Leadership News Hausa:
2025-04-30@20:08:45 GMT

Maraba Da Watan Ramadan

Published: 28th, February 2025 GMT

Maraba Da Watan Ramadan

Har ila yau yana daga hukuncin shari’a, ba a fara azumi da kokwanto, misali ka kwanta bacci sai ka kudirce a ranka cewa in an bayyana ganin wata ina bacci, zan tashi da azumi. Mun gode Allah, yanzu sabida na’u’rar zamani da wuri ake sanar da ganin wata.

Lamarin ganin watan Ramadana abu ne mai sauki, sabida galibin Malamai da Shehunnanmu na kasa da waje baki daya suna kan Hadisin Kuraibu da yake cewa “Kowacce kasa da ganin watanta, misalin kasar: Nijer da Ghana, Mali, Togo da dai sauransu duk suna da Sarkin Musulmi kuma shi zai ayyana ganin watan.

Amma kuma, in Nijer suka ga watan Ramadana, Sarkin Musulmin Nijeriya in yaga dama zai iya cewa na ga wata da ganin watan Nijer sabida dare da lokutan kasashen duk iri daya ne. Sai dai ban da kasar da lokutansu ba iri daya ba ne – ra’ayin wasu malamai kenan.

Amma a wannan zamani na kimiyya da fasaha, Allah shi ne zamani. Annabi ya ce ba ma Hisabi, ba ma Rubutu (ba wai ya hana ba ne) Littafinsa ne ma ya yi nuni da a yi Karatu “Ikra’a” Allah kuma ya yabi masu Rubutu “Bi’aidi safarah, kiramin bararah” sabida muhimmancin karatu da rubutu, a ranar yakin Badar, Annabi (SAW) ya yanke wa duk fursunoni fansa amma ya ce duk wadanda suka iya karatu da rubutu su karantar da yaran Madina, wannan shi ne fansarsu.

Allah ya kawo Kimiyya da fasaha da za a iya ganin abin da ido ba zai iya gani ba daga nesa (Telescope) sabida haka duk duniyar Malaman Musulunci suka yi fatawa cewa yanzun in Makkah ta ga watan Ramadana to duk Musulmi su dauki niyyar azumin.

In Sarkin Musulmi ya ga dama ya yi amfani da hadisin kuraibu, tafiyar iyaye da kakanni cewa kowacce kasa da ganin watanta, Sarkin Musulmi ya yi dai-dai, in ya amshi sabuwar fatawa, sabida Hadisin “Sumu li ru’u’yatihi, wa afdiru li ru’u’yatihi – ku yi azumi in kun ga wata sannan ku ajiye in kun ga wata.” Hadisin ya nuna cewa Annabi (SAW) ya hade Jama’arsa duka gaba daya.

In an ce Makkah, kar ka kalli wadanda suke cikin garin, ka yi amfani da garin, shi ne wanda Annabi ya zauna a ciki, tushen Addinin Musulunci.

Dangane da garuruwan da ba su da dare kuwa, kullum rana ce, su kaddara wata, su yi amfani da lokaci, a tsakiyar rana amma lokacin sahur ne ko kuma a tsakiyar rana amma lokacin shan ruwa ne.

In wani musulmi ya ga wata amma Sarkin Musulmi bai amsa maganarshi ba, to shi wanda ya ga watan azumin ya hau kanshi, sai ya azumci azumin a boye sabida girmama hukuma. Addini ya hana Jama’a ta zauna ba shugabanci.

Hadisin kuraibu, tulin Malamai da Shehunnai suna kan wannan Hadisin kuma wayayyu ne sun yarda da zamani.

Hadisin Kuraibu, Muslim ne ya ruwaito shi kuma ingataccen Hadisi ne, Ummul Fadli binti Haris, Matar Abbas dan Abdulmudallib ce ta aiki Kuraibu Sham, wajen Mu’awiya. Kuraibu yake cewa, bayan na isar da sakonta ina Sham, sai azumi ya riske ni ina can, mun ga jinjirin watan Ramadana ranar Alhamis da dare, bayan na dawo Madina, sai Abdullahi dan Abbas ya yi mun zance kan watan, ya tambaye ni yaushe muka ga watan Ramadana a Sham, sai na ce masa ranar Alhamis da dare, sai ya ce min kai ma Allah ya azurtaka da ganin shi? Na ce masa eh, Jama’a da dama sun gan shi, har Khalifa Mu’awiya ma ya yi Azumi, Abdullahi dan Abbas ya ce masa amma mu sai daren Asabar muka ganshi, kuma za mu ci gaba da azumi har sai mun yi 29 ko 30, Kuraibu ya ce masa shin ba za ka wadatu da ganin wata da azumin Khalifa ba, Abdullahi ya ce a’a, ba zan wadatu da ganinsu ba, haka Annabi (SAW) ya umurce mu, kowacce al’umma da ganin watansu.

Wannan Hadisi ingatacce, galibin malamai suna kan shi amma malamai na zamani masu ilimi da fahimta sun tafi cewa tun da Allah ya kawo wadannan ci gaba na kimiyya da fasaha, ba laifi in Sarkin Musulmi ya yarda da ganin watan Makkah ya ce al’ummar Musulmi na duniya su tashi da azumi a rana daya.

An karbo daga Hafsatu Ummul Muminina ta ce Manzon Allah (SAW) ya ce “Duk wanda bai yi niyyar Azumi ba kafin Asubah, bai da azumi”

Ba laifi, mutum zai iya kudurce niyyar yin azumin Ramadana 29 ko 30 a daren azumin farko bayan an sanar da ganin watan ko kuma ya kudurce niyyar azumin ko wacce rana na daga watan ramadana din. Amma ka kwanta bacci da nufin cewa in an ga watan zan ci gaba da azumi in ba a gani ba shikenan, hakan shari’ah ba ta yarda ba.

Azumin watan Ramadana wajibi ne ga dukkan Musulmi baligi mai lafiya ba mara lafiya ba, wajibcin azumi kamar yadda Allah ya fada a cikin Al’kur’ani da fadarsa yana cewa: “Ya ku Muminai Allah Ya wajabta muku yin azumi kamar yadda ya wajabta ma wadanda suka zo kafin ku, ko za ku ji tsoron Ubangijinku. Kwanaki ne kididdigaggu, wanda ya kasance a cikinku bai da lafiya ko kuma yana kan tafiya, to ya rama abin da ya kubuce masa a wasu ranakun, wadanda kuma ba za su iya yin azumin ba, to su ciyar da Miskinai, amma wanda yake da damar ciyar da miskinai da yawa, to ya yi alkairi ne a wajenshi, lallai yin azumin ya fi alkairi a gare ku, idan kun san wannan alkairin da ke cikin azumin.”

Haka nan a aya ta gaba, Allah ya ce, “Lallai watan Ramadana da aka saukar da Alkur’ani a cikinshi, shiriya ne ga mutane, sannan kuma akwai ayoyi bayyanannu a cikinshi masu shiryarwa zuwa ga Allah da bayyana hukunce-hukunce. Duk wanda ya halarci ganin watan to ya azumce shi, wanda kuma bai da lafiya ko kuma yana kan tafiya, to ya biya abin da ya tsere masa a cikin sauran wasu ranakun, Allah sauki yake nema daga wurinku ba wahalarwa ba, Allah yana son ku cika adadin azumin, sannan yana son ku yi masa kirari daga abin da ya shiryar da ku, ko za ku gode masa?”.

 

Saukar Da Alkur’ani Da Littafan Manzanni

Allah ya saukar da mafificin Littafi (Alkur’ani) a cikin watan Ramadana, a mafificin dare (Lailatul Kadri).

An karba daga Abdullahi bin Abbas, Allah ya yarda da su, yake cewa “Allah Ya saukar da Alkur’ani daga Lauhil Mahfuzi izuwa saman Duniya (a cikin Ramadana aka saukar da Alkur’ani daga Lauhil Mahfuzi zuwa saman Duniya, a dakin Baitul ilimi), Mala’ika Jibril (AS) shi kuma daga nan yake debo ayoyinsa zuwa ga Annabi (SAW), sai da ya shafe shekaru 23 yana kan wannan aikin.

