Gwamnatin kasar Sin ta samar da kudi har yuan biliyan 1.015, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 142 ga lardunan kasar daban daban, domin gudanar da ayyukan jin kai, sakamakon ibtila’in ambaliyar ruwa da ta shafi wasu sassan kasar.

Rahotanni na cewa ma’aikatar kudin kasar, da ma’aikatar gona da raya karkara, da ma’aikatar albarkatun ruwa ne suka samar da kudaden, wadanda za a yi amfani da su a ayyuka daban daban na tallafawa yankunan da ambaliyar ta shafa, ciki har da birnin Beijing, da lardin Hebei, da Mongolia ta gida da Guangdong.

Kana cikin kudin za a samar da tallafin sake shukar da ruwa ya lalata, da ma kayayyakin aikin gona da ambaliyar ta shafa.

Kazalika, za a yi amfani da bangaren kudin wajen tallafin shawo kan fari a lardunan Shandong, da Henan, da Hubei da wasu karin sassan kasar, ta hanyar bayar da tallafin taki, da adana irin shuka, da ban ruwa domin noman rani da tona rijiyoyi. (Mai Fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Lebanon

Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta yi Allah wadai da cin zarafin da gwamnatin mamayar Isra’ila ke yi wa Lebanon

Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta yi Allah wadai da babban harin soji da gwamnatin mamayar Isra’ila ta kai kan kasar Lebanon, tana dora alhakin kai harin kan Majalisar Dinkin Duniya, al’ummun duniya, da kuma kasashen yankin kan abin da ta bayyana a matsayin halin gwamnatin mamayar Isra’ila na kokarin tayar da masifar yaƙe-yaƙe.

Ma’aikatar ta tabbatar da cikakken hadin kan Iran ga gwamnatin Lebanon da al’ummarta a kan wadannan hare-haren ta’addanci, tana mai jaddada goyon bayanta ga halaltacciyar gwagwarmaya wajen kare ikon mallakar Lebanon.

Ta kara da cewa; Hare-haren soji da gwamnatin ‘yan Sahayoniyya take kai wa kan Lebanon, wadanda suka yi sanadiyyar shahada da jikkata sama da ‘yan kasar Lebanon dubu daya da ba su ji ba ba su gani ba, da kuma lalata kayayyakin more rayuwa da wuraren zama tun bayan yarjejeniyar tsagaita wuta ta watan Nuwamban shekara ta 2025, sun zama wani abu da ya saba wa ikon mallakar kasa da kuma ikon mallakar kasa mai cin gashin kanta, kuma ana daukar su a matsayin babban laifi ga zaman lafiya da tsaro na kasa da kasa.

Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta bayyana cewa wadannan hare-haren ta’addanci, wadanda babu shakka suka shirya kuma suka aiwatar tare da cikakken goyon baya da hadin gwiwar Amurka, sun kara tabbatar da yanayin aikata laifuka, ta’addanci, da fadada kasar kwace na Sahayoniyya, kuma ba su da wata manufa illa su lalata ikon mallakar Lebanon da tsaronta da kuma hana sake ginata da ci gaban kasar.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Yi Kira Da A Kafa Kwamitin Kasa Da Kasa Don Binciko Falasdiawan Da Suka Bace A Gaza November 7, 2025 Babban Matsalar Jin Kai A Falasdinu, Inda Falasdinawa Miliyan 1.5 Suke Cikin Halin Bala’i November 7, 2025 Kwamitin Tsaro Ya Dage Takunkumi Kan Manyan Jami’an Gwamnatin Kasar Siriya November 7, 2025 Karuwar Matsalar Jin Kai Mafi Girma A Duniya A Sudan Saboda Ci Gaba Da Masifar Yaki A Kasar November 7, 2025 An Rantsar Da Paul Biya A Matsayin Shugaban Kamaru Karo Na Takwas November 7, 2025 Dakarun Sojin Kasar Sudan Sun yi Watsi Da Batun Dakatar Da Bude Wuta Da Amurka Ta Gabatar November 7, 2025 Zanga zanga Ta Barke A Birmingham Ta Nuna Kin Jinin Isra’ila . November 7, 2025 Pezeshkiyan: Masu Kawo Rarraba Tsakanin Musulmi Suna yi wa Yan Sahayuniya Aiki Ne November 7, 2025 Shugaban Najeriya Bola Tinubu Ya yi Alwashin Kawo Karshen Ta’addanci A Kasar November 7, 2025 Araqchi Ya Ce: Harin Amurka Kan Kasar Venezuela Ya Bayyana Karara Duniya Tana Gani November 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu
  • An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu!
  • Sama da gidaje 8,000 za su samu wutar lantarki daga hasken rana a Gombe
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Lebanon
  • Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho
  • Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
  • Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
  • Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa