Aminiya:
2025-08-08@08:56:41 GMT

Super Eagles ta gamu da cikas a ƙoƙarin neman tikitin Gasar Kofin Duniya

Published: 26th, March 2025 GMT

Tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta gamu da cikas a ƙoƙarinta na neman yankar tikitin shiga Gasar  Kofin Duniya ta baɗi, bayan da ta tashi canjaras 1-1 da Zimbabwe.

Victor Osimhen ne ya fara ci wa Nijeriya kwallo a minti na 74 a filin wasa na Godswill Akpabio da ke Uyo, babban birnin Jihar Akwa Ibom.

Masu neman yi wa Natasha kiranye ba su cika ƙa’ida ba — INEC Dalilin da dimokuraɗiyya ta gaza kawo ci gaba a Afirka — Obasanjo

Sai dai Zimbabwe ta farke ana daf da tashi a minti na 90 ta hannun ɗan wasanta na gaba, Taranda Chirewa.

Wannan sakamako na nufin cewa Nijeriya na matsayi na huɗu a rukunin C, inda Ghana ke gabanta a matsayi na ɗaya da kusan ratar maki shida bayan buga wasanni shida.

Wasan da Nijeriya za ta yi Bafana Bafana a watan Satumba, zai kasance mai matuƙar muhimmanci, la’akari da cewa ƙasar da ke saman kowane rukuni ne kaɗai ke samun damar zuwa Gasar Kofin Duniya.

A ranar Juma’a ce tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta doke Rwanda da ci 2-0 a birnin Kigali a wasannin neman gurbin shiga Gasar Kofin Duniya.

Ɗan wasan Nijeriya Victor Osimhen ne ya zura duka ƙwallayen biyu gabanin hutun rabin lokaci.

A lokacin Nijeriya ta koma matsayi na huɗu a cikin ƙasashe shida da ke Rukunin C bayan wasanni biyar-biyar.

Ƙasar da ta zama ta farko a kowane rukuni daga cikin rukunai tara na ƙasashen Afirka ne ke da tabbacin shiga gasar kofin na duniya, wanda a karon farko aka faɗaɗa zuwa ƙasashe 48.

Sai kuma za a zaɓi ƙasashe huɗu da suka fi ƙoƙari daga cikin waɗanda suka zama na biyu, sai su fafata wasan kifa-ɗaya-ƙwala na neman cike gurbi, inda waɗanda suka samu nasara za su iya samun damar shiga gasar.

Sauran wasannin da suka rage wa Super Eagles su ne na ranar 1 ga Satumba wanda Nijeriya za ta yi da Rwanda sai na ranar 8 ga Satumba tsakaninta da Afirka ta Kudu da kuma na ranar 6 ga Oktoba da za ta fafata da  Lesotho sai cikon na ƙarshe wanda za ta yi karon batta da Benin a ranar 13 ga Oktoba.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gasar Kofin Duniya Nijeriya Kofin Duniya shiga Gasar Gasar Kofin

এছাড়াও পড়ুন:

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

Mun san cewa, ci gaban harkokin matasa na bukatar bunkasar sana’o’i. Cikin shekarun nan, aikin zuba jari ga kasashen Afirka da kasar Sin ke yi na samun ci gaba yadda ake bukata. Inda yawan kudin da Sin take zubawa kai tsaye a fannin samar da kayayyaki a kasashen Afirka, ya kai fiye da dalar Amurka miliyan 400 a duk shekara. Kana darajar hadin kan bangarorin Afirka da Sin ta fuskar gina kayayyakin more rayuwa, ta kai fiye da dala biliyan 37 a duk shekara. Hadin gwiwar bangarorin 2 ya shafi zirga-zirgar ababen hawa, da aikin gona, da makamashi, da tattalin arziki mai alaka da fasahohin zamani, da fasahohin bunkasa tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba, da dai sauransu, ta yadda ya taimaki kokarin raya masana’antu da habaka tsarin tattalin arziki zuwa fannoni daban daban a kasashen Afirka, da samar da dimbin guraben aikin yi, gami da damammakin raya sana’o’i ga matasan kasashen.

Ban da haka, ci gaban harkokin matasa ba zai rasa alaka da karuwar ilimi da ingantuwar fasahohi ba, inda a wannan fanni ma kasar Sin ta tsara ayyukan hadin kai da yawa, don samar da damammakin samun horon fasahohin sana’o’i ga dimbin matasan Afirka, da horar da kwararrun masana matasa masu ilimin aikin gona da masu jagorantar aikin wadatar da manoma ta wasu sabbin fasahohi a kasashen Afirka, da kafa cibiyoyin bude sabbin kamfanoni da kirkiro sabbin fasahohi na matasa, da kulla huldar hadin kai tsakanin jami’o’i dari 1 na kasashen Afirka da kasar Sin, da dai sauransu. Inda gasar da muka ambata ita ma take cikin ayyukan da aka tsara tare da aiwatar da su.

Sande Ngalande, darakta ne na cibiyar nazarin batutuwa masu alaka da shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” ta jami’ar Zambia. Ya taba bayyana cewa, dabarar kasar Sin ta zamanantar da kasa ta amfani kasashen Afirka, inda dimbin matasan Afirka masu sana’o’i daban daban ke son mu’ammala da Sin, da fahimtar Sin, da koyon fasahohin kasar Sin. Kana ta hanyar hadin gwiwar Sin da Afirka, matasan Afirka suna iya kulla zumunci mai zurfi da Sinawa, gami da samun damar raya kansu, da kasashensu, da tabbatar da ci gaba mai dorewa a nahiyar Afirka.

Cikin shirin ajandar shekarar 2063 na kungiyar kasashen Afirka ta AU, an ce ya kamata a sanya matasa su zama karfin farfado da nahiyar Afirka, kuma hadin gwiwar Sin da Afirka na taimakawa wajen ganin tabbatuwar wannan buri a zahiri. (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji
  • Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza
  • Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana
  • An Bude Gasar Wasannin Ta Duniya Ta 2025 A Chengdu
  • Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
  • Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya
  • Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi
  • Mulkin Tinubu ya fi na Buhari muni — Maina Waziri
  • Buni ya shirya bikin karrama daliban da suka lashe gasar duniya
  • Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida