Shin Mbappe Zai Iya Maye Gurbin Ronaldo A Real Madrid?
Published: 30th, March 2025 GMT
A shekarar 2009 ne Cristiano Ronaldo ya saka hannu akan kwantiragin da ya sa ya zama sabon dan wasan Real Madrid, tun daga wancan lokacin Ronaldo ya jefa kwallaye 311 a wasanni 292 da ya bugawa Madrid, hakazalika ya lashe kofuna 15 a shekaru 9 da ya kwashe a Santiago, to amma yanzu Fionrentina Perez ya dauko wani Bafaranshe daga PSG, wanda yanzu haka ya dauko hanyar doke tarihin Ronaldo a Real Madrid.
Kylian Mbappe ne ya jefa kwallaye 2 a wasan da Real Madrid ta doke Leganes, wanda hakan ya sa ta samu maki daya da abokiyar hamayyarta Barcelona dake saman teburin La Liga, kwallaye biyun da Mbappe ya ci ya sa kwallayen da Mbappe ya ci a kakar wasa ta bana su ka kai 33.
Mbappe Da Bellingham Ba Za Su Buga Wasan Da Real Madrid Za Ta Kara Da Leganes Ba Real Madrid Ta Kwashi Kashinta A Gidan BetisMasu masaukin bakin, wadanda su ka fara wasan ba tare da Vinicius Jr, Rodrygo da Federico Valverde ba sakamakon hutun wasan kasashe da su ka tafi, yanzu sun yi daidai da maki tare da Barcelona wadda ke matsayi na daya da maki 63 a wasanni 29 kafin Barcelona ta buga wasanta na wannan makon tsakaninta da Girona.
Ana hasashen muddin Mbappe ya cigaba da zura kwallaye a ragar abokan karawa, zai iya zarce Ronaldo wajen zura kwallaye duba da cewar har yanzu ba a kammala kakar kwallon kafa ta bana ba, sannan kuma tsohon dan wasan na PSG ya lashe kofunan UEFA Super Cup da kuma FIFA Intercontinental Cup.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
A ci gaba da hare-haren da dakarun Isra’ila ke kai wa a Zirin Gaza, yanzu adadin Falasdinawan da suka kashe ya kai 60,034.
A cewar wasu alkaluma daga Ma’aikatar Lafiya ta Gaza, baya ga wannan, adadin wadanda aka raunata kuma a yanzu sun haura 145,870.
Ma’aikatar ta kuma ce har yanzu ana zargin akwai mutanen kuma da ke karkashin baraguzan gine-ginen da aka rusa, wadanda ba za a iya ciro su daga ciki ba.
Fiye da kaso daya cikin uku na mutanen yankin na shafe kwanaki ba su ci abinci ba, kamar yadda wani rahoton samar da abinci mai lakabin IPC na Majalisar Dinkin Duniya ya tabbatar.
Rahoton ya ce ana samun karin hujjoji da ke nuna ana fama da yunwa da karancin abinci da kuma karuwar mace-mace masu alaka da yunwa a yankin da sama da mutum miliyan biyu da dubu dari daya ke rayuwa a cikinsa.
Hukumomi daban-daban na Majalisar Dinkin Duniya dai sun yi gargadin cewa ana fama da matsananciyar yunwar da aka kirkira da gangan a Gaza, inda a iya wannan watan, rahotanni suka tabbatar da mutuwar mutum 63, dalilin yunwar.
Hukumomin dai sun dora wa Isra’ila duk alhakin matsalolin, kasancewar ita ta yi wa yankin kawanya ta kuma hana a shigar da kayan agaji.
Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres, ya ce: “Abubuwa ne ga su nan a Zahiri, ba a boye suke ba. Falasdinawan da suke Gaza na cikin mawuyacin hali da tsananin bukatar agaji.
“Wannan ba wai gargadi muke yi ba. Gaskiya ce ga ta nan karara. Dole kayan agaji su ci gaba da kwarara. Abinci, ruwan sha, magunguna da man fetur dole su ci gaba da shiga ba tare da kowanne irin tarnaki ba,” in ji Guterres.