HausaTv:
2025-07-26@03:46:02 GMT

Kasashen duniya 22 sun bukaci Isra’ila da ta dawo da agaji gaba daya a Gaza

Published: 20th, May 2025 GMT

Kasashen duniya 22 sun bukaci Isra’ila da ta gaggauta dawo da cikakken tallafin da take baiwa zirin Gaza.

Tireloli tara na taimakon jin kai na Majalisar Dinkin Duniya ne aka ba su izinin shiga zirin Gaza a ranar Litinin, wanda ake wa kallo a matsayin digo ‘’ digo a cikin teku,” in ji shugaban kula da ayyukan jin kai na MDD, Tom Fletcher.

Al’ummar Zirin Gaza suna “fuskantar yunwa” kuma “dole ne su sami taimakon da suke bukata,” in ji ma’aikatun harkokin waje na kasashen Australia, Canada, Denmark, Estonia, Finland, Faransa, Jamus, Iceland, Ireland, Italiya, Japan, Latvia, Lithuania, Luxembourg, Netherlands, New Zealand, Norway, Portugal, Slovenia, Spain, Sweden, da United Kingdom.

Kasashen da suka rattaba hannu kan bukatar sun ce, “Bai kamata a rika siyasantar da taimakon jin kai ba.”

Isra’ila ta sake farmawa zirin Gaza ne a ranar 18 ga watan Maris, bayan karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta da ta cimma da kungiyar Hamas.

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya fada a ranar Litinin cewa Isra’ila za ta “karbe ikon gabadayen” yankin zirin Gaza.

Ko a jiya Hukumar kare fararen hula a Gaza ta sanar cewa Isra’ila ta kashe mutane 91 a rana guda.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati

Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dokta Ali Haruna Makoda, ya buƙaci iyaye da su tabbatar da cewa ‘ya’yansu sun koma makaranta a kan lokaci.

Ya yi gargaɗin cewa duk ɗalibin da ya makara wajen dawowa makaranta zai iya fuskantar hukunci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Jaddada Wajabcin Daukan Matakin Kawo Karshen Dakatar Da Laifukan Kisan Kare Dangi A Gaza
  • Hukumar Ba Da Agajin Jin Kai Ta ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinawa Ta “UNRWA” Ta Sanar Da Kashe Ma’aikatan 330 A Gaza
  • Iran da Bangladesh sun bukaci taron gaggawa na OIC kan kisan kiyashi a Gaza
  • Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Fara Tattaunawa kan Masifar Zirin Gaza Na Falasdinu
  • Asusun Kula Da Kananan Yara Na Majalisar Dinkin Duniya “UNICEF” Ya Yi Gargadi Kan Bala’in Jin Kai A Gaza
  • Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
  • Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati
  • Yahudawan Sahayoniyya Sun Bullo Da Dabarar Kisa Kan Falasdinawa Musamman ‘Yan Gudun Hijira
  • Sheikh Qasem: Nuna Halin Ko In-Kula Na Duniya Ne Ya Jawo Kisan Kiyashi A Gaza
  • Jami’an Kasashen Rasha, China, Iran Sun Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa A Tehran