Sheikh Qassem: Tsaron Isra’ila zai ruguje cikin sa’a 1 idan ta shelanta yaki a kan Lebanon
Published: 6th, August 2025 GMT
Babban sakataren kungiyar Hizbullah Sheik Naim Qassem ya jaddada cewa, ba a samu wani abu na keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta ba daga bangarenmu ba, amma Isra’ila ta keta wannan yarjejeniya sau dubbai.
Da yake jawabi a wajen taron cika kwanaki 40 da shahadar Birgediya Janar Mohammad Saeed Izadi (Hajji Ramadan), Sheikh Qasem ya bayyana cewa, Haramtacciyar Kasar Isra’ila tana fatan ganin an kwace makaman Hizbullah, ta yadda hakan zai bata damar cin karenta babu babbaka a kan kasar Lebanon.
Ya ci gaba da cewa, “Abin da ya faru a Siriya ya yi tasiri matuka kan matakan da Isra’ila ta dauka, wanda hakan ya sanya ta yi nadama wajen tsara yarjejeniyar.
Shugaban na Hizbullah ya jaddada cewa, Amurka ce ta tsara dukkanin bukatu da aka gabatar da nufin raunana kasar Labanon da kungiyar Hizbulah, da al’ummar Lebanon baki daya, domin hakan ne kawai zai amfanar da muradun Isra’ila a kan kasar ebanon.
Ya kuma tattauna abubuwan da wakilin Amurka Tom Barrack ya rubuta, wanda ya bayyana a matsayin “mafi muni” fiye da nau’i biyu na baya. Sheikh Naim Qassem ya yi nuni da cewa, daya daga cikin muhimman bukatun nasa shi ne kungiyar Hizbullah ta ruguza rabin kayayyakin aikinta na soji a cikin wata guda, sannan Isra’ila ta fice daga wurare masu muhimmanci guda uku kawai daga cikin biyar din da ta mamaye a kudancin Lebanon.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kwamitin Sulhu na MDD ya yi zaman gaggawa kan batun Gaza August 6, 2025 Kamaru: An haramta wa babban dan hamayya tsayawa takara a zaben Oktoba August 6, 2025 Yunkurin Netanyahu na mamaye Gaza ya tayar da balli a Haramtacciyar Kasar Isra’ila August 6, 2025 Araqch: Hadin Kai Tsakanin Cibiyoyi Na Tabbatar Da Karfi Da Ci Gaba August 5, 2025 Wilayati: Iran Ba Za Ta Amince Da Yin Amfani Da Hanyar Zangezur Ta Hanyar Da Bata Dace Ba August 5, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Da Ke Yankin Jaffa Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila August 5, 2025 Dr Muhammad Tahir Da Aka Yi Wa Barazanar Kisa Ya Bayyana Abin Da Ya Gani Na Masifa A Gaza August 5, 2025 An Samu Bullar Sabani Da Rikici Tsakanin ‘Yan Sahayoniyya Game Da Batun Mamaye Zirin Gaza August 5, 2025 Jiniyoyin Gargadi Sun Tashi A HKI Bayan Da Yemen Ta Cilla Sabbin Makamai August 5, 2025 Iran Ta Kafa Kwamitin Tsaron Kasa Wanda Zai Kula Da Sabbin Matsalolin Tsaro August 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Isra ila ta
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Jinjinawa Al’ummar Iran Kan Namijin Kokarinsu
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Al’ummar Iran sun dakile shirin ‘yan sahayoniyya a yakin kwanaki 12
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Al’ummar Iran sun dakile shirin yahudawan sahayoniyya a yakin kwanaki 12 da aka kwashe ana gwabzawa. A lokacin da yake halartar taron manema labarai da kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Ismail Baqa’i ya gudanar a yau Litinin, Araqchi ya ce: Na farko dai ya zama wajibi a gare shi ya girmama dukkanin shahidai: shahidan juyin juya halin Musulunci, shahidan tsaro mai alfarma (1980-1988), da dukkanin shahidan da suka sadaukar da rayuwarsu wajenkare kasa, tun farko-farko har zuwa yau, musamman ‘yan jaridu da shahida yakin matsorata masu wuce gona da iri na yakin kwanaki 12.”
Ministan harkokin wajen kasar ya kara da cewa: Babu shakka wannan yaki zai kasance daya daga cikin abubuwan da ba za a taba mantawa da shi ba a tarihin Iran na yau da kullum, yakin da gwamnatin ‘yan sahayoniyya masu laifi tare da goyon baya da hadin gwiwar manyan kasashen duniya da sauran su suka kaddamar na wuce gona da iri kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran tare da fatan cimma munanan manufofinsu da wani harin ba-zata cikin kankanin lokaci, to sai dai al’ummar Iran sun sake tabbatar cewa sun yi tsayin daka tare da zage dantse babu abin da zai kawar da su kan azamarsu, saboda mutane suna ne da saiwoyinsu suka shimfiɗa a cikin kasa sama da dubban shekaru, saiwoyin suke kara karfi kowace rana, ƙasar da ta wanzu saboda sadaukarwa, da tsayin daka, da Imani.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Iran Ko Da Zata Sake Tattaunawa Da Amurka Zata Kasance Dauke Da Makamai Cikin Shirin August 4, 2025 Rahotonni Sun Bayyana Cewa; Agajin Jin kai Da Ake Wurga Ta Sama A Gaza Tamkar Digon Ruwa Ne August 4, 2025 Wa’adin Da Shugaban Amurka Ya Gindaya Na Kawo Karshen Yaki A Ukraine Ya Karato Ba Tare Da Alamun Karewarsa Ba August 4, 2025 Sojojin Somaliya Sun halaka Mayakan Kungiyar Al-Shabab Fiye Da Hamsin A Kudu Maso Yammacin Mogadishu August 4, 2025 Pakisatan: Iran Ce Madogara Ga Al-ummar Musulmi August 4, 2025 Wakilin Hukumar FAO A Iran Yace Sauyin Yanayi Ya shafi Dukkan Yankin August 4, 2025 Malamai A Najeriya Suna Goyon Bayan Iran A Yadda Take Fuskantar HKI August 4, 2025 Shugaban Kasar Lebanon Ya Yi Alkawalin Adalci Ga Wadanda Feshewar Beirut Ta Shafa August 4, 2025 Iran Ta Ce Ba Wani Ma’aikacin Hukumar IAEA A Kasar A Halin Yanzu August 4, 2025 Pezeshkian ya yaba da irin goyon bayan da Pakistan ta baiwa Iran a lokacin yaki August 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci