Kasashen duniya 22 sun bukaci Isra’ila da ta dawo da agaji gaba daya a Gaza
Published: 20th, May 2025 GMT
Kasashen duniya 22 sun bukaci Isra’ila da ta gaggauta dawo da cikakken tallafin da take baiwa zirin Gaza.
Tireloli tara na taimakon jin kai na Majalisar Dinkin Duniya ne aka ba su izinin shiga zirin Gaza a ranar Litinin, wanda ake wa kallo a matsayin digo ‘’ digo a cikin teku,” in ji shugaban kula da ayyukan jin kai na MDD, Tom Fletcher.
Al’ummar Zirin Gaza suna “fuskantar yunwa” kuma “dole ne su sami taimakon da suke bukata,” in ji ma’aikatun harkokin waje na kasashen Australia, Canada, Denmark, Estonia, Finland, Faransa, Jamus, Iceland, Ireland, Italiya, Japan, Latvia, Lithuania, Luxembourg, Netherlands, New Zealand, Norway, Portugal, Slovenia, Spain, Sweden, da United Kingdom.
Kasashen da suka rattaba hannu kan bukatar sun ce, “Bai kamata a rika siyasantar da taimakon jin kai ba.”
Isra’ila ta sake farmawa zirin Gaza ne a ranar 18 ga watan Maris, bayan karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta da ta cimma da kungiyar Hamas.
Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya fada a ranar Litinin cewa Isra’ila za ta “karbe ikon gabadayen” yankin zirin Gaza.
Ko a jiya Hukumar kare fararen hula a Gaza ta sanar cewa Isra’ila ta kashe mutane 91 a rana guda.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Wani Kamfanin Kera Kayankin Aikin Likita Ya Gabatar Da Sabon Na’urar Tiyata
Wani kamfanin kera kayakin aikin likita mai zaman kansa a nan Tehran ya gabatar da wata na’ura mai aikin tiyata wanda kuma aka dora masa kayan aiki na zamani.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa an gabatara da wannan na’urar a kasuwar baje kolin kayakin aikin likita karo na 26TH wanda ke gudana a nan birnin Tehran.
Labarin ya kara da cewa samar da kayalin aikin likita wadanda suke tafiya da zamani, ya zama dole ne bayanda aka haka sayarwa kasar Iran irinsu daga waje.
Wannan hanin ya sa a dole daga cikin gida kwararru suka fara samar da kayakin aikin likita na zamani, don wadatar da asbitocin kasar daga sayan na waje, har ma tana sayarwa kasashen waje.
Mostafa Abdulgaffar shugaban kamfanin da ya samar da wannan na’urar yace : Na’urar za ta taimakawa lokitoci da wasu ayyuka masu muhimmanci dangane da marasa lafiyan da sukewa aiki, ta yadda likitocin ba za su yi kuskure na bata wani wuri a cikin jikin marasa lafiya wanda sukewa aiki ba.
Abdulgaffar ya kara da cewa kafin haka kasar Iran tana shigo da irin wadannan kayakin aikin likita ne daga kasashen Amurka, da Jamus. Amma bayan an dorawa kasar takunkuman tattalin arziki, sun dukufa a cikin gida saida suka samar da su. Suka kuma sami lasicin aiki da su a cikin asbitocin kasar da kuma saida su ga kasashen waje.