Malaman jami’o’i sama da 100 daga Isra’ila sun bayyana cewar jan kafar da ƙasar Jamus ke yi wajen ɗaukar matakin matsin lamba ga gwamnatin Isra’ila na iya bai wa ƙasar damar ci gaba da aikata manyan laifuffuka a Gaza.

Wata wasika da masanan suka rubuta wa ɗaya daga cikin manyan shugabannin jam’iyyar SPD da ke mulki a Jamus, ta ce rashin ɗaukar matakin na iya bada damar gudanar da wasu sabbin laifuffuka a Gaza, tare da watsi da irin tarihin da aka koya a shekarun baya.

A ranar 22 ga watan Yuli, biyu daga cikin jiga jigan kawancen jam’iyyun dake jagorancin Jamus, sun bukaci ƙasar da ta shiga cikin ƙasashen duniya da ke ƙawance domin gaggauta kawo ƙarshen yaƙin Gaza da kuma sanya takunkumi a kan Isra’ila da kuma kin sayar mata da makamai.

Gwamnatin Jamus da ke ƙarƙashin ƙawance jam’iyyun CDU da SCU da kuma SPD ta ƙarfafa sukar da take yiwa gwamnatin Isra’ila a kan yadda take azabtar da mazauna Gaza wajen hana kai musu kayan agaji, amma kuma ya zuwa yanzu bata bayyana ɗaukar wasu matakai masu tsauri ba.

Isra’ilar dai ta yi watsi da duk wani yunkuri na zargin da ake mata na amfani da yunwa wajen azabtar da mutane akalla miliyan biyu dake zama a Gaza, inda ta bayyana cewar ƙungiyar Hamas ce ke sace abincin da ake kai wa mutanen yankin.

Matakan kai hari a kan masu neman kayan agajin da Isra’ila ke yi a kan mazauna Gazar, sun yi sanadiyar hallaka akalla mutane sama da dubu guda.

Kungiyar Hamas ta ƙaddamar da harin da ya hallaka Yahudawa sama da 1,200 a watan Oktobar shekarar 2023, abinda ya sa Isra’ila ƙaddamar da yakin da ya hallaka mutane sama da 50,000 a bangaren Falasdinawa.

Tuni ƙasashen Birtaniya da Canada da kuma Faransa suka bayyana aniyarsu ta amincewa da ƙasar Falasdinu a taron Majalisar Ɗinkin Duniyar da zai gudana a watan Satumba, inda suke cewa ta wannan hanyar ce kawai za a samu zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya.

Isra’ila da Amurka sun bayyana matuƙar ɓacin ransu da matakin, yayin da a yau Firaminista Benjamin Netanyahu ke cewa ba zai dakatar da yakin da yake yi ba har sai ya murkushe ƙungiyar Hamas.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Haramtacciyar Kasar Isra’ila Ita Ce Babbar Tushen Bullar Tashe-Tashen Hankula A Yankin

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Gwamnatin ‘yan sahayoniyya ita ce babbar tushen rashin zaman lafiya a yankin

Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araqchi, yayin da yake magana kan kalaman Fira Ministan gwamnatin ‘yan sahayoniyya ya ce: “Gwamnatin Yahudawan Sahayoniyya ita ce babbar tushen rashin zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya.”

A shafinsa na Twitter, Araqchi ya rubuta cewa: Wannan abin da ake kira “tushen tsaro a Gabas ta Tsakiya” ana nemansa ne saboda kisan kare dangi da laifukan yaƙi. Yana sanya tsarin wariyar al’umma ga Falasdinawa miliyan 7.5, ya jefa bama-bamai a ƙasashe bakwai a bara, kuma ya mamaye yankunan Falasdinawa, Lebanon, da Siriya.

Ya ƙara da cewa: “Gwamnatin ‘yan sahayoniyya tan zama ita ce babbar tushen rashin zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Tabbatar Da Hannun Amurka Wajen Kaddamar Da Yaki Kanta November 8, 2025 Iran Da Mexico Sun Karyata Zarge-Zargen Da Aka Yi Kan Jamhuriyar Musulunci Ta Iran November 8, 2025 Hamas Ta Goyi Bayan Matakin shari’ar Turkiyya Kan Neman kama Masu Take Hakkin Bil’Adama A Isra’ila November 8, 2025 Tarayyar Afirka Ta Yi Kiran Da A Girmama ‘Yancin Kai Na Najeriya Da Rashin Tsoma Baki A Harkokin Gidanta November 8, 2025  Tanzania: An Tuhumi Mutane Da Dama Da Laifin Cin Amanar Kasa Bayan Rikicin Zabe November 7, 2025 Limamin Juma’ar Tehran: Tsayin Dakan ‘Yan Gwagwarmaya Daga Koyi Ne Da Alkur’ani Mai Girma November 7, 2025 Unicef: Kananan Yara 47 ” Isra’ila” Ta Kashe A Yammacin Kogin Jordan November 7, 2025 Tarayyar Turai: Ana Fuskantar Matsananciyar Wahalar Isar Da Kayan Agaji Zuwa Al-Fashar Na Sudan November 7, 2025 Iran Ta Yi Allah Wadai Da Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Lebanon November 7, 2025 Iran Ta Yi Kira Da A Kafa Kwamitin Kasa Da Kasa Don Binciko Falasdiawan Da Suka Bace A Gaza November 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Turkiya Ta Fitar Da Sammacin Kama Natanyaho Da Wasu Jami’ian Isra’ila Kan Yakin Gaza
  • Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
  • Haramtacciyar Kasar Isra’ila Ita Ce Babbar Tushen Bullar Tashe-Tashen Hankula A Yankin
  • Unicef: Kananan Yara 47 ” Isra’ila” Ta Kashe A Yammacin Kogin Jordan
  • Kwamitin Tsaro Ya Dage Takunkumi Kan Manyan Jami’an Gwamnatin Kasar Siriya
  • Zanga zanga Ta Barke A Birmingham Ta Nuna Kin Jin Isra’ila .
  • Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu
  • An rantsar da shugaban Kamaru Paul Biya karo na 8
  • Hafsan sojin sama ya umarci a yawaita yi wa ’yan ta’adda ruwan bama-bamai
  • Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i