Mai barkwanci ya yi kuskuren liƙe bakinsa da sufa-gilu
Published: 5th, March 2025 GMT
Wasa ya koma kuka bayan da wani mai wasan barkwanci manne laɓɓansa ba sa buɗewa bayan da ya shafa musu gam din sufa-gilu a yayin da yake yin bidiyo kai-tsaye domin ƙayatar da masu bibiyarsa.
Mutumin ya shafa gilu ne, inda ya manne laɓɓansa, wanda cikin dakika kaɗan, mannewar ta kama fatar laɓɓan kamar yadda ya so, inda hakan ya sa yabar laɓɓansa a rufe sosai.
A zamanin da ake amfani da shafukan sada zumunta na zamani, mutane sukan yi iyakacin ƙoƙarinsu don samun mabiya da sakonsu zai kai gare su a intanet.
Raye-rayen zuwa abubuwan barkwanci, suna yin tasiri a shafukan sada zumunci na zamani.
Kwanan nan, wani bidiyo na wani mutum ɗan kasar Philippines ya ɗauki hankalin jama’a a intanet.
A cikin bidiyon, mutumin ya shafa sufa-gilu a laɓɓansa a matsayin wani ɓangaren na wasan barkwanci, amma lamarin ya sauya zuwa wani abun daban.
Bidiyon da tashar Talabijin ta Badis TV ta yada a shafin Insitagaram ya nuna wani mutumi zaune a cikin shago, rike da robar sufagilu kuma cikin wasa yana nuna kansa a kyamara.
Yana shafa shi, yana mannewa a lebbansa, amma cikin dakika kadan, mannewa ta kama fatun laɓɓansa yadda yake so, hakan dole ya sa ya bar laɓɓan a rufe sosai.
Da farko, mutumin ya bayyana yin hakan a matsayin nishadantarwa, yana dariya kamar ya yi nasara. Sai dai dariyarsa ta koma kuka, inda ya yi ta ƙoƙarin buɗe baki.
Nishadantarwarsa ta rikide zuwa firgici lokacin da ya gane laɓɓansa ba za su rabu ba, duk ya yi kokarin yin hakan.
Bayan wani lokaci sai hawaye hawaye suka fara gangarowa a fuskarsa yayin da yanayin ya yi tsanani, wanda hakan ya sa shi cikin damuwa.
Bidiyon ya sami ra’ayoyi sama da miliyan 6.7 na mabiya shafin kuma ya haifar da martani da yawa daga masu amfani da kafofin sada zumunta na zamani.
Da yake mayar da martani ga bidiyon, wani mabiyin shafin ya yi dariya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Barkwanci
এছাড়াও পড়ুন:
Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Yi Watsi Da Duk Wani Zarge-Zargen Neman Bata Mata Suna
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta musanta zarge-zargen da Amurka da kasashen yamma suka yi mata
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Ismail Baqa’i ya musanta zarge-zargen da Amurka da Faransa da wasu kasashen yammacin Turai ke yi wa Iran a matsayin abin dariya da rashin tushe. Ya kuma jaddada cewa, suna daga cikin fito-na-fito na hasashe da kuma kokarin karkatar da ra’ayin jama’a daga muhimman batutuwan da ke faruwa a yanzu, wato kisan kiyashi da kashe-kashen jama’a da ake yi a kasar Falasdinu.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ya jaddada a cikin wata sanarwa da aka fitar a yau Juma’a cewa: Amurka, Faransa da dukkan sauran kasashen da suka sanya hannu kan sanarwar baya-bayan nan kan Iran, a matsayin gwamnatin da ke goyon bayan kungiyoyin ‘yan ta’adda da kuma karfafa tashin hankali, wajibi ne su dauki nauyin wadannan matakai da suka saba wa dokokin kasa da kasa.
Baqa’i ya yi tsokaci kan hare-haren wuce gona da iri da Amurka da yahudawan sahayoniyya suka yi wa Iran a baya-bayan nan, da kuma laifukan kisan kare dangi da ake ci gaba da yi a Gaza. Ya kuma jaddada cewa ana yin hakan ne tare da goyon baya ko amincewar wadanda suka rattaba hannu kan wannan bayani na adawa da Jamhuriyar Musulunci.
Iran
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Limamin Sallar Juma’a Ya Ce; Iran Zata Mayar Da Isra’ila Kufai Idan Ta Sake Kai Hari Kan Kasarta August 1, 2025 Kasar Slovenia Da Haramta Tura Makamai Zuwa Haramtacciyar Kasar Isra’ila August 1, 2025 Kasar Spain Ta Bayyana Abin Da Ke Faruwa A Gaza A Matsayin Abin Kunya Ga Bil’Adama August 1, 2025 Iran ta yi watsi da zargin gwamnatocin turai na yunkurin kashe wasu mutane a kasashensu August 1, 2025 Mali da Rasha sun tattauna kan hadin gwiwar makamashi August 1, 2025 Afirka ta Kudu na shirin daukar matakan kauce wa tasirin harajin Amurka August 1, 2025 Haaretz: Sojojin Isra’ila 7 ne suka kashe kansu a watan Yuli August 1, 2025 Gaza: Mutane Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Wasu Kuma Sun Jikkata August 1, 2025 Kungiyar AU Ta Yi Watsi Da Kafa Gwamnatin Adawa Da Kungiyar RSF Ta Yi A Sudan August 1, 2025 Shugaban Kasar Iran Zai Ziyarci Pakistan A Gobe Asabar August 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci