Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci ta EFCC, Ola Olukoyede, ya ce galibin rukunin gidajen da aka fara amma aka yi watsi da su a Abuja na ma’aikatan gwamnati ne da suka mallaka da kudaden sata.

Ya bayyana hakan ne a Abuja ranar Laraba yayin wata tattaunawa da wata kungiyar lauyoyi mai suna Law Corridor ta shirya mai taken “Manyan kalubalen da ke fuskantar sana’ar rukunin gidaje a Najeriya“.

Gwamna ya yi wa iyalan ’yan wasan Kano da suka rasu a hatsari goma ta arziki Ministocin Ghana biyu sun rasu a hatsarin jirgin sama

Ya ce akwai irin wadannan gidajen da aka yi watsi da su sama da shekara 10, inda ya ce tuni hukumar ta kafa kwamiti na musamman da zai fara ziyartar irin gidajen.

Ola ya ce, “Na kafa kwamitin. Za mu fara ziyartar irin wadannan gidajen ba wai a iya Abuja ba, a duk fadin Najeriya. Muna so mu san mamallakansu.

“Abin da zai ba ka mamaki shi ne wasu daga cikin wadannan gidajen an yi watsi da su sama da shekaru 10 zuwa 20 ba tare da an waiwaye su ba. Kawai da zarar sun kai wani mataki sai a yi watsi da su.

“Babu wanda ya san me ke faruwa. Amma abin da muka iya ganowa shi ne yawancin irin wadannan rukunin gidajen na ma’aikatan gwamnati ne da suka saci kudade.

“Da zarar sun bar aiki sai kudaden su daina shigowa sai su dakatar da aikin. Shi kuma magini sai ya fara neman masu zuba jarin da zai taimaka musu su karasa aikin,“ in ji shi.

Shugaban na EFCC ya ce ko a ’yan kwanakin nan sai da hukumar ta kwace irin wadannan gidajen sama da 15.

“Muna da bayanan sirri. Wasu daga cikinku da ke zaune a nan ma watakila na cikin masu irin wadannan gidajen,“ in ji Shugaban na EFCC.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: irin wadannan gidajen yi watsi da su

এছাড়াও পড়ুন:

Sashen Lafiya Zai Fara Amfani Da Sabuwar Fasahar AI Don Inganta Lafiya

Kwalejin Kiwon Lafiya ta Najeriya ta fara taron shekara-shekara karo na 19 na kimiyya da nufin yin amfani da sabbin fasahohi da kirkire-kirkire wajen kawo sauyi a fannin likitanci a kasar.

 

Da yake yiwa manema labarai jawabi gabanin taron a Sokoto, shugaban kwalejin na kasa, Dokta Peter Ebeigbe ya ce taron zai tattauna hanyoyin da za a bi domin tunkarar manufofi aiwatarwa mai inganci da shigar da kamfanoni masu zaman kansu a fannin ilimin likitanci na gaba da digiri na biyu.

 

Gidan Rediyon Najeriya dake Sokoto ya ruwaito cewa, ana sa ran taron zai kuma tattauna kan ingancin aikace-aikacen kirkirariyar fasaha ta Artificial Intelligence (AI) da illolinsa na isar da sahihanci mai inganci.

 

Shugaban na kasa ya kara da cewa ana sa ran masu hannu da shuni hudu ne zasu jagoranci taron.

 

Nasir Malali

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Wajabcin Haduwar Kasashen Musulmi Wajen Hana Laifukan Gaza
  • Ministocin Ghana biyu sun rasu a hatsarin jirgin sama
  • “Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa
  • Ministan tsaron Ghana da wasu sun rasu a hatsarin jirgin sama
  • Batun Ceto Wanda Ake Zargi Da Kwaya: Kwamishinan Kano Ya Yi Murabus
  • Sashen Lafiya Zai Fara Amfani Da Sabuwar Fasahar AI Don Inganta Lafiya
  • Tinubu ya bai wa ’yan wasan ƙwallon kwandon mata kyautar Dala dubu 100 da gidaje
  • Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule
  • Kano Za Ta Mayar Da Gidan Yarin Kurmawa Zuwa Gidan Tarihi – Gwamnati