana taimaka wa jami’an tsaro da bayanai, ya ce ba a taɓa yin sulhu da mutum yayin da yake ci wa jama’a zarafi ba.

Ya ce: “Za a iya cewa mutum ya yi sulhu alhali yana ci gaba da karɓar haraji daga hannun manoma da tilasta musu noma? Ko kuma yana kashe mutane da ƙond motar jami’an tsaro?”

Guyawa ya ƙara da cewa Turji da sauran ‘yan ta’adda kamar Kachalla Choma da Kachalla Haru suna da makamai da kwamandoji da yawa, kuma babu wani abu da ke nuna sun ajiye makamansu.

Ya ce malamin da ya faɗi cewa Turji ya ajiye makami bai san yankin ba, kuma bai san halin da ake ciki ba.

A cewarsa, a kwanakin baya ma Turji ya kashe jami’an tsaro tare da ƙone motarsu.

Ya ƙara da cewar idan da gaske ya yi sulhu, da ba zai aikata haka ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Guyawa

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin da Trump ya yi iƙirarin ana kisan Kiristoci a Nijeriya — Ndume

Sanata Ali Ndume ya ce jahiltar halin da Najeriya ke ciki ne ya sa Shugaban Amurka Donald Trump ya yi iƙirarin cewa ana kisan Kiristoci a ƙasar.

Ndume, wanda ke wakiltar mazabar Borno ta Kudu a Majalisar Dattawa, ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise ranar Talata.

Ousmane Dembele zai buga wasan PSG da Bayern Munich ’Yan kwangila sun hana zaman majalisa kan rashin biyan haƙƙoƙinsu

Sanatan ya ce maganganun Trump sun nuna rashin cikakken fahimtar yadda matsalar tsaro take da sarƙaƙiya a Najeriya.

Ya ce matsalar rashin tsaro a ƙasar ta shafi al’umma baki ɗaya ba tare da la’akari bambancin addini ba, yana mai cewa “mutane daban-daban ne ke fuskantar hare-hare daga ‘yan ta’adda, ba Kiristoci kaɗai ba.”

Sanatan ya ƙara da cewa kamata ya yi shugabannin ƙasashen waje su riƙa neman cikakken bayani kafin su yi maganganu da ka iya tada hankali, musamman kan lamurran da suka shafi addini da tsaro.

“Trump bai fahimci haƙiƙanin abin da ke faruwa a Najeriya ba. Matsalar nan ta wuce batun addini, domin dukkan al’ummomi na cikin halin tsoro da fargaba saboda ayyukan ‘yan ta’adda,” in ji Ndume.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An yi musayar yawu tsakanin Barau da Akpabio a majalisa kan barazanar Trump
  • Dalilin da Trump ya yi iƙirarin ana kisan Kiristoci a Nijeriya — Ndume
  • Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno
  • An kama barawo da wayoyin sata 17 a taron sauya shekar Gwamnan Bayelsa
  • Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 
  • Trump ya jaddada shirin Amurka na kai hari a Najeriya
  • El-Zakzaki: Yakin Sudan Yana Kare Maslahar Kasashen Yamma ne Kawai
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • Maganin Nankarwa (3)