Aminiya:
2025-09-18@01:16:47 GMT

Mai barkwanci ya yi kuskuren liƙe bakinsa da sufa-gilu

Published: 5th, March 2025 GMT

Wasa ya koma kuka bayan da wani mai wasan barkwanci manne laɓɓansa ba sa buɗewa bayan da ya shafa musu gam din sufa-gilu a yayin da yake yin bidiyo kai-tsaye domin ƙayatar da masu bibiyarsa.

Mutumin ya shafa gilu ne, inda ya manne laɓɓansa, wanda cikin dakika kaɗan, mannewar ta kama fatar laɓɓan kamar yadda ya so, inda hakan ya sa yabar laɓɓansa a rufe sosai.

Fasinjoji 16 sun ƙone ƙurmus a Ogun DAGA LARABA: Yadda Zawarawa Suke Ɗanɗana Kuɗa A Watan Ramadana

A zamanin da ake amfani da shafukan sada zumunta na zamani, mutane sukan yi iyakacin ƙoƙarinsu don samun mabiya da sakonsu zai kai gare su a intanet.

Raye-rayen zuwa abubuwan barkwanci, suna yin tasiri a shafukan sada zumunci na zamani.

Kwanan nan, wani bidiyo na wani mutum ɗan kasar Philippines ya ɗauki hankalin jama’a a intanet.

A cikin bidiyon, mutumin ya shafa sufa-gilu a laɓɓansa a matsayin wani ɓangaren na wasan barkwanci, amma lamarin ya sauya zuwa wani abun daban.

Bidiyon da tashar Talabijin ta Badis TV ta yada a shafin Insitagaram ya nuna wani mutumi zaune a cikin shago, rike da robar sufagilu kuma cikin wasa yana nuna kansa a kyamara.

Yana shafa shi, yana mannewa a lebbansa, amma cikin dakika kadan, mannewa ta kama fatun laɓɓansa yadda yake so, hakan dole ya sa ya bar laɓɓan a rufe sosai.

Da farko, mutumin ya bayyana yin hakan a matsayin nishadantarwa, yana dariya kamar ya yi nasara. Sai dai dariyarsa ta koma kuka, inda ya yi ta ƙoƙarin buɗe baki.

Nishadantarwarsa ta rikide zuwa firgici lokacin da ya gane laɓɓansa ba za su rabu ba, duk ya yi kokarin yin hakan.

Bayan wani lokaci sai hawaye hawaye suka fara gangarowa a fuskarsa yayin da yanayin ya yi tsanani, wanda hakan ya sa shi cikin damuwa.

Bidiyon ya sami ra’ayoyi sama da miliyan 6.7 na mabiya shafin kuma ya haifar da martani da yawa daga masu amfani da kafofin sada zumunta na zamani.

Da yake mayar da martani ga bidiyon, wani mabiyin shafin ya yi dariya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Barkwanci

এছাড়াও পড়ুন:

Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo

Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar SDP a zaben 2023, Adewole Adebayo, ya ce Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ba shi da burin da ya wuce na tara haraji tun yana Gwamna a Legas.

Adebayo ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels.

Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya

A cewarsa, “Kowa ya san cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu sananne ne wajen karbar haraji. Amma wannan tsarin karbar haraji ya fi tsarin da ya tarar da shi wanda ba shi da tsari.

“Ya yi hakan a Legas, sannan ya zo Abuja domin ya dora daga inda ya tsaya a Legas.”

Sai dai Adebayo ya ce Tinubu ya yi kokari wajen bunkasa tattalin arzikin Najeriya.

“A bayyane yake cewa tattalin arzikin da Shugaba Buhari ya bari ba a tafiyar da shi yadda ya kamata ba, kuma yana cikin mawuyacin yanayi kamar na mara lafiya da aka kai dakin jinya. Kamar yadda likita ke bukatar yin cikakken bincike domin gano matsalar mara lafiyan, haka ma ake bukatar fahimtar matsalar tattalin arziki kafin a fara warkar da ita.

“Abin da Shugaba Tinubu ya yi shi ne ya daidaita marar lafiyan, amma ban tabbatar ko ya kai ga gano matsalar ba. Don haka mara lafiyar ba zai mutu nan da nan ba, amma kuma ba a samo maganin cutar shi ba.

“Ba a gano ciwon da ke damun mara lafiyan ba, amma a matsayinsa na likita, yana daukar wasu matakai. Wasu daga cikin matakan ma sun kara ciwon mara lafiyar, amma sannu a hankali likitan yana samun nasara a wasu bangarorin, wanda hakan ke sa wasu su yi tunanin cewa mara lafiyan na kan hanyar warkewa,” in ji Adebayo.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja