Rundunar ’yan sandan Nijeriya ta sanar da cewa a ɗakin wani otel ta gano gawar wani tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Ficen Nijeriya, David Shikfu Parradang.

A baya dai an ruwaito cewa wasu masu garkuwa da mutane ne suka kashe Mista Parradang bayan sun karɓe kuɗin da ya ciro a banki a yankin Area 1 da ke babban birnin ƙasar.

Masu garkuwa sun kashe tsohon Kwanturola-Janar na Hukumar Shige da Fice a Abuja Tinubu ya naɗa Babatunde Ogunjimi Akanta Janar na Tarayya

Sai dai wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Abuja, Josephine Adeh ta fitar a yammacin wannan Talatar, ta ce tsohon babban jami’in Hukumar Shige da Ficen ya mutu ne a ɗakin wani otel saɓanin rahoton da ke cewa masu garkuwa da mutane ne suka kashe shi.

Adeh ta ce rasuwar Mista Parradang na zuwa ne bayan ya yi wata baƙuwa mace da ta kai masa ziyara ɗakin otel ɗin ya kama na kwana guda.

“Bisa rahotanni da ke cewa an yi garkuwa da tsohon jami’in Hukumar Shige da Ficen sannan daga bisani aka kashe, muna so mu tabbatar da gaskiyar lamarin.

“Abin da ya faru shi ne da misalin ƙarfe 12 na ranar 3 ga watan Maris, Mista Parradang ya ziyarci Otel ɗin Joy House da ke yankin Area 3 na Abuja a wata baƙar mota ƙirar marsandi.

“Ya biya Naira 22,000 kuɗin kwana ɗaya. Sai dai bayan wani ɗan lokaci ya buƙaci ɗaya daga cikin masu aiki a otel ɗin cewa ya yi baƙuwa yana so a rako ta ɗakin nasa.

“Matar da ta kai masa ziyara ta bar otel ɗin da misalin ƙarfe 4 na yammacin wannan rana.

“Har bayan tafiyar wannan mata Mista Parradang bai fito daga ɗakin ba, sai washegari da misalin ƙarfe 4 na asubahi wani abokinsa mai aikin ɗamara ya biyo sawu yana cigiyarsa har otel ɗin.

“Yana zuwa kuwa aka garzaya da shi [abokin nasa] har ɗakin, inda aka tarar da gawarsa zaune a kan kujera.

“Nan da nan aka sanar da ofishin ’yan sanda na Durumi kuma suka zo suka ɗauki hotuna da sauraren ababen da su taimaka musu wajen gudanar da bincike.”

Sanarwar ta ƙara da cewa, a halin yanzu an miƙa gawar Mista Parradang zuwa Asibitin Ƙasa da ke Abuja domin ɗauka matakan da suka dace “yayin da ma’aikatan otel ɗin ke ci gaba da bai wa ’yan sanda haɗin kai a binciken da suka gudanarwa.”

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: David Shikfu Parradang Hukumar Shige da Fice Hukumar Shige da Ficen Mista Parradang

এছাড়াও পড়ুন:

Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara

Ɗan takarar jam’iyyar Labour a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, Peter Obi, ya ziyarci tsohon shugaban ƙasa, Olusegun Obasanjo, da kuma sabon Olubadan na Ibadan, Rashidi Ladoja, a wani zagayen ganawa da manyan ’yan siyasa gabanin zaɓen 2027.

Obi, wanda ke ƙoƙarin ƙara yauƙaƙa zumunci da manyan shugabanni a fadin ƙasar, ya bayyana cewa ziyarar na da alaƙa da burinsa na ganin an samu shugabanci na gaskiya da riƙon amana a Najeriya.

An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Obi ya bayyana cewa ziyararsa ta musamman zuwa Ibadan na da nufin girmama Rashidi Ladoja, wanda aka naɗa a matsayin Olubadan, da kuma jaddada muhimmancin Ibadan a siyasa, zamantakewa, da tattalin arzikin ƙasar.

“Na kai ziyara don girmama sabon Olubadan, Rashidi Ladoja, wanda ƙwarewarsa a matsayin tsohon sanata, gwamna, kuma attajiri za ta taimaka wajen ɗaga martabar Ibadan,” in ji Obi.

Ya ƙara da cewa tattaunawarsa da Obasanjo da Ladoja na da nasaba da ci gaban Najeriya da kuma shugabanci da ke da burin sauya al’umma ta fuskar gaskiya da adalci.

Ziyarar Obi na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da shirye-shiryen siyasa gabanin babban zaɓen shekarar 2027, inda ake hasashen zai sake tsayawa takarar shugaban ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar