Aminiya:
2025-08-05@11:07:28 GMT

Ɗaliba ’yar shekara 15 daga Yobe ta lashe Gasar Muhawara ta Duniya

Published: 5th, August 2025 GMT

Wata ɗaliba ’yar shekara 15 daga Jihar Yobe, Rukayya Muhammad Fema, ta zama Gwarzuwar Shekarar 2025 a Gasar Muhawara ta Duniya ta Teen Eagle.

Rukayya ta yi zarra ne a wannan babbar gasa da ta gudana a birnin Landan na ƙasar Birtaniya, inda zaƙaƙuran ɗalibai daga ƙasashe 69 a faɗin duniya suka fafata a tsakaninsu.

Jami’in Sadarwar Zamani na Gwamnatin Jihar Yobe, Yusuf Ali, ya bayyana cewa Rukayya ta samu kafa wannan tarihi ne a dalilin zurfin tunani da kuma kaifin basirarta da kuma fahimtar al’amuran duniya, duk kuwa da ƙarancin shekarunta.

Ɗalibar daga Kwalejin Nigerian Tulip International (NTIC), Rukayya, ta ɗauki hankalin alƙalan gasar da sauran jama’a saboda ƙarfin hujjojinta da ta gabatar da kuma iya bayani mai ganawarsa cikin natsuwa, lamarin da ya ba ta damar doke duk abokan karawarta.

Nafisa ta cancaci kyautar Dala 100,000 da gida da OON —Pantami NAJERIYA A YAU: Yadda Ayyuka Suka Ragu A Jihohi Bayan Kudin Shiga Ya Karu

Ita ce mutum ya biyu daga Jihar Yobe kuma daga makaranta tare da Nafisa Abdullah Aminu wadda ta zama gwarzuwa a ɓangaren Harshen Turanci a yayin gasar, inda suka wakilci Najeriya, ƙasa mai yawan al’umma sama da miliyan 200.

Nasararta nuna irin basirar da Allah Ya yi wa matasan Najeriya inda suke yin zarra a sassan duniya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗaliba Gasar Muhawara Muhawara Rukayya Girma

এছাড়াও পড়ুন:

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

“Jerin sunayen yaran Gaza da ke mutuwa “, dole ne a tabbatar da ba a kara yawansu ba. Shin wadannan sunayen yara kanana da hotunan su ba za su iya tada hankalin bangarori masu rikici ba?

 

Akasarin kasashen duniya sun yarda cewa “shawarar samar da kasashe biyu” ita ce mafitar warware matsalar Falasdinu, kuma amincewa da kasar Falasdinu wani muhimmin mataki ne na aiwatar da wannan shawara. Kwanan nan, an gudanar da babban taron kasa da kasa kan warware matsalar Falasdinu da aiwatar da shawarar “samar da kasashe biyu” a hedkwatar MDD da ke birnin New York, inda ministocin harkokin wajen kasashe 15 suka sanya hannu kan sanarwar hadin gwiwa, suna nuna niyyar amincewa da kasar Falasdinu. A yanzu, fiye da kashi biyu bisa uku na kasashe membobin MDD sun amince da kasar Falasdinu. Muna fatan ganin an tabbatar da shawarar “kafa kasashe biyu” da wuri, domin hasken zaman lafiya ya zo Gaza. Yaran Gaza ma yara ne, kamar kowane yaro na kowane iyali a duniya, suna da hakkin rungumar gobe. (Mai zane da rubutu:MINA)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nafisa ta cancaci kyautar Dala 100,000 da gida da OON —Pantami
  • ’Yar shekara 17 daga Yobe ta lashe Gasar Turanci ta Duniya
  • Tinubu ya bai wa ’yan wasan ƙwallon kwandon mata kyautar Dala dubu 100 da gidaje
  • Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
  • Ƴan matan Najeriya Sun Lashe Gasar Kwallon Kwando Ta Afirka
  • Gwamnan Yobe ya naɗa Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi
  • Jamus ta soma jefa kayan agaji a Zirin Gaza
  • Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?
  • Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya