Mai barkwanci ya yi kuskuren liƙe bakinsa da sufa-gilu
Published: 5th, March 2025 GMT
Wasa ya koma kuka bayan da wani mai wasan barkwanci manne laɓɓansa ba sa buɗewa bayan da ya shafa musu gam din sufa-gilu a yayin da yake yin bidiyo kai-tsaye domin ƙayatar da masu bibiyarsa.
Mutumin ya shafa gilu ne, inda ya manne laɓɓansa, wanda cikin dakika kaɗan, mannewar ta kama fatar laɓɓan kamar yadda ya so, inda hakan ya sa yabar laɓɓansa a rufe sosai.
A zamanin da ake amfani da shafukan sada zumunta na zamani, mutane sukan yi iyakacin ƙoƙarinsu don samun mabiya da sakonsu zai kai gare su a intanet.
Raye-rayen zuwa abubuwan barkwanci, suna yin tasiri a shafukan sada zumunci na zamani.
Kwanan nan, wani bidiyo na wani mutum ɗan kasar Philippines ya ɗauki hankalin jama’a a intanet.
A cikin bidiyon, mutumin ya shafa sufa-gilu a laɓɓansa a matsayin wani ɓangaren na wasan barkwanci, amma lamarin ya sauya zuwa wani abun daban.
Bidiyon da tashar Talabijin ta Badis TV ta yada a shafin Insitagaram ya nuna wani mutumi zaune a cikin shago, rike da robar sufagilu kuma cikin wasa yana nuna kansa a kyamara.
Yana shafa shi, yana mannewa a lebbansa, amma cikin dakika kadan, mannewa ta kama fatun laɓɓansa yadda yake so, hakan dole ya sa ya bar laɓɓan a rufe sosai.
Da farko, mutumin ya bayyana yin hakan a matsayin nishadantarwa, yana dariya kamar ya yi nasara. Sai dai dariyarsa ta koma kuka, inda ya yi ta ƙoƙarin buɗe baki.
Nishadantarwarsa ta rikide zuwa firgici lokacin da ya gane laɓɓansa ba za su rabu ba, duk ya yi kokarin yin hakan.
Bayan wani lokaci sai hawaye hawaye suka fara gangarowa a fuskarsa yayin da yanayin ya yi tsanani, wanda hakan ya sa shi cikin damuwa.
Bidiyon ya sami ra’ayoyi sama da miliyan 6.7 na mabiya shafin kuma ya haifar da martani da yawa daga masu amfani da kafofin sada zumunta na zamani.
Da yake mayar da martani ga bidiyon, wani mabiyin shafin ya yi dariya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Barkwanci
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
Gwamnatin Jihar Kano ta musanta zargin da wasu ke yi cewa ta karɓo sabon bashi na dala miliyan 6.6 daga watan Yuni zuwa Disamba 2023, tana mai cewa wannan zargi ƙarya ne marar tushe da aka ƙirƙira domin ɓata mata suna. Wannan na zuwa ne bayan wata ƙungiyar siyasa mai suna APC Patriotic Volunteers ta yi zargin cewa gwamnatin NNPP mai ci a jihar ta karɓo bashi daga ƙasashen waje ba tare da bayyana hakan ba.
Darakta Janar na Ofishin Gudanar da Basussuka a jihar, Dr. Hamisu Sadi Ali, ya bayyana cewa tun daga lokacin da gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta hau mulki, ba ta karɓi wani sabon bashi ko na gida ko na waje ba, balle a ɓoye shi daga idon jama’a. Ya ce duk wani bashi da gwamnatin jihar ke aiki da shi a halin yanzu an gada ne daga gwamnatin da ta gabata.
Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa Sarki Sanusi II Ya Yi Hawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda Na Haramta Hawan Sallah A KanoDr. Ali ya kuma ƙalubalanci tsohon Sakataren Gwamnatin Jiha, Alhaji Usman Alhaji, wanda ya jagoranci ƙungiyar da ta yi zargin, yana mai cewa duk wanda ke da hujjar wannan zargi ya fito da takardun da ke tabbatar da hakan – ciki har da sunan mai bayar da bashin, kwafen yarjejeniyar, dalilin karɓa, da tsarin biyan bashin.
A cewarsa, akwai doka mai ƙarfi da ke kula da basussuka a jihar, wadda gwamnatin APC ta gabata ta kafa a 2021. Wannan doka ta bai wa ofishinsa ikon karɓar bashi cikin tsarin doka da cikakken sahihanci, kuma ba wani bashi da aka karɓa tun bayan 2023. Ya ce gwamnati na gudanar da harkokinta cikin gaskiya da rikon amana, kuma ba za ta lamunci ƙarya da siyasar ɓatanci ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp