Aminiya:
2025-08-01@16:02:11 GMT

Fasinjoji 16 sun ƙone ƙurmus a Ogun

Published: 5th, March 2025 GMT

Aƙalla fasinjoji 16 suka ƙone ƙurmus, yayin da wasu uku suka jikkata a wani hatsarin mota da ya afku ranar Talata a Jihar Ogun.

Aminiya ta ruwaito cewa hadarin wanda ya rutsa da mota ɗaya kacal ya afku ne a gidan Buhari da ke kan titin Abeokuta zuwa Shagamu.

DAGA LARABA: Yadda Zawarawa Suke Ɗanɗana Kuɗa A Watan Ramadana ‘A ɗakin otel muka tsinci gawar tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Fice’

An bayyana cewa, hatsarin dai ya rutsa da wata farar motar bas kirar Mazda mai lamba KJA 949 YJ, da misalin ƙarfe 1:00 na rana.

Kakakin Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC), Florence Okpe, ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ta fitar.

Ta ce ba za a iya tantance jinsin waɗanda abin ya shafa ba saboda “sun ƙone ƙurmus ta yadda ba a iya fahimtar halittar jikinsu ba.”

Okpe ta ɗora alhakin faruwar hatsarin a kan gobarar da ta tashi a cikin motar, tana mai cewa bas ɗin tana ɗauke da fasinjoji 21 da kuma wata tukunyar gas wadda ta yi bindiga a cikin motar.

“Hatsarin ya rutsa ne da mutane 21. Ba a iya tantance waɗanda abin ya shafa ba saboda sun ƙone ba a iya gane su ba.

“Mutane 16 ne suka mutu a hatsarin, yayin da uku suka samu raunuka daban-daban, sai kuma wasu biyu suka tsallake rijiya da baya.

“Abinda ake zargin ya haddasa hadarin shi ne gobarar da ta tashi a cikin motar, wadda kuma tana ɗauke da wata tukunyar gas, wanda ya kai ga fashewar,” in ji ta.

Okpe ta ce an kai waɗanda suka jikkata zuwa Cibiyar Lafiya ta Tarayya da ke Idi Aba a birnin Abeokuta.

Kwamandan Hukumar FRSC na yankin, Akinwumi Fasakin, yayin da yake jajantawa iyalan mamatan, ya yi gargaɗin cewa, ya kamata a riƙa safarar kayan da ka iya jawo tashin wuta cikin kulawa da kuma motocin da aka keɓe waɗanda ƙwararru direbobi ke tuƙawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hatsari Jihar Ogun

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa

Gwamnan Jihar ta Gwambe, ya tunatar da cewa; a lokacin da Bola Ahmed Tinubu ya tsaya a gabanmu a matsayin ɗan takara a yaƙin zaɓen 2023, ya yi wa Arewacin Nijeriya alƙawura na musamman. Kazalika, Arewa ta amince da manufofin shugaban ƙasar, ta kuma yi tsayin daka wajen zaɓensa, inda suka bayar da gudunmawa na kimanin kashi 60 cikin 100 na ƙuri’un da Tinubun ya samu.

“A yau, ga shi mun taru, domin yin nazari a kan waɗancan alƙawuran tare kuma da tantance irin ci gaban da aka samu ya zuwa yanzu, abubuwan da muka samu su ne; sauye-sauyen da aka samu duk kuwa da irin ƙalubalen da ake fuskanta a wannan ƙasa. Wannan na nuna cewa, demokuraɗiyyarmu za ta iya yin aiki ne kaɗai idan ana cika alƙawuran da aka ɗauka, sannan shugabanni ba za su iya aiwatar da alƙawuran ba har sai sun samu haɗin kan ƴan ƙasa.  

“Zan iya bugun ƙirji wajen bayyana irin ci gaban da yankinmu na Arewa ya samu. ɗon haka, muna yi wa shugaban ƙasa godiya dangane da waɗannan sabbin tsare-tsaren ci gaba da ya kawo mana, mafi yawan ayyukan day a gada daga gwamnatin da ta gabata, yanzu haka yana kan hanyar kammala su.” 

Ya bayyana ire-iren waɗannan ayyuka da suka haɗa da aikin babbar hanyar Abuja zuwa Kano, layin jirgin ƙasa na Kano zuwa Katsina zuwa Maraɗi, gyaran matatar mai ta Kaduna, aikin bututun iskar gas na Abuja, Kaduna, Kano da kuma ci gaba da aikin haƙar mai a Kolmani.

“Waɗannan ayyuka, ko shakka babu; za su kawo ci gaba a ɓangaren masana’antu da samar da tsaro a yankunanmu na Arewa,” in ji shi. 

Gwamna Yahaya ya ƙara da cewa, akwai kuma wasu sabbin ayyukan more rayuwar da ken an tafe, waɗanda suka haɗa da hanyoyi daban-daban a tsakanin jihohi kamar babbar hanyar Sakkwato zuwa Badagiri, wadda za ta haɗa ƴan kasuwar Arewa da na Kudu da kuma shirin samar da harkokin nomad a zai shafi Arewa.

Bugu da ƙari, ya lissafo wasu da suka haɗa da faɗaɗawa tare da inganta cibiyoyin harkokin kiwon lafiya, wanda y ace; dukkanninsu suna nuni ga manufar da aka tsara, don inganta rayuwar al’ummar wannan yanki na Arewa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗaliban da aka sace a Binuwai sun kuɓuta 
  • Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa
  • Mun ci ribar Naira biliyan 414 a cikin wata 6 a Najeriya – Kamfanin MTN
  • Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a Jigawa
  • Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu
  • Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno
  • Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang