Iran: An nada Larijani a matsayin sakataren kwamitin koli na tsaron kasa
Published: 6th, August 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya nada Ali Larijani babban mai baiwa Jagoran juyin juya halin Musulunci shawara a matsayin sabon babban sakataren kwamitin kolin tsaron kasar.
Larijani ya taba rike mukamin sakataren majalisar koli ta tsaron kasar daga ranar 15 ga watan Agustan shekarar 2005 zuwa ranar 20 ga watan Oktoban shekarar 2007, sannan ya rike mukamin kakakin majalisar dokokin kasar Iran daga shekarar 2008 zuwa 2020.
A ranar Lahadin da ta gabata, Iran ta sake gudanar da wasu sabbin canje-canje a kwamitin tsaron kasar, domin yin nazari a kan tsare-tsaren tsaro da kuma karfafa karfin sojin kasar.
Sanarwar da aka fitar a hukumance ta bayyana cewa, shugaba Masoud Pezeshkian ne zai jagoranci kwamitin tsaron, kuma zai hada da shugabannin sassan iko guda uku, wato shugaban kasa, shugaban majalisar dokoki da kuma alkalin alkalai, gami da manyan kwamandojin soji, da ministocin sassan da abin ya shafa.
Majalisar za ta mayar da hankali ne kan tantance dabarun tsaro da kuma inganta karfin soji.
Kafa wannan majalissar ya yi dai-dai da sashe na 176 na kundin tsarin mulkin kasar Iran, wanda ya bai wa kwamitin koli na tsaron kasar damar kirkiro wasu rassa na musamman a lokacin da ya dace don cika bukatun tsaron kasa. Ana sa ran majalisar za ta fara aiki nan ba da dadewa ba, wanda ke nuna wani yunkuri na samar da wasu sabbin dabarun tsaro a daidai lokacin da ake samun ci gaba a yankin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sheikh Qassem: Tsaron Isra’ila zai rushe cikin sa’a 1 idan ta shelanta yaki a kan Lebanon August 6, 2025 Kwamitin Sulhu na MDD ya yi zaman gaggawa kan batun Gaza August 6, 2025 Kamaru: An haramta wa babban dan hamayya tsayawa takara a zaben Oktoba August 6, 2025 Yunkurin Netanyahu na mamaye Gaza ya tayar da balli a Haramtacciyar Kasar Isra’ila August 6, 2025 Araqch: Hadin Kai Tsakanin Cibiyoyi Na Tabbatar Da Karfi Da Ci Gaba August 5, 2025 Wilayati: Iran Ba Za Ta Amince Da Yin Amfani Da Hanyar Zangezur Ta Hanyar Da Bata Dace Ba August 5, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Da Ke Yankin Jaffa Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila August 5, 2025 Dr Muhammad Tahir Da Aka Yi Wa Barazanar Kisa Ya Bayyana Abin Da Ya Gani Na Masifa A Gaza August 5, 2025 An Samu Bullar Sabani Da Rikici Tsakanin ‘Yan Sahayoniyya Game Da Batun Mamaye Zirin Gaza August 5, 2025 Jiniyoyin Gargadi Sun Tashi A HKI Bayan Da Yemen Ta Cilla Sabbin Makamai August 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: tsaron kasar
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Da Japan Suna Iya Jagorantar Duniya Don Rabata Da Makamai Kare Dangi
Ministan harkokin wajen kasar Aran Abbas Aragchi ya bayyana cewa JMI da kuma kasar Japan suna iya jagorantar kasashen duniya zuwa ga rabata daga makaman kare dangi.
Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Ministan yana fadar haka a wani rubutu da yayi, wanda kuma aka buga a jaridar Asahi Shimbun ta kasar Japan. Ya kuma kara da cewa, kasashen biyu an yi amfani da makaman kare dangi a kansu. Y ace kamar yadda Amurka ta yi amfani da makaman nukliya kan kasar Japan a shekara ta 1945 a karshen yakin duniya na biyu, haka nan Sadam ya yi amfanin da makaman guba a kan iraniyawa a kallafeffen yakin da suka fafata na shekaru 8 a tsakaninsu.
Arachi ya ce, kasashen biyu a matsayin kasashen da aka yi amfani da makaman kare dangi a kansu suna iya samar da wata motsi a duniya wacce za’a iya kaiwa ga lalata dubban makaman kare dangi a duniya.
Ministan yayi wannan rubutun ne don taya kasar Japan jejen kashe dubban mutanen kasar da makaman nukliya a shekara 1945, wanda a yau yake cika shekaru 80 da faruwa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kungiyar Hamas Ta Bayyana Cewa Ba za ta Ajiye Makamanta ba Sai Bayan samar Da Kasar falasdinu August 3, 2025 Kungiyar Hamas Ta Wallafa Hotunan bidiyo Na Fursinan HKI tsare A Gaza August 3, 2025 Sojojin HKI, Daga Jiya Zuwa Yau lahadi Kadai Sun Kashe Falasdinawa 62 August 3, 2025 Pezeskkian Ya Ce: Suna Fatan Musayar Kasuwancin Tsakanin Iran Da Pakistan Ta Haura Dala Biliyan 10 August 2, 2025 Araqchi: Abokantaka Da Ke Tsakanin Iran Da Pakistan Wata babbar Jari Ce Nan Gaba August 2, 2025 Jaridar Isra’ila Ta Ce: Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ta Sha Kashi A Yakin Gaza August 2, 2025 Dakarun Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Da Ke Haramtacciyar Kasar Isra’ila August 2, 2025 Rahoton Majalisar Dinkin Duniya Ya Yi Gargadi Kan Barazanar Kungiyoyin ‘Yan Ta’adda A Afirka August 2, 2025 Shugaba Pezeshkiyan Ya Yi Juyayin Shahadar Haniya Bayan Shekara Guda Da Shahada August 2, 2025 MDD: HKI Ta Kashe Falasdinawa Fiye Da 100 A Cikin Kwanaki 2 A Lokacinda Suka Karban Abinci August 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci