Ruftawar gini ta kashe uwa da ’ya’yanta 5 a Katsina
Published: 6th, August 2025 GMT
Wata uwa da ’ya’yanta biyar sun riga mu gidan gaskiya a dalilin ruwan sama kamar da bakin ƙwarya wanda ya janyo ruftawar ginin gidansu a ƙauyen Dankama da ke Karamar Hukumar Kaita a Jihar Katsina.
Aminiya ta ruwaito cewa, lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe biyu na dare a ranar Litinin yayin da waɗanda ajalin ya katsewa hanzari ke tsaka da barci.
Bayanai sun ce wasu mutum huɗu waɗanda su ma lamarin ya rutsa da su an gaggauta miƙa su asibiti domin samun kulawa.
Magidancin da aka yi wa wannan babban rashi, Muhammad Sani Garba, yayin ganawa da manema labarai ya ce ba ya gida lokacin da tsautsayin ya auku.
“Wannan tsautsayi ya rutsa da mutum goma, amma abin baƙin ciki, shida daga cikinsu sun rasu. A halin yanzu, mutum huɗu suna asibiti ana duba lafiyarsu,” in ji shi.
“Na ɗauki wannan a matsayin ƙaddara daga Ubangiji. Allah Ya jiƙansu, Ya sanya su a Aljannar Firdausi,” a cewarsa.
Daraktar Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Katsina (SEMA), Hajiya Binta Dangani, ta tabbatar da faruwar lamarin, tana mai cewa ma’aikatan hukumar sun ziyarci wurin da lamarin ya faru domin tantance halin da ake ciki da ɗaukar matakin gaggawa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Katsina Ruftawar gini
এছাড়াও পড়ুন:
An cafke mutum 6 kan tono gawa a kabari don yin asiri a Gombe
Hukumar Sibil Difens (NSCDC) a Jihar Gombe, ta kama mutum shida bisa zargin tono gawar wani mutum a kabari tare da cire sassan jikinta domin yin asiri.
Ɗaya daga cikin waɗanda aka kama, Kawuji Sarki, mai shekaru 39, ya amsa laifin.
Wata mata ta ƙona al’aurar ’yarta da wuta kan zargin maita a Bauchi Janye Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya koma RibasYa bayyana cewa wani mutum mai suna Aliyu Chindo ne, ya ba su aikin cire idanun mamacin, tare da yi wa kowannensu alƙawarin Naira 500,000.
Sai dai ya ce bayan kai masa sassan jikin, Chindo ya gudu ba tare da ya biya su ba.
Nan take jami’an tsaro suka cafke su.
An gano cewa sun tono kabarin wani tsoho mai shekaru 85, Mallam Manu Wanzam, wanda aka binne a ranar 9 ga watan Satumba a maƙabartar Gadam Arewa da ke Ƙaramar Hukumar Kwami.
Kakakin NSCDC a jihar, SC Buhari Sa’ad, ya bayyana sunayen sauran da aka kama: Adamu Umar (22), Umar Jibrin Aboki (21), Abdullahi Umar Dauda (17), Muhammed Isa Chindo (28), da Manu Sale (23).
Ya ƙara da cewa ana ci gaba da neman Aliyu Chindo da ya tsere.
Kwamandan hukumar a jihar, Jibrin Idris, ya bayyana lamarin a matsayin “rashin imani,” tare da tabbatar da cewa za su gurfanar da waɗanda suka kama a kotu bayan kammala bincike.