An karba daga Wa’ilatu bin Asda’in ya karba daga manzon Allah (SAW) cewa an saukar da littattafan Annabi Ibrahim (AS) a daren farko na watan Ramadana; Littafin Attaurar Annabi Musa (AS), ta sauka a daren bakwai na watan Ramadana; Injilar Annabi Isa (AS) ta sauka 13 ga watan Ramadana; sai Alkur’anin Annabi Muhammad (SAW) ya sauka daren 14 ga watan Ramadana.

Abdullahi bin Abbas ya ce, Annabi SAW ya fada wa wata Mata daga cikin Mutanen Madina cewa idan Ramadana ya zo, ta je ta yi Umra, domin yin Umra a cikin watan Ramadana daidai yake da aikin Hajji, Nasa’i ya ruwaito Hadisin.

Allah ya ba mu damar azumtar wannan azumin gabaki daya, Allah ya buda wa ‘yan uwa musulmin duniya da abin da za su ci su sha, Allah ya bai wa kasarmu Nijeriya zaman lafiya. Allah ya saka wa iyayenmu na Zawiyya da alkairi wanda da albarkarsu da karfin Allah muke gudanar da wannan lamarin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Maraba Ramadan saukar da Alkur ani ga watan Ramadana Hadisin Kuraibu da ganin watan Sarkin Musulmi da ganin wata

এছাড়াও পড়ুন:

Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 115

115-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissiso da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin dastane rastan, ko kum littafin mathnawi na maulana Jalaluddeen rumi. Ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin shirimmu na yau.

///… Masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Al-hassan limami na biyu daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All..(s), kuma da na farko ga Fatimah(s) diyar manzon All..(s), sannan jikansa na farko.

A cikin shirimmu da ya gabata, mun ji yadda wasu malaman tarihi suka kawo wasu hadisai wadanda basu inganta ba suka jinginawa Imam Alhassan Almujtaba (a) dangane da son da yakewa khalifa na ukku wasu Uthman bin Affan, mun gudanar da bincike cikin daya daga cikin hadisan a sanadi da kuma mataninsa inda muka tabbatar da cewa , Mada’ini wanda aka ruwaito wannan hadisin, nasibi ne, wato wata jama’a wacce ta ke addini da kiyayya ga iyalan gidan manzon All..(s), har’ila yau yana kirkiro hadisan na kariya ya jinganawa manzon All..(s) na muzantasu da kuma kirkiro wasu hadisan daga manzon All..(s) na yabon banu umayya.

Sannan a matanin hadisin mun bayyana kariyar zance mai cewa Imam Hassan yana zargin babansa Imam Ali (a) da hannu a kashe Uthman dan Affan, sannan yana tare da mahaifinsa, manya-manyan yake-yake guda biyu da yayi a lokacin khalifancinsa, da wadanda  suke tuhumarsa da zubar da jinin Khalifa Uthman.

Wato yake-yaken Jamal da Siffin. Imam Hassan (a) ya yaki wadannan makiyan mahaifinsa wadanda suke zarginsa da hannu a kissan Uthman. Kuma bamu taba sanin akwai sabani tsakanin Imam Ali (a) da yayansa Alhassan da Alhussain (a).

Daga karshen mun kawo maku yadda manyamanayn sahabban manzon All..(s) da suka rage a Madina suka rubuta wasi ku zuwa sauran sahabbansa a sauran yankuna na daular musulunci suna neman taimakonsu don kauda Khalifa uthman daga khalifanci, saboda ya sabawa littafin All..da sunnar manzon All..da kuma siran khalifofin da suka gabata. Sun koka kan yadda ya mika al-amuran daular musulunci ga danginsa banu Umayya suna satar dukiyar al-umma sannan sun barsu da talauci.

Mun bayyana cewa akwai abubun lura a cikin wannan wasikar kamar haka,

1-Sunan zarginsa na kin amfani da littafin All..

02-Sauya sunnan manzon All..(s) da kuma, yayi watsi da ita,

03-yayi watsi ga hanyar khalifofin biyu da suka gabace shi wato Abubakar da Umar

04- Ya kauda ma’anar khalifancin manzon All..(s) daga yadda yakamata ta kasance,

5-Kwace dukkan duniyar Al-ammu da kuka sarrafata a wasu wurare kebantattu, wato kashe ta kan dangin khalifa wato Banu Umayya.

Malaman tarihi sun bayyana cewa, wadannan al-amura sun girgiza daular musulunci, kuma sun kusan su rusata.

Sannan mun bayyana cewa wadanda suke sukan shugabancin Khalifa Uthman sun rubuta wata wasika ga murabiduna, wato wadanda suke kula da kan iyakokin daular musulunci daga cikin sahabbai, sun bukacesu su dawo madina don tsada khalifancin manzon All..(a), don tabbatar da khaifancin ya dawo kan yadda yakamata ya kasanci.

Ga kuma matanin wasikar kamar haka.

{Lalle ku, kun fita ne don ku yi jihadi a kan tafarkin All..mai girma da daukaka, kuna neman kare addinin Muhammad (s) to lalle khalifanku ya lalata addnin Muhammadu, ku dawo ku tsaida shi,…}.

Banda haka a lokacinda wasikun nan suka isa yankuna da dama na daular musulunci sun yi ta aika tawaga don ganin abinda yake faruwa a Madina, sannan tawagogi da suka isa Madina don ganewa idanunsu abubuwan da suke faruwa, da kuma tattauna matsalolin da kuma yadda za’a magance su, sun hada da.

Tawaga daga kasar Masar, kafin haka akwai mutane 700 da suka tura tun farko bayan da suka kama wani bawan Khalifa Uthman wanda ake kira warsh dauke da wasikar Khalifa zuwa dan uwansa gwamnan Masar Abdullahi ibn Abisharkh, na ya kashe sui dan sun isa da sabon kwamna Muhammad dan Abubakar.

A wannan karon mutanen masar sun aiki mutane 400. Tare da jagorancin Muhammad dan Abubakar wanda dama yana manina, da Abdrrahman dan Udais Al-balawi.

2-sai tawagar Kufa wanda ya hada da Malik dan Ashtar, Zaidu dan Sauhan Al-Abdi, da Ziyad dan Annadhir Al-harithy. Da abdullahi dan Asam Al-Amuri da shugabansu gaba daya, Amru dan Ah-tham .

03-sai tawagar Basra wacce ta hada da Hakin dan Jibilah, tere da wasu mutane 100. Bayan haka wasu khamsin sun bisu. A cikinsu akwai Zarih dan Abidi Al-Abdi, da bishru dan shuraih Alkaisi, da dan Mahrash, da wasunsu daga cikin fitattun mutane kuma sanannu na Basra.

A lokacinda wadannan tawagogi suka isa Madina an yi maraba da su, kuma nag ode masu da karban kiran da aka yi masu, sannan sun tattauna da sauran sahabbai da kuma musulmai dan al-amuran da suka faru, da kuma irin mummunan halin da musulmi suka shiga ciki saboda yadda Khalifa Uthman ya sauya al-amura da dama, daga cikin ya hanasu dukiyoyinsu, wadanda suka saba samu a zamanin khalifofin da suka gabata. Ko kuma ya fita daga tsarin da manzon All..(s) yake raba dukiya a cikin al-umma.

Bayan yan kwanaki sai mutanen kasar masar sun ga cewa kafin ko me da farko a rubutawa khalifa Usman  wasika, a yi masa nisiha kan ya dawo kan tafarkin da ya dace ga kuma kadan daga cikin abinda wasikar ta kunsa.

Bayan Basmala da salati ga manzon All..(s) da kuma godiya ga All..sai suka ce

(bayan haka, ka sani kan cewa, {Lalle All..baya sauya halin da mutane suke ciki sai sai sun sauya halinsu, muna hadaka da All..kuma muna sake hadaka da All..Lalle kai kana cikin duniya mai gucewa, … .. kuma kada ka manta da rabon a lahira, kada duniya ta rudeka, kuma ka san cewa mu don All..muke yi, kuma don All…muke fushi. Kuma muna neman yardarm All.. ne, kuma lalle ba zamu dauke takubbammu daga wuyoyimmu ba saika tuba daga abubuwan da ka aikata mana, tuba mai tsanani kuma a fili, wannan shi ne maganarmu da kai, sannan bukatarmu a gareka, All..ne mai karban uzurimmu dangane da kai..wassalam…}.

A lokacinda Khalifa Uthman ya karanta sai ya ji tsoro. Sai Mughira ya nemi izininsa yayi Magana da mutane, sai ya bashi izini, a lokacinda suka ganshi sai suka daga murya suna cewa: Ya makaho  koma ya Fajiri koma ya fasiki koma.ya koma ya kasa Magana da su.

Sai Uthman ya kira Amru dan Asi, ya bukaci yayi Magana da su, ya amince, amma a lokacinda suka ganshi, sai yayi masu, sallama ba wanda ya amsa daga cikinsu,  suka daga murya suna cewa: Ko koma ya makiyin All.. ka kuma ya dan Nabigha. Kai ba amintecce ne a wajemmu ba kuma mai aminci ba.

A nan sai Khalifa Uthman ya fahinci cewa babu wanda zai taimaka masa sai Amirulminina Aliyu dan Abitalib (a), sai ya nemi taimakonsa, ya fada masa cewa, yayi kira ga mutane zuwa ga Alkur’ani mai girma da sunnar annabinsa.

Sai Imam ya amince, amma da sharudda kan cewa, ya yi masa alkawali tsakaninsa da All..zai yi aiki da abinda ya fada. Sai ya yi alkawali zai zai cika alkawalinsa, za iyi aiki da abinda ya fada.

Sai Imam (a) ya je wajen mutane, shima a lokacinda suka ganshi suka ce, koma , sai yace a’a na zo maku da cewa, za’a yi aiki da littafin All.., kuma za’a sauya duk abinda kuka yi fushi dominsa. Sai ya fada masu abinda khlifa ya bada.  Sai suka ce: Ka lamunce mana haka zai faru? Sai yace :ee. Sai suka ce mun yarda.   

Sai ya shigar da manya manya daga fitattun mutane  wajen Uthman, sai suka yi ta sukansa, sannan suka ce, ya Sanya abinda ya yi alkawali na aiki da littafin All..da kuma sunnar manzon All..(s) da kuma bawa musulmi hakkinsu da ake basu.

Sai ya amince ya rubuta ya basu sannan suka karbi takardan suka kama hanyar masar.

Wannan shi ne nassin abinda ya rubuta ya basu’

{Wannan rubutun daga bawan All..Uthman Amirulmuminina zuwa ga wadanda suke sukansa daga cikin muminai da musulmai, kan cewa hakkinsu ne in yi aiki da littafin All..da sunnar annabinsa a cikinu, za’a bawa talaka hakkinsa, wanda yake cikin tsoro a amintar da shi, wanda aka kora adawo da shi …kuma za’a samar da kudade ga musulmi. Sannan Aliyu dan Abitalib (a) shi ne mai lamuncewa muminai, kuma wajibi ne ga Uthman ya cika alkawalin da ya dauka cikin wannan rubutun}.

Banda haka Zubair dan Awwam, Talha dan Ubaidullahi,Sa’du dan Abi wallas, Abdullahi dan Umar, Zaidu dan Thabit, Sahal dan Hunaif,, Abu ayyuba Khalid dan zaid, kuma anyi wannan rubutun a cikin watan Zulkida shekara ta shekara 35.

Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shirimmu nay au sai kuma wata fitowa idan All..ya kaimu. Wassalau alaikum warahamatullahi wa barakathu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Sin Na Maraba Da Karin Abokai Daga Kasa Da Kasa Su Ziyarci Kasar
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Sama Da Masu Sayayya Daga Ketare 220,000 Ne Suka Halarci Bikin Baje Kolin Canton Karo Na 137
  • Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Sarkin Musulmi Ya Ayyana Ranar Talata 1 Ga Watan Zulki’ida
  • Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu
  • Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 115