Falasdinawa 40 Ne suka Yi Shahada A Zirin Gaza Sakamakon Ta’addancin Sojojin Mamayar Isra’ila A Jiya Juma’a
Published: 3rd, May 2025 GMT
Falasdinawa 40 ne suka yi shahada a hare-haren da sojojin mamayar Isra’ila suka kai kan Zirin Gaza tun daga wayewar garin jiya Juma’a
Rahotonni sun bayyana cewa: A yammacin jiya Juma’a, Falasdinawa fararen hula 8 ne suka yi shahada yayin da wasu kuma suka jikkata sakamakon wani hare-haren da jiragen saman sojin mamayar Isra’ila suka kai kan wani gida a sansanin Jabaliya da al-Balad da ke arewacin zirin Gaza.
Haka zalika hare-haren sun yi sanadiyyar shahadar Falasdinawa 6 sannan wasu 8 suka jikkata a wani harin da jiragen saman yakin mamayar Isra’ila suka kai kan taron fararen hula da ke kusa da mahadar Abd al-Aal da ke kan titin al-Jala’a da ke arewacin birnin Gaza.
A cewar majiyoyin cikin gida, jiragen saman yakin mamayar Isra’ila sun kai hari kan wani asibiti da ke titin al-Jala’a, inda suka janyo shahadan Mahmoud Abdullah al-Muqayyad, Ahmed Qaza’ar, Tamer Hamdan, Samer al-Nuwairi, Hatem al-Sa’ati, da Rizq al-Madhoun.
A kudancin zirin Gaza kuwa, Falasdinawa uku ne suka yi shahada, kuma wasu suka jikkata, lokacin da wani jirgin saman yakin mamayar Isra’ila ya kai hari kan wata tanti da ke dauke da ‘yan gudun hijira a yankin Mawasi na Khan Yunis.
Sojojin mamayar Isra’ila na ci gaba da kai hare-hare a zirin Gaza a rana ta 46 a jere, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar daruruwan mutane, da jikkatan wasu na daban
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: mamayar Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Sojojin Isra’ila Sun Kashe Kananan Yara Masu Yawa A Iran
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Yahudawan sahayoniyya sun kashe adadi mai yawa na yaran Iran a cikin ta’addancin da suke yi
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Ismail Baqa’i ya bayyana cewa: Gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta kashe kananan yara masu yawa na Iran a cikin wannan ta’asa da take gudanarwa kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
A cikin wani sako da Ismail Baqa’i ya rubuta a ranar Lahadin da ta gabata ya bayyana cewa: “Gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta kashe adadi mai yawa na yara Iraniyawa tare da kai hari kan asibitin yara a tsawon kwanaki uku na hare-haren soji kan Iran. Kamar yadda Ya’ir Golan, tsohon mataimakin hafsan hafsoshin sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila ya amince da cewa: Kashe yara wani nau’i ne na nishaɗi a gare su.”