Aƙalla fasinjoji 16 suka ƙone ƙurmus, yayin da wasu uku suka jikkata a wani hatsarin mota da ya afku ranar Talata a Jihar Ogun.
Aminiya ta ruwaito cewa hadarin wanda ya rutsa da mota ɗaya kacal ya afku ne a gidan Buhari da ke kan titin Abeokuta zuwa Shagamu.
DAGA LARABA: Yadda Zawarawa Suke Ɗanɗana Kuɗa A Watan Ramadana ‘A ɗakin otel muka tsinci gawar tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Fice’An bayyana cewa, hatsarin dai ya rutsa da wata farar motar bas kirar Mazda mai lamba KJA 949 YJ, da misalin ƙarfe 1:00 na rana.
Kakakin Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC), Florence Okpe, ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ta fitar.
Ta ce ba za a iya tantance jinsin waɗanda abin ya shafa ba saboda “sun ƙone ƙurmus ta yadda ba a iya fahimtar halittar jikinsu ba.”
Okpe ta ɗora alhakin faruwar hatsarin a kan gobarar da ta tashi a cikin motar, tana mai cewa bas ɗin tana ɗauke da fasinjoji 21 da kuma wata tukunyar gas wadda ta yi bindiga a cikin motar.
“Hatsarin ya rutsa ne da mutane 21. Ba a iya tantance waɗanda abin ya shafa ba saboda sun ƙone ba a iya gane su ba.
“Mutane 16 ne suka mutu a hatsarin, yayin da uku suka samu raunuka daban-daban, sai kuma wasu biyu suka tsallake rijiya da baya.
“Abinda ake zargin ya haddasa hadarin shi ne gobarar da ta tashi a cikin motar, wadda kuma tana ɗauke da wata tukunyar gas, wanda ya kai ga fashewar,” in ji ta.
Okpe ta ce an kai waɗanda suka jikkata zuwa Cibiyar Lafiya ta Tarayya da ke Idi Aba a birnin Abeokuta.
Kwamandan Hukumar FRSC na yankin, Akinwumi Fasakin, yayin da yake jajantawa iyalan mamatan, ya yi gargaɗin cewa, ya kamata a riƙa safarar kayan da ka iya jawo tashin wuta cikin kulawa da kuma motocin da aka keɓe waɗanda ƙwararru direbobi ke tuƙawa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hatsari Jihar Ogun
এছাড়াও পড়ুন:
Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025
Hukumar Jin Daɗin Alhazai a Jihar Kebbi ta bayyana cewa ta kammala dukkan shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin bana a Ƙasa Mai Tsarki.
Amirul Hajji na jihar na shekarar 2025 kuma Sarkin Argungu, Alhaji Samaila Muhammad Mera, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a lokacin taron farko da aka gudanar a hedkwatar hukumar da ke Birnin Kebbi.
Ya kuma yi alkawarin tabbatar da jin daɗin mahajjatan jihar yayin da suke a ƙasa mai tsarki.
Amirul Hajjin ya bayyana cewa jimillar mahajjata 3,800 daga jihar ne suka biya kuɗin kujerunsu gaba ɗaya domin aikin hajjin bana, kuma jigilar mahajjatan za ta fara ne ranar 9 ga watan Mayu, inda ya ce da yardar Allah za a ci gaba da jigilar ba tare wani tsaiko ba har sai an kammala.
Ya kuma bayyana cewa, a wannan shekarar, za a yi wa mahajjata canjin kuɗin guzirinsu na BTA zuwa kudin Saudiyya wato riyal kai tsaye, da nufin dakile ayyukan damfara da kuma kare mahajjata daga asarar kuɗi yayin musayar kuɗaɗe a nan gida da kuma Saudiyya.
Alhaji Muhammadu Mera ya shawarci mambobin tawagar gwamnati da jami’an hukumar jin daɗin mahajjata da su gudanar da ayyukansu bisa tsoron Allah, tare da kare haƙƙoƙin mahajjata, daidai da manufar Gwamna Nasir Idris na gudanar da sahihin aikin Hajji mafi kyau.
Shugaban Hukumar, Alhaji Faruk Musa Yaro, ya yi alkawarin bayar da cikakken haɗin kakaga tawagar gwamnati domin tabbatar da nasarar aikin Hajji da ba a taɓa irin sa ba a tarihin jihar.
Ya ce an riga an samu masauki da sauran abubuwan buƙata ciki har da sufuri da abinci a ƙasa mai tsarki, sannan kuma kamfanin jirgin samsada ya yi jigilar Alhazan jihar a shekarar da ta gabata, wato Flynas, a bana ma shi ne zau yi jigilar mahajjatan zuwa kasa mai tsarki.
Haka kuma, an an fara yi wa Amirul Hajj da sauran mambobin tawagar gwamnati allurar rigakafi yayin kaddamar da shirin rigakafin mahajjatan.
Daga Abdullahi Tukur