Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin gaggauta aiwatar da shirin bayar da kulawar lafiya kyauta ga tsofaffin ma’aikata masu ƙaramin albashi da ke ƙarƙashin tsarin fansho na haɗin gwiwa (Contributory Pension Scheme – CPS), yana mai bayyana shirin a matsayin muhimmin bangare  da zai taimaka wa rayuwarsu.

A wata sanarwa da mai ba Shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, ya fitar, Shugaba Tinubu ya kuma bada umarnin a gaggauta aiwatar da karin fansho da aka dade ana jiran shi, tare da kafa mafi ƙarancin adadin fansho domin kyautatawa tsofaffin ma’aikata mafi rauni a tsarin CPS.

Wannan umarni ya biyo bayan bayani da Daraktar Janar ta Hukumar Kula da Fansho ta Ƙasa (PenCom), Ms. Omolola Oloworaran, ta gabatar wa Shugaban ƙasa.

Shugaba Tinubu ya kuma umurci Daraktar Janar ta PenCom din da ta gaggauta warware matsalar fanshon ’yan sanda da ta daɗe tana ci gaba, yana mai jaddada cewa ’yan sanda samar da tsaro a ƙasa suna da hakkin samun fansho cikin mutuntawa da kwanciyar hankali.

Daraktar Janar din ta kuma sanar da Shugaban ƙasa yadda ake ƙoƙarin kare darajar asusun fansho duba da hauhawar farashi da matsin tattalin arziki, da kuma shirin kaddamar da tsarin ba da gudummawar fansho da kudin waje domin bai wa ’yan Najeriya mazauna ƙasashen waje damar shiga tsarin fansho.

Shugaba Tinubu ya nuna cikakken goyon bayansa ga waɗannan gyare-gyare, yana mai sake jaddada aniyar gwamnatinsa na bunƙasa ci gaba mai ɗorewa da kare rayuwar talakawan Najeriya.

 

Daga Bello Wakili

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin da muke goyon bayan Tinubu kan karɓo bashi — Majalisar Wakilai

Majalisar Wakilai ta bayyana cewa ta amince da duk wasu tsare-tsare da dabarun karɓo rancen kuɗaɗe na Shugaba Bola Tinubu, bisa la’akari da ƙoƙarin da yake yi na farfaɗo da tattalin arziki da kuma rage talauci a ƙasar nan.

Shugaban Majalisar, Abbas Tajudeen ne ya bayyana hakan a yayin da yake jawabi ranar Litinin, a taron shekara-shekara karo na takwas kan bitar kasafin kuɗaɗe na majalisun dokokin nahiyyar Afirka (African Network of Parliamentary Budget Offices) da ke gudana a Abuja.

Sarkin Ruman Katsina ya rasu Jariri ya mutu a bayan uwarsa yayin tsere wa ’yan bindiga a Neja

Abbas ya ƙaryata raɗe-raɗin cewa majalisar ta ƙi amincewa da tsare-tsaren karɓo rance na shugaban ƙasar, inda ya ce zantuka ne marasa tushe da aka ƙirƙira da manufa ta yaudara.

A cewarsa, “kwanan nan, an yi wa jawabin da Shugaban Masu Rinjaye na majalisar ya gabatar a taron majalisun dokoki na Afirka (West African Parliamentary Conference, WAPC) mummunar fassara, har aka rika yi wa majalisar kuskuren fahimta cewar ba ta goyon bayan tsare-tsare da dabarun rancen gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Wannan kuskuren fahimta ne, kuma ba gaskiya ba ce.”

Abbas ya jaddada cewa Majalisar Dokokin Tarayya baki ɗaya, sun amince cewa rance mai tsari cike da kulawa hanya ce da ake amfani da ita wajen gina muhimman ababen more rayuwa, ƙarfafa ci gaban tattalin arziki, da kuma tallafa wa marasa galihu.

Ya bayyana cewa, a ƙarƙashin jagorancin Tinubu, ana karkatar da kuɗaɗen rancen ne zuwa manyan ayyuka da suka haɗa da wutar lantarki, sufuri da noma, waɗanda za su ƙara inganta hanyoyin tattara kuɗaɗen shiga.

Abbas ya kuma tabbatar da cewa duk wani bashi za a karɓo shi ne cikin hikima da kuma tsare-tsaren rance na ƙasar na matsakaicin lokaci da wanda sun dace da duk wasu ƙa’idoji a fadin duniya.

Kazalika, ya jaddada muhimmancin kafa Ofishin Kasafin Kuɗi da Bincike na Majalisa (NABRO) domin yin bincike mai zaman kansa kan batutuwan rance, karɓo bashi da kuma manufofin kuɗi.

Sai dai shugaban majalisar ya yi gargaɗin cewa duk da yake karɓo rancen wajibi ne, amma buƙatar rufe ɓarakar sata da fitar da kuɗaɗen haramun ita ma babban lamari ne da ya zama tilas.

Ya bayyana cewa Najeriya na asarar kusan dala biliyan 18 duk shekara ta hanyar cin hanci da zamba da kuma halasta kuɗaɗen haramun — adadin da ya kai kusan kashi 3.8% na GDP.

Abbas ya ce haɗa rance mai tsari da kuma tsauraran matakan sa ido da yaƙi da cin hanci shi ne zai tabbatar da makomar tattalin arzikin Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNGA: Yau Shettima zai gabatar da jawabin Najeriya a MDD
  • An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m
  • Wa’adin Mulki Ɗaya Kacal Za Ka Yi — ADC Ga Tinubu
  • Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Ɓullar Cutar Mpox A Jihar
  • Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Ɓullar Cutar Mpox A Jihar
  • NEF za ta ƙaddamar da taron zuba jari don bunƙasa Arewa
  • Dalilin da muke goyon bayan Tinubu kan karɓo bashi — Majalisar Wakilai
  • Karin ƙananan hukumomi 2 sun yi sulhu da ’yan bindiga a Katsina
  • Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban Ƙasa
  • Komai Nisan Dare Gari Zai Waye