Gidauniyar Sir Ahmadu Bello Ta Yi Kira Ga Hadin Kai Da Adalci A Ramadan
Published: 4th, March 2025 GMT
Yayin da al’ummar Musulmai a Najeriya da duniya ke fara azumin watan Ramadan, Gidauniyar Tunawa da Sir Ahmadu Bello ta aike da sakon fatan alheri, tana kira da a yi amfani da wannan lokaci mai daraja wajen sabunta zukata da nuna tausayi da karfafa hadin kai a kasa.
A cikin wata sanarwa da Daraktan Janar na gidauniyar, Abubakar Gambo Umar ya sanya wa hannu, ta jaddada bukatar kyautata dabi’u da wanzar da zaman lafiya da adalci a kasuwanci a lokacin azumi.
Gidauniyar ta yi kira ga malaman addini da su ci gaba da yada sakonnin tsoron Allah da hakuri da kaunar juna, domin karfafa darussan Ramadan na sabunta imani da hadin kan al’umma.
Hakazalika, gidauniyar ta gargadi ’yan kasuwa da dillalai da su guji tsawwala farashi da cutar da mabukata, tana mai cewa Ramadan lokaci ne na tausayi da taimakon juna, ba wahala da neman riba ta haram ba.
“Yayin da muke tsarkake kanmu ta hanyar azumi da ibada, mu kuma daga murya cikin addu’a don hadin kai, zaman lafiya, da ci gaban ƙasarmu ƙaunatacciya. Allah Ya baiwa shugabanninmu shiriya, Ya kuma ba ƙasarmu ƙarfin da za ta shawo kan ƙalubalen da take fuskanta. in ji sanarwar”.
Gidauniyar ta jaddada kudirinta na karfafa zaman lafiya da adalci da daidaito a cikin al’umma, tare da kira ga ’yan Najeriya da su rungumi kyawawan halaye na Ramadan—imani, hakuri da karamci.
A karshe, gidauniyar ta yi fatan Allah Ya albarkaci kowa da zaman lafiya da rahama a wannan wata mai alfarma.
Rel: Khadija Kubau
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Gidauniyar Kira Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
Ana ci ga ba da zaman dar-dar a kasar Burkina faso, bayan da shugaban kasa mai ci Ibrahim traure ya sake tsallaka rijiya da baya, a wani kokarin juyin mulki wanda bai sami nasara ba a makon da ya gabata.
Shafin yanar gizo na labarai ‘Africa News’ya nakalto radiyo Faransa RFI yana fadar cewa an bankado juyin mulkin ne bayan da dukkan bakin da aka gayyata a ranar 22 ga watan Afrilu zuwa wani taro sun kasa halattan taron. Wanda ya nuna shakku kan abinda aka kulla a cikin taron.
Labarin ya kara da cewa a cikin yan kwanaki masu zuwa mutanen kasar zasu fito zanga-zanga don nuna goyon bayansu ga shugaban Traore.
Har’ila yau ana gudanar da bincike a cikin barikokin sojojin kasar a birnin Wagadugu a kokarin gano wadanda suke adawa da gwamnatin Traore, sannan suke aiki wa kasashen yamma musamman kasar Faransa wajen ganin bayan shugaba Ibrahim Traore.
Kafin haka dai an nakalto ministan tsaron kasar ta Burkina faso Muhammada Sana ya na wani bayani a tashar talabijin na kasar, kan cewa kafin su gano shirin juyin mulki sun satar maganar wayar tarho tsakanin wani babban sojan kasar da shugaban wata kungiyar ta’addaci wanda aka shirya za su kashe shugaba Traore.