Aminiya:
2025-11-02@06:26:21 GMT

Muhimmancin ƙamshi a rayuwar mace

Published: 4th, March 2025 GMT

Ƙamshi abin so ne a wurin kowa. Mata su kasance suna saka turaren wuta a kullum. Su mayar da shi dole kamar yin wanke-wanke.

Ko kun san cewa, wannan turaren wutar za a iya amfani da shi da kabbasa domin turara zanin gado da rigar sawa?

An horas da masu unguwannin Katsina kan sasanta jama’a Ramadan: Gwamnatin Jigawa ta rage lokacin aiki

Bayan haka, akwai turaren humra wadda za a iya shafa shi a gashin kai.

Akwai na hammata daban sannan akwai na shafawa kamar mai, wanda aka fi sani da kulacca da kuma na riga.

Lallai duk macen da ta kasance cikin ƙamshi, za ta sami girmamamwa a cikin al’umma da kuma mai gidanta.

Kuma akwai turaren kanti kamar su ‘Dior’ da cool water da sauransu.

Yadda za ai amfani da turaren gargajiya

A sami kabbasa (za a iya saminsa a kasuwa) da kasko, a zuba garwashin wuta sannan a dora kabbasar a kai.

A kuma zuba turaren wuta a cikin garwashin sannan sai a rufe kabbasa da kayan da za a saka a ranar ko kuma wanda za a je unguwa da su, hayakin ya shiga kayan sosai.

Bayan haka, sai a shafa kulaccam (kamar man shafawa yake amma da turaruka aka hada shi).

Bayan an yi wanka sai a shafa a matsayin man shafawa. Sannan sai a saka riga a shafa humra fari ko baki a jikin kayan.

Idan kayan mai duhu ne sai a saka humra baƙa. Idan kuma kayan masu haske ne sai a saka farar humra.

Idan kuwa ana son amfani da turaren kanti, fesawa kawai ake yi.

Amma na gargajiya ya fi daɗewa a jiki don kuwa ko kaya sun yi datti da ƙyar a ji warin kayan don ƙamshin turaren.

Irin waɗannan turaruka na taimaka wa masu jego wajen rage ƙarnin nono a jikinsu da kuma jikin jariri.

Sai a ga wasu matan daga sun haihu, suna ƙarni, ɗan da suka haifa ma idan an ɗauka sai a ji cewa yana ƙarni.

Wani ƙarnin jinjirin ma har ya shafi wanda ya ɗauki jinjirin.

Don haka, sai a kula wajen amfani da turare domin magance waɗannan matsalolin.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Turare

এছাড়াও পড়ুন:

Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum

Rikicin jam’iyyar PDP ya ƙara tsananta bayan sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, ya sanar da dakatar da shugaban jam’iyyar na ƙasa, Ambasada Illiya Damagum.

Yayin da yake yi wa manema labarai jawabi a Abuja, Anyanwu, wanda yake ɗan tsagin  Nyesom Wike, ya ce an dakatar da Damagum da wasu manyan jami’an jam’iyyar guda biyar saboda zargin rashin ƙwarewa, almundahana, da ƙin bin hukuncin kotu.

Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike

“Mun yanke shawarar dakatar da shugaban jam’iyyar na ƙasa, Ambasada Ilya Damagum, saboda rashin ƙwarewa, almundahana, da ƙin mutunta hukuncin kotu,” in ji Anyanwu.

“An dakatar da shi na tsawon wata guda, kuma dole ne ya gurfana gaban kwamitin ladabtarwa.”

Anyanwu, ya kuma yaba da hukuncin kotu wanda ya soke babban taron jam’iyyar na ƙasa, inda ya bayyana cewa wannan nasara ce ga mambobin PDP baki ɗaya.

“Muna jinjina wa ɓangaren shari’a bisa wannan hukunci da ya nuna adawa da zalunci da rashin bin doka. Wannan nasara ce ga kowane ɗan jam’iyyar PDP,” in ji shi.

Sauran da aka dakatar sun haɗa da mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Debo Ologunagba; mataimakin shugaban jam’iyyar na Kudu, Taofeek Arapaja.

Akwai kuma sakataren kuɗi na ƙasa, Daniel Woyenguikoro; jagoran matasan jam’iyyar, Sulaiman Kadade da mataimakin sakataren jam’iyyar na ƙasa, Setonji Koshoedo.

Sanarwar Anyanwu, na zuwa ne bayan ɓangaren Damagum ya dakatar da shi da wasu magoya bayan Wike, lamarin da ya ƙara ba tsananta rikicin shugabanci a jam’iyyar PDP.

Anyanwu, ya kuma sanar da naɗa Alhaji Abdulrahman Mohammed, mataimakin shugaban jam’iyyar na yankin Arewa ta Tsakiya, a matsayin sabon muƙaddashin shugaban jam’iyyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum