Kwalejin Horasda Hafsoshin Soja ta Kasa dake Kaduna -NDA ta karyata jerin sunayen wadanda suka yi nasara shiga kwalejin dake yawo a halin yanzu.

 

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na makarantar, Manjo Mohammed Maidawa ya fitar ya ce jerin sunayen ba su fito daga Kwalejin NDA ba.

 

Don haka ya shawarci jama’a da su yi watsi da jerin sunayen da aka zayyana, domin za a buga sahihan jerin sunayen a cikin fitattun jaridu na kasa da kuma a yanar gizon NDA a kan https://NDA.

edu.ng/, a lokacin da ya dace.

 

PR/Usman Sani.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: jerin sunayen

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Babban sakatare na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin wato JKS, kana shugaban kasar, Xi Jinping ya bayar da muhimmin umarni game da binciken ra’ayoyin jama’a masu amfani da shafukan Intanet kan aikin tsara shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15 a kwanan nan, inda ya ce, ya kamata aikin tattara ra’ayoyin jama’a ta yanar gizo wajen tsara shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar na 15 ya samu shigar jama’a sosai, kuma ya kasance wani aiki na dimokuradiyya dake shafar dukkan bangarori.

Jama’a sun yi ta ba da shawarwari tare da gabatar da ra’ayoyi masu muhimmanci, wadanda ya kamata sassan da abin ya shafa su yi nazari a hankali tare da shigar da su cikin tsarin. Kuma dole ne kwamitocin JKS da gwamnatoci a dukkannin matakai su bi tsarin da ya shafi al’umma, su gudanar da bincike mai zurfi kan ra’ayoyin jama’a, da sauraron muryoyinsu, da shigar da hikimominsu cikin tsarin, ta yadda za a samar da hadin gwiwa mai karfi don ingnta zamanintarwa irin ta kasar Sin, da ci gaba da tabbatar da cikar burin jama’a na samun ingantacciyar rayuwa.

Daga ranar 20 ga watan Mayu zuwa ranar 20 ga watan Yunin bana, an fara aikin tattara ra’ayoyin jama’a kan tsara shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar na 15 ta yanar gizo, kuma an bullo da shiri na musamman a shafin intanet na Jaridar People’s Daily, da na kamfanin dillancin labarai na Xinhua, da shafin intanet na babban rukunin gidajen rediyo da talbijin na kasar Sin wato CMG, da kuma kan dandalin “Learning Power”, don neman ra’ayoyin jama’a.

Ya zuwa yanzu, aikin ya sami shawarwarin jama’a masu duba shafin intanet sama da miliyan 3, tare da samar da muhimman bayanai don tsara shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar na 15. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet
  • Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana
  • Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15
  • Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
  • Jerin gwanon nuna goyon baya ga al’ummar Gaza a Sydney Australia
  • Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin
  • Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a