Aminiya:
2025-11-04@15:54:23 GMT

Kwamishina ya yi murabus kan ƙarbar belin dillalin ƙwayoyi a Kano

Published: 6th, August 2025 GMT

Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi, ya yi murabus daga muƙaminsa saboda ce-ce-ku-ce da ya biyo bayan karɓar belin wani wanda ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi da ya yi.

Namadi ya yi murabus ne sa’o’i kaɗan bayan da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya karɓi rahoton kwamitin bincike da ya kafa kan lamarin.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Namadi ya ce ya yanke shawarar yin murabus ne don “amfanin jama’a gaba daya” da kuma kare gwamnatin a “yaƙin da take yi da sayarwa da shan miyagun kwayoyi.”

Sai dai ya dage kan cewa ba shi da laifi, amma ya yarda cewa ra’ayin jama’a na da muhimmanci, kuma yana da kyau ya kare kimar gwamnatin.

Tuni Gwamna Abba Kabir Yusuf ya karɓi murabus ɗin tare da yi wa tsohon kwamishinan fatan alheri.

Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya ce Gwamnatin Jihar Kano na ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da adalci da yaƙi da laifukan da suka shafi miyagun ƙwayoyi.

Gwamna Abba ya kuma jaddada muhimmancin dukkan jami’an gwamnati su riƙa yin taka-tsantsan da neman izini daga manyan hukumomi kan batutuwa masu mahimmanci na jama’a.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: belin dillalin miyagun ƙwayoyi ƙwayoyi Murabus zargi

এছাড়াও পড়ুন:

An kama barawo da wayoyin sata 17 a taron sauya shekar Gwamnan Bayelsa

Jami’an tsaro sun kama wani mutum da wayoyin sata guda 17 da kuma kudi a wurin taron sauyin shkear Gwamna Douye Diri daga Jam’iyyar PDP zuwa APC.

A ranar taron, Gwamna Diri tare da yawancin ’yan majalisar dokokin jihar Bayelsa sun sanar da ficewarsu daga jam’iyyar PDP zuwa APC, a gaban Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, da wasu gwamnoni da manyan jami’an siyasa na ƙasa.

Shugaban sa-kai na jihar, Doubiye Alagba, wanda ya jagoranci kama wanda ake zargin, ya bayyana cewa an mika mutumin ga jami’an Operation Puff Adder na rundunar ’yan sandan jihar domin gudanar da cikakken bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.

A cewar Alagba, wanda ake zargin ya amsa laifinsa, inda ya ce ya shigo daga jihar Ribas ne musamman domin amfani da taron siyasar da aka shirya wajen yin sata.

Karuwanci da zubar da cikin ’yan mata ’yan gudun hijira ya karu a Maiduguri NAJERIYA A YAU: Rashin aikin yi da hanyoyin magance su a Najeriya

Ya ce jami’ansu sun kama shi ne bayan sun lura da motsinsa da ya sa suka zarge shi. Bayan bincike, sai suka gano wayoyi 17, kudi N91,000, da kuma katunan ATM da dama a cikin jaka da yake dauke da ita.

Alagba ya kara da cewa, Francis ya shaida musu cewa yana aiki tare da wasu abokan laifi da suka tsere yayin kamun.

Ya kuma bayyana cewa kafin a kama shi, sun riga sun kwashe sama da N400,000, sannan daya daga cikin wadanda suka gudu yana da karin wayoyi da sauran kayayyakin da suka sace.

Shugaban sa-kai din ya gargadi masu aikata laifuka da su guji shiga Bayelsa, yana mai cewa jami’ansa sun samu horo na musamman kan tattara bayanan sirri, lura da halayen jama’a da kuma tsaron taruka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama barawo da wayoyin sata 17 a taron sauya shekar Gwamnan Bayelsa
  • Gwamna Namadi Ya Yaba Da Tasirin Shirin NG-CARES A Jihar Jigawa
  • Abba ya umarci a riƙa gudanar da taron tsaro a ƙananan hukumomin Kano
  • Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya
  • Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT
  • Uwargidan Gwamnan  Zamfara Ta Yaba Wa  Karamar Hukumar Gusau Bisa Shirin Tallafawa Jama’a
  • NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Yabawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Hanyoyi A Fadin Jihar
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci