Aminiya:
2025-09-19@09:41:15 GMT

Sanata Buba ya ƙaddamar da allurar rigakafin dabbobi kyauta

Published: 5th, August 2025 GMT

Sanatan Bauchi ta Kudu, Shehu Buba Umar ya ƙaddamar da allurar rigakafin dabbobi da kuma takin zamani kyauta ga al’ummar mazaɓarsa.

Da yake ƙaddamar da allurar rigakafin dabbobin garin Goɗɗiya da ke Ƙaramar Hukumar Bogoro, Sanata Buba ya ce, “A bana, za mu yi allurar rigakafin dabbobi 85,000 a wannan yankin na Majalisar Dattawa.

Ya ce a baya an yi wa dabbobi kimanin 40,000 allurar rigakafin a fadin yankin.

“Na yi imanin cewa wannan abu ɗaya ne daga ayyukan wakilci wa mutanenmu manoma da makiyaya. ’Yan Najeriya ne kamar mu duka, suna zaɓe mu, kuma suna ba da gudummawa sosai ga tattalin arzikin ƙasar nan.

“Wannan ba wani abu ba ne na musamman amma na yi imanin cewa wani abu ne da muke yi wa makiyaya da manoma.”

Ya ce alluran rigakafin na kyauta na da nufin kare rayuwar dabbobi, da ƙara haɓaka kiwonsu, da kuma tabbatar da lafiyarsu da wadatar abinci a ƙananan hukumomi bakwai da ke Shiyyar Bauchi ta Kudu.

“Wannan aikin wata babbar alama ce da ke nuna aniyarmu ta kare lafiyar dabbobinmu, da kare lafiyar al’ummarmu, da kuma martaba tattalin arzikinmu.

“Za a gudanar da wannan aiki a dukkanin ƙananan hukumomin bakwai na shiyyar Sanata na Bauchi ta kudu, inda za a yi wa shanu, tumaki da awaki a kowace ƙaramar hukuma alluran rigakafin.

“Ƙwararrun likitocin dabbobi da masana kimiyyar kiwon lafiyar dabbobi za su yi aiki tare da shugabannin al’umma, masu dabbobi, da sauran masu ruwa da tsaki don tabbatar da cewa wannan aikin ya samu nasara a a kowace ƙaramar hukuma.”

Wani mai ruwa da tsaki a mazaɓar Dass, Tafawa Valewa da Vogoro Alhaji Aminu Tukur ya buƙaci manoman yankin da su fito da dabbobinsu domin yin rigakafin.

Tukur ya yi kira ga Sanatan da ya gina cibiyar koyar da sana’o’i a yankin domin rage yawan matasa marasa aikin yi, ya kuma shawarce shi da ya riƙa bibiyar aikin hanyar Gwamnatin Tarayya da tsohon Shugaban Majalisar Wakilai Yakubu Dogara ya fara da ba a ƙarasa su ba.

Makiyaya da dama da suka ci gajiyar allurar sun yaba da yadda Sanata Buba ya jajirce wajen inganta harkokin kiwon dabbobi da lafiyarsu, da tallafa wa manoma ta hanyar ingantattun tsare-tsare da kuma daukar matakai cikin lokaci. Sun nuna jin daɗinsu bisa bayar da tallafin a kan lokaci.

Sankaran ya kuma fara rabon takin zamani buhu 4,200 samfurin NPK kyauta ga manoma.

Ya ce an dauki matakin ne don tallafa wa ayyukan noma da inganta amfanin gona ga manoman yankin.

Sanatan ya ce shirin na da nufin ƙarfafa wa manoma gwiwa domin su sami damar rage ƙalubalen da ake fuskanta wajen samar da abinci tare da inganta adadi da ingancin amfanin gona ga al’ummar gundumar.

Ya gode wa kwamitin rabon kayayyakin tare da shawartar su da su tabbatar da adalci tare da raba kayan ga manoma na gaskiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Allurar rigakafin dabbobi allurar rigakafin dabbobi

এছাড়াও পড়ুন:

Cutar Kwalara ta kashe mutum 58 a Bauchi

Aƙalla mutane 58 ne aka tabbatar da mutuwarsu sakamakon barkewar cutar Kwalara a ƙananan hukumomi 14 daga cikin 20 da ke jihar Bauchi.

Haka kuma, an samu sabbin mutane 258 da suka kamu da cutar a faɗin jihar.

Amurka ta hau kujerar-na-ƙi kan buƙatar MDD ta tsagaita wuta a Gaza An yanke wa Soja hukuncin kisa ta hanyar rataya

Mataimakin Gwamnan jihar, Auwal Mohammed Jatau, ne ya bayyana hakan yayin ƙaddamar da wasu kwamitoci biyu kan yaki da cutar a jihar.

Mataimakin Gwamnan ya nuna damuwarsa kan yadda barkewar cutar ke ci gaba da kashe mutane, lalata rayuwar jama’a, da kuma jefa tsarin kiwon lafiya na jihar cikin matsala.

Jatau ya bayyana cewa: “Ana iya kaucewa wannan barkewar cutar idan aka ɗauki matakan gaggawa, aka haɗa kai wajen tunkarar cutar, tare da ci gaba da inganta ruwa, tsafta da kula da muhalli. Jihar Bauchi ta samu sabbin mutane 258 da suka kamu da cutar, tare da mutuwar wasu 58.”

Ya ƙara da cewa duk da ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke yi, Kwalara na ci gaba da zama barazana ga lafiyar jama’a.

Ya ce kafa kwamitin yaki da cutar ba wai kawai ya zo a kan lokaci ba, har ma yana da matuƙar muhimmanci wajen cimma burin da aka sa gaba na dakile ci gaba da yaduwarta.

A cewarsa: “Wannan kwamitin zai zama ja-gaba wajen jagorancin hukumomin gwamnati a jihar Bauchi kan barkewar Kwalara, tare da tsara dabarun kariya na dogon lokaci da suka yi daidai da Tsarin Ƙasa na Yaki da Cholera da kuma manufofin Cibiyar Dakile Cututtuka ta Najeriya (NCDC).”

Mataimakin gwamnan ya tunatar da mambobin kwamitocin cewa zaɓensu ya nuna ƙwarewarsu, sadaukarwarsu da muhimmancin rawar da za su taka wajen nasarar aikin, tare da fatan za su tabbatar da sa ido, gano cuta da wuri, da kuma ɗaukar matakin gaggawa idan ta barke.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cutar Kwalara ta kashe mutum 58 a Bauchi
  • Sojoji Sun Raba Takin Zamani Ga Manoma A Katsina
  • Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka
  • Gwamnatin Gombe ta gyara hanyoyin kiwo domin daƙile rikicin manoma da makiyaya
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo