Kwalejin Horasda Hafsoshin Soja ta Kasa dake Kaduna -NDA ta karyata jerin sunayen wadanda suka yi nasara shiga kwalejin dake yawo a halin yanzu.

 

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na makarantar, Manjo Mohammed Maidawa ya fitar ya ce jerin sunayen ba su fito daga Kwalejin NDA ba.

 

Don haka ya shawarci jama’a da su yi watsi da jerin sunayen da aka zayyana, domin za a buga sahihan jerin sunayen a cikin fitattun jaridu na kasa da kuma a yanar gizon NDA a kan https://NDA.

edu.ng/, a lokacin da ya dace.

 

PR/Usman Sani.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: jerin sunayen

এছাড়াও পড়ুন:

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

A baya bayan nan, tawagar likitocin kasar Sin ta 24 dake aikin agajin kiwon lafiya a janhuriyar Nijar, ta gudanar da tiyatar ALT irinta ta farko da aka yi nasarar gudanarwa a yankin yammacin Afirka.

An gudanar da tiyatar ne a babban asibitin gwaji na kasar ta Nijar. Kuma ana gudanar da tiyatar ALT ne ta hanyar yankar wasu sassan fata da tsokar cinyar mara lafiya, domin dasawa a wasu sassan jikinsa da suka lalace sakamakon wata matsala.

Ana kallon nasarar da aka samu ta aiwatar da wannan tiyata a Nijar, a matsayin nasarar da za ta cike gibin da ke akwai a fannin, a yankin yammacin Afirka. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin
  • An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang
  • Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka
  • Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya
  • Shugabar Ma’aikata Ta Jihar Kaduna Ta Yi Kiran Amfani Da Fasahar AI.
  • Yadda Jama’a Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
  • Isra’ila na ci gaba da ragargaza Birnin Gaza ta sama da ƙasa
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya