Aminiya:
2025-08-05@21:29:24 GMT

Mulkin Tinubu ya fi na Buhari muni — Maina Waziri

Published: 5th, August 2025 GMT

Tsohon Ministan Harkokin ’Yan Sanda, Adamu Maina Waziri, ya caccaki Shugaba Bola Ahmed Tinubu da cewa gwamnatinsa ta kere ta tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta fuskar muni, wanda a yanzu ƙasar tana cikin mummunan bala’i. 

Waziri, wanda jigo ne a jam’iyyar ADC (African Democratic Congress), ya bayyana haka ne a yayin wata tattaunawa da aka yi da shi a gidan talabijin na Trust TV.

’Yan gida ɗaya sun kitsa garkuwar ƙarya domin karɓar N5m a wurin mahaifinsu Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 17 a Borno da Adamawa

“Babu ta inda gwamnatin Tinubu ba ta gaza ba. Ta gaza a dukkan fannoni, kama daga kan tsaro, tattalin arziki, yaƙi da cin hanci saboda komai ya tabarbare. Nijeriya ta koma baya sosai a ƙarƙashin mulkinsa,” in ji shi.

Duk da ya amince an tafka kura-kurai a gwamnatin Buhari, Waziri ya ce a ganinsa Tinubu ya yi wa tsohon shugaban ƙasar fintinkau ta fuskar gazawa.

Tsohon Ministan ya bayyana cewa mulkin shugaba Tinubu ya jefa ’yan Nijeriya cikin ƙuncin rayuwa, musamman tun bayan janye tallafin mai da sauye-sauyen tattalin arziki, wanda ya janyo hauhawar farashin kaya da ƙarancin abinci.

Ya kuma soki yadda wasu ’yan siyasa ke nuna goyon baya ga gwamnatin Tinubu saboda saboda son zuciya da wani ra’ayi na ƙashin kai, yana mai cewa “wadannan mutanen su kansu suna cikin tsaka mai wuya, amma sai su riƙa yabon gwamnati saboda siyasa.”

Ya ce yana mamakin irin waɗannan mutane musamman waɗanda yankunansu ke fama da hare-haren ’yan bindiga da rashin tsaro za su riƙa fitowa a kafafen watsa labarai suna goyon bayan gwamnati, lamarin da ya bayyana a matsayin mai ɗaure kai.

“Ina mamakin yadda wasu mutane waɗanda ƙananan hukumominsu ke ƙarƙashin ikon ’yan bindiga za su iya fitowa a talabijin na ƙasa su na yabon wannan gwamnati,” in ji shi.

Waziri ya ƙara da cewa, a yanzu Nijeriya na buƙatar shugabanci nagari, wanda babu makirci da ruɗu a cikinsa, saboda haka babu wata gwamnati da ta rasa ƙima irin wannan da za ta nemi wa’adi na biyu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Adamu Maina Waziri Muhammadu Buhari

এছাড়াও পড়ুন:

Wulayati: Iran Zata Mayar Da Martani Kan Gwamnati Da Ke Neman Yin Amfani Da Hanyar Zangezur Ta Hanyar Da Bata Dace Ba

Mai ba da shawar ga Jagora ya jaddada cewa: Iran za ta mayar da martani da karfi ga duk wata gwamnati da ke neman yin amfani da hanyar Zangezur ta hanyar da ba ta dace ba

Ali Akbar Wulayati, mai ba da shawara ga Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran kan harkokin kasa da kasa, ya yi gargadin cewa: “Duk wata gwamnati a yankin ko a wajenta da ke son maimaita gwajin da aka yi a baya game da hanyar Zangezur, za ta fuskanci martani mai karfi daga Iran.”

A shafinsa na Twitter, Ali Akbar Welayati ya rubuta cewa: “A nan ma, wasu gwamnatocin da ba su nuna halin ko-in-kula ba, ba ruwansu da muradun kansu da na yankin, sun tabo batun hanyar Zangezur tare da buga kowace kofa don cimma haramtattun manufofinsu a yankin Kudancin Caucasus.”

Ya kara da cewa: Yana so ta tunatar da ku cewa duk wata gwamnati a yankin ko a wajenta da ke son maimaita gwajin da aka yi a baya, za ta fuskanci martani mai karfi daga Iran.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Da Ke Yankin Jaffa Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila August 5, 2025 Dr Muhammad Tahir Da Aka Yi Wa Barazanar Kisa Ya Bayyana Abin Da Ya Gani Na Masifa A Gaza August 5, 2025 An Samu Bullar Sabani Da Rikici Tsakanin ‘Yan Sahayoniyya Game Da Batun Mamaye Zirin Gaza August 5, 2025 Jiniyoyin Gargadi Sun Tashi A HKI Bayan Da Yemen Ta Cilla Sabbin Makamai August 5, 2025 Iran Ta Kafa Kwamitin Tsaron Kasa Wanda Zai Kula Da Sabbin Matsalolin Tsaro August 5, 2025 Rasha Zata Kara Kyautata Dangantaka BRICS don Magance Takunkuman Amurka A Kanta August 5, 2025 Gagarumar Zanga-Zang A birnin Paris Na kasar Faransa Saboda Killace Gaza August 5, 2025 Burtaniya Zata Fara maida yan Gudun Hijira Zuwa Faransa Bisa Wata Sabuwar Yarjeniya August 5, 2025 Borrell: Rashin tabuka komai daga Turai ya karfafa gwiwar Isr’ila wajen aikata laifuka August 5, 2025 UNICEF: Akalla yara 28 ne ke mutuwa a kowace rana a Gaza sakamakon harin Isra’ila da yunwa August 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wulayati: Iran Zata Mayar Da Martani Kan Gwamnati Da Ke Neman Yin Amfani Da Hanyar Zangezur Ta Hanyar Da Bata Dace Ba
  • Gagarumar Zanga-Zang A birnin Paris Na kasar Faransa Saboda Killace Gaza
  • LASTMA Ta Rufe Gidan Casu A Legas Saboda Karya Dokar Hanya
  • Tinubu ya bai wa ’yan wasan ƙwallon kwandon mata kyautar Dala dubu 100 da gidaje
  • Gwamnatin Kano Ta Karɓi Rahoton Binciken Kwamishinan Sufuri Kan Belin Wanda Ake Zargi Da Safarar Kwayoyi
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara
  • Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi
  • Kano Za Ta Mayar Da Gidan Yarin Kurmawa Zuwa Gidan Tarihi – Gwamnati
  • Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC