Falasdinawa 40 Ne suka Yi Shahada A Zirin Gaza Sakamakon Ta’addancin Sojojin Mamayar Isra’ila A Jiya Juma’a
Published: 3rd, May 2025 GMT
Falasdinawa 40 ne suka yi shahada a hare-haren da sojojin mamayar Isra’ila suka kai kan Zirin Gaza tun daga wayewar garin jiya Juma’a
Rahotonni sun bayyana cewa: A yammacin jiya Juma’a, Falasdinawa fararen hula 8 ne suka yi shahada yayin da wasu kuma suka jikkata sakamakon wani hare-haren da jiragen saman sojin mamayar Isra’ila suka kai kan wani gida a sansanin Jabaliya da al-Balad da ke arewacin zirin Gaza.
Haka zalika hare-haren sun yi sanadiyyar shahadar Falasdinawa 6 sannan wasu 8 suka jikkata a wani harin da jiragen saman yakin mamayar Isra’ila suka kai kan taron fararen hula da ke kusa da mahadar Abd al-Aal da ke kan titin al-Jala’a da ke arewacin birnin Gaza.
A cewar majiyoyin cikin gida, jiragen saman yakin mamayar Isra’ila sun kai hari kan wani asibiti da ke titin al-Jala’a, inda suka janyo shahadan Mahmoud Abdullah al-Muqayyad, Ahmed Qaza’ar, Tamer Hamdan, Samer al-Nuwairi, Hatem al-Sa’ati, da Rizq al-Madhoun.
A kudancin zirin Gaza kuwa, Falasdinawa uku ne suka yi shahada, kuma wasu suka jikkata, lokacin da wani jirgin saman yakin mamayar Isra’ila ya kai hari kan wata tanti da ke dauke da ‘yan gudun hijira a yankin Mawasi na Khan Yunis.
Sojojin mamayar Isra’ila na ci gaba da kai hare-hare a zirin Gaza a rana ta 46 a jere, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar daruruwan mutane, da jikkatan wasu na daban
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: mamayar Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’ilBagaei ya yi tir da samar da duk wata hulda da HKI sannan tana ganin yin haka yana dai-dai da taimaka mata ko halatta mata ayyukan ta’addancin da take aikatawa a Gaza.
Kamfanin dillancin labaran Tasnem na kasar Iran ya nakalto Bagaei yana fadar haka a yau Laraba, a taron mako-mako da ya saba a ma’aikatsa a nan Tehran. Ya kuma kara da cewa, Iran tana kira ga dukkan kasashen duniya musamman kasashen yankingabas ta tsakiya da su kauracewa Haramtacciyar kasar Isra’ila (HKI) ko ta ina.
Ya ce kasashen musulmi da dama, har ma da wasu wadandaba musulmi ba sun dade da katse dangantakarsu da haramtacciyar kasar, babu dangantakar diblomasiyya babu na kasuwanci da ita. Don haka wadanda suka rage su yi da gaggawa.
Jami’in diblomasiyyar ya yabawa kungiyoyi daban-daban a kasashen turai wadanda suke kamfen na kauracewa HKI da kuma yanke hulda da ita ko ta ina, da kuma dakatar da sayar mata makamai wadanda take kashe falasdinawa da su.
Don haka ,inji Bagaei, idan kasashen musulmi suka shiga cikin gayyar wadan dannan kasashe da suka kauracewa HKI, suka kuma aiwatar da kauracewar a kasa, to kuwa zamu ga nasar babba nan gaba da yardar All…
Daruruwan Falasdinawa ne suka yi shahada a birnin Gaza babban birnin yankin saboda hare-hare babu kakkautawa da take kaiwa kan mutanen birnin Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza September 17, 2025 Iran da Saudiyya sun bukaci hadin kan Musulmi game da halin da ake a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci