Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya, a karon farko ya yi Allah-wadai da kasar Rwanda kan goyon bayan da take bai wa mayakan kungiyar M23 a gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango (DRC).

Kwamitin ya kuma nemi ksar ta Rwanda da ta”gaggauta” janye sojojinta daga gabashin Jamhuriyar Demokuradiyyar Kwango.

Kudurin na ranar Juma’a “ya kuma yi kakkausar suka ga hare-haren da kuma ci gaban da kungiyar M23 ke ci gaba da yi a arewacin Kivu da Kivu ta Kudu tare da goyon bayan dakarun tsaron kasar ta Rwanda”.

A wani labarin kuma sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya yi kira da a tsagaita bude wuta nan take a gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango yayin wata tattaunawa ta wayar tarho da shugaban Kenya William Ruto.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka Tammy Bruce a wata sanarwa da ta fitar ta ce “Sun jaddada cewa babu wata hanyar soji da za ta magance rikicin, kuma sun yi kira da a tsagaita bude wuta cikin gaggawa.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Kama Wata Mata Da Take Shirin Kashe Benjemin Netanyahu

Kafafen watsa labarun HKI sun ambato hukumar leken asiri ta “Shabak’ tana sanar da kame wata mace, dake zaune a tsakiyar wannan haramtacciyar kasa bayan da aka tuhumeta da Shirin kashe Fira minister Benjamin Netanyahu.

‘Yan sandan HKI sun ce, matar da aka kama ta so yin amfani da abubuwa masu fashewa da ake kerawa da hannu ( IDE), kuma a halin yanzu  Shabak tana gudanar da bincike.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Naira: Kotu ta yanke wa Hamisu Breaker da G-Fresh hukunci ɗaurin wata 5
  • Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD
  • Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta
  • ‘Yan Tawayen Sudan Ta Kungiyar Rapid Support Forces Sun Kashe Mutane 27 A Yammacin Jihar Kordofan Ta Kasar Sudan
  • Matsalar Tsaro: Sarakuna Sun Bukaci Gwamnati Ta Canza Salo
  • Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
  • Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Fara Tattaunawa kan Masifar Zirin Gaza Na Falasdinu
  • An Kama Wata Mata Da Take Shirin Kashe Benjemin Netanyahu
  • Tinubu na amfani da ƙarfin mulki wajen tsoratar da ’yan adawa — Sule Lamido
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Hakkinta Na Tace Sinadarin Uranium A Cikin Kasarta