Ma’aikatan gwamnati na amfani da kudaden sata wajen gina rukunin gidaje – EFCC
Published: 7th, August 2025 GMT
Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci ta EFCC, Ola Olukoyede, ya ce galibin rukunin gidajen da aka fara amma aka yi watsi da su a Abuja na ma’aikatan gwamnati ne da suka mallaka da kudaden sata.
Ya bayyana hakan ne a Abuja ranar Laraba yayin wata tattaunawa da wata kungiyar lauyoyi mai suna Law Corridor ta shirya mai taken “Manyan kalubalen da ke fuskantar sana’ar rukunin gidaje a Najeriya“.
Ya ce akwai irin wadannan gidajen da aka yi watsi da su sama da shekara 10, inda ya ce tuni hukumar ta kafa kwamiti na musamman da zai fara ziyartar irin gidajen.
Ola ya ce, “Na kafa kwamitin. Za mu fara ziyartar irin wadannan gidajen ba wai a iya Abuja ba, a duk fadin Najeriya. Muna so mu san mamallakansu.
“Abin da zai ba ka mamaki shi ne wasu daga cikin wadannan gidajen an yi watsi da su sama da shekaru 10 zuwa 20 ba tare da an waiwaye su ba. Kawai da zarar sun kai wani mataki sai a yi watsi da su.
“Babu wanda ya san me ke faruwa. Amma abin da muka iya ganowa shi ne yawancin irin wadannan rukunin gidajen na ma’aikatan gwamnati ne da suka saci kudade.
“Da zarar sun bar aiki sai kudaden su daina shigowa sai su dakatar da aikin. Shi kuma magini sai ya fara neman masu zuba jarin da zai taimaka musu su karasa aikin,“ in ji shi.
Shugaban na EFCC ya ce ko a ’yan kwanakin nan sai da hukumar ta kwace irin wadannan gidajen sama da 15.
“Muna da bayanan sirri. Wasu daga cikinku da ke zaune a nan ma watakila na cikin masu irin wadannan gidajen,“ in ji Shugaban na EFCC.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: irin wadannan gidajen yi watsi da su
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kira Ga Samar Da Tattalin Arziki Da Shugabancin Kwararru
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa tattalin arzikin kasar Iran nan gaba zai ginu ne bisa shirin bayan karewar man fetur ne, inda fasahohi da ilmi da kirkire-kirkire da kuma darussan da za’a dauko daga kasashe kawayen kasar a kungiyoyin BRICS da kuma SCO ne zasu zama abin dogaru.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ya nakalto shugaban yana fadar haka ne a daren jiya Asabar a wani taro wanda yake magana a kan hanyoyin da Iran zata bi don bunkasa fasaha da ilmin kere-keren kasar da samar da ci gaba masu dorewa a kasar. Pezeshkiya yace sauye-suyen da sauri da ake samu a duniya musamman a yankin tekun fariya sun sanya dabarbarun ci gaba na sauyawa da sauri ga kasar Iran.
Ya ce dole ne Iran ta maida hankali wajen samar da dukiya ta hanyar samar da kamfanoni wadanda suka gina ayyukansu kan bincike da ilmi. Mu dauko ilmomin jami’o’immu mu maida su a aikace a cikin kamfanonimmu.
Sanna ya kara da cewa dole ne mu dauki korewar da kasashe mambobi a kungiyoyin BRICS da SCO mu yi amfani da su.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Arakci Ya Kore Cewa Ya Zanta Da Steven Witkoff Na Amurka September 21, 2025 Hizbullah Ta Yi Gayyar Tunawa Da Zagayowar Shahadar Sayyid Hassan Nasrallah September 21, 2025 Hamas Ta Yi Bukaci A Hukunta HKI Akan Rusa Asibitoci September 21, 2025 IRGC: Duk Wani Sabon Kuskuren Abokan Gaba Zai Fuskanci Mayar Da Martani Mai Tsanani September 21, 2025 Israila Ta Kai Hari Kan Wata Mota A Kudancin Labanon September 21, 2025 Iran Za ta Iya Shawo Kan Duk Wani Takunkumi Da Aka Sanya Mata . September 21, 2025 Pakistan:Yarjejeniyar Tsaro Da Suka Kulla Da Saudiya Kamar Kawancen Tsaro Na Nato Ne. September 21, 2025 Matatar Mai Ta Dangote Ta Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai A Nijeriya September 21, 2025 Isara’ila Ta Kaddamar Da Shirin Iko Da Wasu Yankuna A Yammacin Kogin Jodan. September 21, 2025 Iran za ta katse hulda da IAEA idan aka maida mata takunkuman MDD September 20, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci