Aminiya:
2025-05-04@05:37:01 GMT

An kama masu garkuwa da mutane 3 da kuɓutar da wasu

Published: 3rd, May 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta sashen tawagarta masu tattara bayanan sirri (IRT), ta kuɓutar da wasu ’yan ƙasar Ghana biyu da aka yi garkuwa da su tare da damƙe wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da ke aiki a kan iyakokin ƙasashen duniya.

Rundunar ’yan sandan a ranar Juma’ar  ta ce hakan ya biyo bayan rahoton da aka shigar gaban babban ofishin hukumar a Abuja a ranar 27 ga Afrilu, 2025, game da yin garkuwa da wani Anastasia Arthur da aka fi sani da Baidoo, ɗan ƙasar Ghana mai shekara 48.

An gano shanu 25 da suka ɓace a dajin Sakkwato ’Yan kungiyar asiri: Mutum 95 sun shiga hannu a Edo

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Olumuyiwa Adejobi, ya fitar, ta bayyana cewa binciken farko ya nuna cewa sace Baidoo ya samo asali ne daga wata zamba ta soyayya ta Facebook.

Adejobi ya ce ci gaba da bincike na fasaha ya nuna wani muhimmin wuri da ke da alaƙa da waɗanda suka aikata laifin, kuma an tura jami’ai domin ɗaukar mataki cikin gaggawa.

Ya ce, tare da haɗin gwiwa da hukumar ’yan sandan Ghana, jami’an IRT sun gano wata ƙungiyar masu aikata laifuka da masu garkuwan da ke aiki a ƙasashen Ghana da Najeriya.

Ya ce, “Babban nasarar da aka samu a binciken sun haɗa da kama wani Emeka Christian, ɗan Najeriya mai shekara 27 da ke zaune a Bolgatanga, Upper Eastern Ghana, wanda ya amsa laifin karɓar kuɗi cedis GH10,000 a matsayin kuɗin fansa ga wanda aka yi garkuwa da shi ta hanyar asusun wayarsa na Ghana.

“Ya kuma amince da tura Naira kwatankwacin kuɗin zuwa wani asusun bankin Najeriya mallakar wani Peter Okoye.”

 

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Masu Garkuwa da mutane

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Rigunan Kariya Ga Wasu Jihohin Najeriya.

Gwamnatin tarayya ta kaddamar da wayar da kan al’umma kan kare lafiyar ruwa tare da raba riguna a wasu zababbun Jihohin Najeriya.

 

Ministan Tattalin Arzikin Ruwa, Adegboyega Oyetola wanda ya kaddamar da taron a gidan gwamnati, Minna ya ce wannan ra’ayin ya yi daidai da jajircewar Gwamnatin Tarayya na kare rayuka da dukiyoyin al’umma da rayuwar ’yan Najeriya da ke dogaro a kullum kan hanyoyin ruwa na cikin kasa wajen sufuri da kasuwanci.

 

Ya amince da dimbin karfin tattalin arzikin magudanan ruwa a kasar nan da ke fama da tashe-tashen hankula sakamakon yawaitar hadurra na kwale-kwalen da ke bukatar hada kai, da kuma daukar matakai bisa dabaru don haka aka fara raba riguna 3,500 a matakin farko ga jihohi 12 ciki hadda jihar Neja.

 

Ministan wanda ya yabawa Gwamna Umar Bago bisa ga kokarin da yake yi na ganin ya inganta harkokin sufurin koguna a cikin Jihar tare da sayo da rarraba jiragen ruwa guda biyar ya yi kira ga sauran gwamnonin Jihohi da shugabannin al’umma da su yi koyi dashi.

 

A nasa jawabin gwamnan jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya ce gwamnati tare da hadin gwiwar hukumar kula da hanyoyin ruwa ta kasa NIWA da sauran masu ruwa da tsaki za su aiwatar da aikin da aka wajaba na amfani da rigar kariya da kuma bin dukkan ka’idojin kiyaye hanyoyin ruwa a jihar.

 

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Neja, Abdulmalik Sarkin Daji ya wakilce shi ya yi tir da yadda ake tafka ta’asa a cikin kwale-kwale a jihar inda ya ce gwamnatin jihar ta gano musabbabin hatsarin kwale-kwale a jihar kuma ta kuduri aniyar magance ta ta hanyar tabbatar da doka da oda da kuma zuba jari a hanyoyin ruwa.

 

Manajan Darakta kuma babban jami’in gudanarwa na hukumar kula da hanyoyin ruwa ta kasa NIWA, Bola Oyebamiji wanda shi ma ya amince da kudurin Gwamna Bago na magance matsalolin da suka shafi harkar sufurin ruwa, ya bayyana bukatar kara karfafa hadin gwiwa da abokan hulda wajen dakile bala’in da jiragen ruwa ke tafkawa a hanyoyin ruwa.

 

Kwamishiniyar Sufuri, Hajiya Hadiza Idris Kuta ta yabawa ma’aikatar harkokin ruwa da tattalin arzikin kasa bisa tallafin da take baiwa jihar Neja da samar da motocin daukar marasa lafiya da kwale-kwalen fasinja da suka hada da samar da jami’an kula da ruwa da aka jibge a yankunan gabar tekun jihar yayin da ta kuma yarda cewa rigunan ceton da aka raba wa jihar zai taimaka matuka.

 

Etsu Nupe kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Jihar Neja Alh, Yahaya Abubakar wanda Wambai Nupe, Injiniya Ndagi Aliyu ya wakilta ya sake jaddada bukatar cibiyoyi na gargajiya a matsayinsu na masu ruwa da tsaki a matakin kasa da su kara kaimi wajen wayar da kan al’ummarsu kan bukatar kiyaye hanyoyin ruwa.

 

KARSHEN ALIYU LAWAL.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kama jami’an tsaro da ke haɗa baki da ’yan ta’adda
  • An gano shanu 25 da suka ɓace a dajin Sakkwato
  • ’Yan kungiyar asiri: Mutum 95 sun shiga hannu a Edo
  • An Kama Wani Babban Jami’in Sojan Kasar Burtaniya A Najeriya Tare Da Zarginsa Da Shigo Da Makamai
  • An kama mutane 1,611 da ƙwato motoci 21, babura 51 da aka sace a Abuja
  • ’Yan acaba sun yi wa mai fura fyaɗe Abuja
  • Gwamnatin Tarayya Ta Raba Rigunan Kariya Ga Wasu Jihohin Najeriya.
  • An Bada Gudummawar Kekunan ga Masu Bukatu Na Musamman A Birnin Kebbi.
  • An Bukaci Masu Yiwa Kasa Hidima Su Yi Amfani Da Kafofin Sadarwa Na Zamani Don Inganta Hadin Kan Kasa.