Aminiya:
2025-08-05@14:53:07 GMT

Majalisar Katsina ta amince da sabuwar Dokar Masarautu

Published: 5th, August 2025 GMT

Majalisar Dokki ta Jihar Katsina ta amince da sabuwar Dokar Masarautu ta jihar, bayan ta yi wa daftarin dokar karatu na daya har zuwa na uku.

A sabuwar dokar da aka yi wa kwaskwarima, wadda take jiran sa hannun Gwamna Umaru Dikko Radda, gwamnan jihar ne kadai ke da ikon daga darajar sarki.

Kazalika ta ba wa gwamnan jihar kadai ikon zabar masu zabar sarki, sa’annan ta kara yawan da masu zaben sarki daga mutane hudu zuwa biyar.

Kauran Katsina, Galadiman Katsina, ’Yandakan Katsina da Durbi su ne mutum hudu da aka sani a mastayin masu zabar sarki, amma yanzu dokar ta da Marusan Katsina Hakimin Shargalle, sarautar da aka ba wa tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Sanata Hadi Sirika.

Gobara ta cinye gidan hakimi a Bauchi Nafisa ta cancaci kyautar Dala 100,000 da gida da OON —Pantami Ɗaliba ’yar shekara 15 daga Yobe ta lashe Gasar Muhawara ta Duniya

A makon da ya gabata ne masarautar ta ba wa Hadi Siriki wannan sarauta wadda aka dauke ta daga Dutsi, yayin da ita Dutsin kuma aka mayar da Baburtau a matsayin mukamin Hakimin.

Gabanin wannan sabuwar doka a satin da ya gabata ne Masarautar Katsina ta fitar da sunayen wasu hakiman da aka kirkiro a masarautar.

Bayan waccan sanarwa, sai kuma ga kwafin ita wannan doka wadda majalisar ta yi wa karatu na yawo a kafofin sada zumunta.

Kazalika, akwai ’yan Majalisar Masarautun na Katsina da Daura wadanda aka yi wasu canje-canje.

A yanzu ’yan majalisar sun qunshi wakilai biyu da malamai, biyu daga attajiran jihar, wakili daga sashen kungiyoyin matasa. Sauran su ne, wakilin Kwamishinan Kananan Hukumomi, wakili daga Ma’aikatar Masarautu da masu zaben sarki.

Hatta da Sakataren Majalisa za a turo shi ne daga gwamnati maimakon a da sarki ne ke zabar shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: dokar masarautu Masarautar Katsina masu zabar sarki Sabuwar Doka

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗaliba ’yar shekara 15 daga Yobe ta lashe Gasar Muhawara ta Duniya

Wata ɗaliba ’yar shekara 15 daga Jihar Yobe, Rukayya Muhammad Fema, ta zama Gwarzuwar Shekarar 2025 a Gasar Muhawara ta Duniya ta Teen Eagle.

Rukayya ta yi zarra ne a wannan babbar gasa da ta gudana a birnin Landan na ƙasar Birtaniya, inda zaƙaƙuran ɗalibai daga ƙasashe 69 a faɗin duniya suka fafata a tsakaninsu.

Jami’in Sadarwar Zamani na Gwamnatin Jihar Yobe, Yusuf Ali, ya bayyana cewa Rukayya ta samu kafa wannan tarihi ne a dalilin zurfin tunani da kuma kaifin basirarta da kuma fahimtar al’amuran duniya, duk kuwa da ƙarancin shekarunta.

Ɗalibar daga Kwalejin Nigerian Tulip International (NTIC), Rukayya, ta ɗauki hankalin alƙalan gasar da sauran jama’a saboda ƙarfin hujjojinta da ta gabatar da kuma iya bayani mai ganawarsa cikin natsuwa, lamarin da ya ba ta damar doke duk abokan karawarta.

Nafisa ta cancaci kyautar Dala 100,000 da gida da OON —Pantami NAJERIYA A YAU: Yadda Ayyuka Suka Ragu A Jihohi Bayan Kudin Shiga Ya Karu

Ita ce mutum ya biyu daga Jihar Yobe kuma daga makaranta tare da Nafisa Abdullah Aminu wadda ta zama gwarzuwa a ɓangaren Harshen Turanci a yayin gasar, inda suka wakilci Najeriya, ƙasa mai yawan al’umma sama da miliyan 200.

Nasararta nuna irin basirar da Allah Ya yi wa matasan Najeriya inda suke yin zarra a sassan duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya
  • Ɗaliba ’yar shekara 15 daga Yobe ta lashe Gasar Muhawara ta Duniya
  • ’Yar shekara 17 daga Yobe ta lashe Gasar Turanci ta Duniya
  • An sace jariri sabuwar haihuwa a asibitin Ekiti
  • Gwamna AbdulRazaq Ya Amince Da Naira Biliyan 20 Don Gyaran Gine-ginen Makarantu A Kwara
  • Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC
  • An yi wa Jalo Daudu sarautar Tafarkin Gombe
  • An yi wa Jalo Daudu a sarautar Tafarkin Gombe
  • Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a