An kori ma’aikatan Microsoft saboda adawa da yahudawan sahyoniya
Published: 28th, February 2025 GMT
Kamfanin Microsoft ya kori ma’aikata biyar bayan da suka nuna rashin amincewa da kwangilar da kamfanin ya kulla da sojojin Isra’ila.
A rahoton cibiyar yada labarai ta Falasdinu, ma’aikatan sun gudanar da zanga-zangar ne a hedkwatar Microsoft da ke Redmond a birnin Washington, sanye da riguna masu dauke da taken nuna adawa da amfani da fasahar kamfanin wajen kai wa Falasdinawa hari.
Matakin ya zo ne bayan da aka buga wani rahoto da ke nuna cewa an yi amfani da bayanan sirri na wucin gadi da na’urar tantance gajimare na Microsoft wajen ayyukan sojojin Isra’ila.
Bayan wani bincike da Kamfanin Dillancin Labarai na Associated Press ya yi a baya-bayan nan, ya bayyana cewa kamfanonin fasahar kere-kere na Amurka sun taimaka wa Isra’ila wajen kara yawan laifuka da kashe-kashe a Gaza da Lebanon ta hanyar samar da kayayyakin leken asiri ga gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila.
Jaridar The Guardian ta Burtaniya ta bayar da wani rahoto da ke cewa, Microsoft ya karfafa alakarsa da sojojin Isra’ila tare da ba su tallafin fasaha a yakin Gaza.
Jaridar Guardian ta kara da cewa dogaron da sojojin Isra’ila suka yi kan fasahar Microsoft ya karu matuka a lokacin yakin Gaza, kuma sun yi amfani da hakan wajen aiwatar da kashe-kashe kan Falastinawan Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: sojojin Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Ireland Ta Yi Dokar Hana Shigar Da Kayan Da Aka Kera A ” Isra’ila” Cikinta
Gwamnatin kasar Ireland ta yi doka a jiya Talata wacce ta hana a shigar da duk wasu kaya da aka kera a matsugunan ‘yan share wuri zauna da a karkashin dokokin kasa da kasa ake daukarsu a matsayin haramtattu.
Mai Magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Ireland ya fada wa kamfanin dillancin labaurn Faransa cewa; Gwamnati ta amince da a ci gaba da yin wasu dokokin da hana mu’amalar kasuwanci da matsugunan ‘yan share wuri zauna da ba su bisa doka, domin an yi su ne akan kasar Falasdinawa.”
Daga cikin kayayyakin da Majalisar dokokin ta Ireland ta haramta, da akwai ‘ya’yan marmari da itatuwa.
Ministan harkokin wajen Ireland Simon Harris ya fada wa ‘yan jarida cewa, yana fatan ganin matakin da karamar kasarsu ta dauka a kan Isra’ilan ya yi wa sauran kasashen nahiyar turai tasiri su bi sahu.”
Gwamnatin ta Ireland ta sanar da cewa; ta dogara ne da hukuncin kotun duniya ta manyan laifuka wacce ta fitar a watan Yuni na 2024.
A gefe daya kasashe turai da su ka hada Ireland, Spain da Norway sun bayyana aniyarsu ta amincewa da gwamnatin Falasdinu. Ita ma kasar Slovania ta bi sahun wadannan kasashen na turai, yayin da kasar Faransa ta bakin shugabanta Emmanuel Macro ta bayyana cewa; tana Shirin yin furuci da Daular Falasdinu.