Super Eagles ta gamu da cikas a ƙoƙarin neman tikitin Gasar Kofin Duniya
Published: 26th, March 2025 GMT
Tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta gamu da cikas a ƙoƙarinta na neman yankar tikitin shiga Gasar Kofin Duniya ta baɗi, bayan da ta tashi canjaras 1-1 da Zimbabwe.
Victor Osimhen ne ya fara ci wa Nijeriya kwallo a minti na 74 a filin wasa na Godswill Akpabio da ke Uyo, babban birnin Jihar Akwa Ibom.
Sai dai Zimbabwe ta farke ana daf da tashi a minti na 90 ta hannun ɗan wasanta na gaba, Taranda Chirewa.
Wannan sakamako na nufin cewa Nijeriya na matsayi na huɗu a rukunin C, inda Ghana ke gabanta a matsayi na ɗaya da kusan ratar maki shida bayan buga wasanni shida.
Wasan da Nijeriya za ta yi Bafana Bafana a watan Satumba, zai kasance mai matuƙar muhimmanci, la’akari da cewa ƙasar da ke saman kowane rukuni ne kaɗai ke samun damar zuwa Gasar Kofin Duniya.
A ranar Juma’a ce tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta doke Rwanda da ci 2-0 a birnin Kigali a wasannin neman gurbin shiga Gasar Kofin Duniya.
Ɗan wasan Nijeriya Victor Osimhen ne ya zura duka ƙwallayen biyu gabanin hutun rabin lokaci.
A lokacin Nijeriya ta koma matsayi na huɗu a cikin ƙasashe shida da ke Rukunin C bayan wasanni biyar-biyar.
Ƙasar da ta zama ta farko a kowane rukuni daga cikin rukunai tara na ƙasashen Afirka ne ke da tabbacin shiga gasar kofin na duniya, wanda a karon farko aka faɗaɗa zuwa ƙasashe 48.
Sai kuma za a zaɓi ƙasashe huɗu da suka fi ƙoƙari daga cikin waɗanda suka zama na biyu, sai su fafata wasan kifa-ɗaya-ƙwala na neman cike gurbi, inda waɗanda suka samu nasara za su iya samun damar shiga gasar.
Sauran wasannin da suka rage wa Super Eagles su ne na ranar 1 ga Satumba wanda Nijeriya za ta yi da Rwanda sai na ranar 8 ga Satumba tsakaninta da Afirka ta Kudu da kuma na ranar 6 ga Oktoba da za ta fafata da Lesotho sai cikon na ƙarshe wanda za ta yi karon batta da Benin a ranar 13 ga Oktoba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gasar Kofin Duniya Nijeriya Kofin Duniya shiga Gasar Gasar Kofin
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
Kungiyar ‘Abokan Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya’ ta yi Allah wadai da harin da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai kan Iran
Kasashe mambobin kungiyar aminan yarjejeniyoyin Majalisar Dinkin Duniya sun fitar da wata sanarwa ta musamman inda suka yi kakkausar suka kan wuce gona da irin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Sanarwar ta yi la’akari da harin hadin gwiwa ta sama da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kaddamar a ranar 13 ga watan Yuni a kan wasu wurare da dama a Iran, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da jikkata wasu daruruwa da suka hada da mata da kananan yara da masana kimiyya, matakin da ya saba wa Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya da muhimman ka’idojin dokokin kasa da kasa.
‘Yan kungiyar sun kuma yi Allah wadai da harin ganganci kan fararen hula, da wuraren zaman jama’a, da kuma cibiyoyin nukiliyar na zaman lafiya, suna masu gargadin cewa irin wadannan ayyuka na iya haifar da watsuwar kayan aikin kimiyya da zai zama babbar barazana ga rayuwar fararen hula da muhalli.
Kungiyar ta yi kira da a tsaya tsayin daka kan amfani da karfi a kan Iran, tana mai jaddada nauyin da ke wuyan babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya na kiyaye manufofi da ka’idojin Yarjejeniyar Majalisar.
Har ila yau, ta jaddada aikin babban daraktan hukumar ta IAEA na yin Allah wadai da hare-haren da haramtacciyar kasar Isra’ila ke kaiwa kan cibiyoyin nukiliyar Iran.