A sakamakon haka, an gurfanar da wanda ake tuhuma a gaban kuliya bisa tuhumarsa kan wannan laifin wanda kuma ya amsa laifin lokacin da aka karanta masa tuhumar.

 

A hukuncin da ya yanke, Alkalin Kotun, Mai shari’a Nasir Ahmad ya yanke hukuncin ɗaurin shekaru biyu a gidan yari, da tarar Naira 20,000, da karin ɗaurin watanni shida a gidan yari, da kuma bulala arba’in.

 

Kotun ta ce, an yanke wannan hukuncin ne don ya zama izini ga masu shirin aikata irin wannan laifin a nan gaba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An kama ’yan bindiga 4 a Kano

An kama wasu mutum huɗu da ake zargin ’yan bindiga ne ɗauke da makamai da ake zaton bindigogi ne a tashar mota ta Ƙofar Ruwa da ke Jihar Kano.

Tashar motar, wadda ke kusa da kasuwar kayan gini ta Ƙofar Ruwa a Ƙaramar Hukumar Dala.

MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a

A cewar mazauna yankin, an kama mutanen ne lokacin da suke ƙoƙarin shiga mota domin tafiya zuwa wani waje a cikin Kano.

“Mutanen da ke tashar motar ne suka lura da makaman da suke ɗauke da su. Take suka gaggauta sanar da jami’an tsaro, waɗanda suka kama su. Su huɗu ne gaba ɗaya,” in ji Musa Balarabe, wani mazaunin yankin.

Ya ce an kama su ne da misalin ƙarfe 1 na rana.

Da farko an kai su ofishin ’yan sanda na Ƙofar Ruwa, kafin daga bisani aka mayar da su ofishin Dala.

Wani mazaunin yankin, Umar Nuhu, ya ce yana cikin shagonsa da ke Kwanar Taya, kusa da ofishin ’yan sandan, lokacin da aka kawo mutanen.

Ya ce hakan ya jawo firgici, inda mutane suka fara gudu a ko’ina.

Nuhu, ya ƙara da cewa mutane da yawa sun yi dandazo a ofishin ’yan sandan, yayin da wasu matasan ke son ɗaukar doka a hannu.

Da aka tuntuɓi kakakin ’yan sandan Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, bai ce komai kan lamarin ba.

Ya ce har yanzu suna tattara bayanai kafin su fitar da sanarwa.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wata sabuwar sanarwa daga rundunar ’yan sandan jihar.

Tashar Kofar Ruwa, tasha ce da ke jigilar fasinjoji zuwa jihohi irin su Katsina, Jigawa, Sakkwato, Zamfara, Kebbi, har ma da Jamhuriyar Nijar.

Wannan na zuwa ne daidai lokacin da Jihar Kano ke fama da hare-haren ’yan bindiga, musamman a yankunan da ke da iyaka da Jihar Katsina.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a Katsina
  • DAGA LARABA: Kalubalen Dake Gaban Janar Christopher Musa A Matsayin Ministan Tsaro
  • Tinubu ya naɗa Janar Christopher Musa sabon Ministan Tsaron Nijeriya
  • NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
  • Wani Dan Adawa Da Gwamnatin Paul Biya Ya Mutu A Gidan Yari A Kasar Kamaru
  • An kama ’yan bindiga 4 a Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • MDD: Kasar Somaliya Tana Fuskantar Mawuyacin Yanayi Saboda Fari
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano