Baghaei : Ziyarar Pezeshkian a Pakistan ta bude wani sabon Shafin alaka
Published: 5th, August 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta yaba da ziyarar kwanaki biyu da shugaban kasar Masoud Pezeshkian ya kai a Pakistan, wanda a sakamakon an bude wani sabon shafi na karfafa alaka mai karfin gaske tsakanin Iran da Pakistan da suke makwabtaka da juna.
“Ziyarar shugaban kasar Pakistan na da matukar muhimmanci,” in ji Esmaeil Baghaei yayin wani taron manema labarai na mako-mako a ranar Litinin a birnin Tehran, yayin da yake magana kan ziyarar Pezeshkian.
Baghaei ya ba da misali da matsayar da kasashen suka dauka na yin ciniki cikin ‘yanci bisa yarjejeniyar da ta dace a matsayin wani muhimmin batu na ziyarar, yana mai cewa wannan lamari mai matukar muhimmanci ga bangarorin biyu.
Ya kara da cewa, yayin ziyarar, an rattaba hannu kan wasu takardu 12 a fannoni daban-daban da suka hada da tattalin arziki, kasuwanci, yawon bude ido, safara, da kuma al’adu.
Jami’in ya ce Iran ta kasance kasa ta farko da ta amince da Pakistan bisa kafuwarta, ya kuma yi nuni da dangantaka ta abokantaka da ‘yan uwantaka da aka kulla tsakanin bangarorin biyu tun daga lokacin.
“A tsawon shekarun da suka gabata, dangantaka tana ci gaba da yin karfi, a matakin gwamnati da kuma tsakanin al’ummomin kasashen biyu, Iran na bayar da muhimmanci matuka kan dangantakarta da Pakistan, inji Baghaei.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Afirka ta Kudu ta zayyana matakan tallafi ga ‘yan kasuwa na cikin gida a matsayin martani ga harajin Trump August 5, 2025 Hamas ta musanta kalaman Witkoff game da batun mika makamanta August 5, 2025 Araqchi: Namijin kokarin al’ummar Iran abin yabawa ne August 4, 2025 Khatibzadeh: Iran ba za ta amince da saryar da hakkokinta ba a duk wata tattaunawa da Amurka August 4, 2025 Rahotonni: Agajin Jin kai Da Ake Jefawa Ta Sama A Gaza Ba Shi Da Tasiri August 4, 2025 Wa’adin Da Shugaban Amurka Ya Gindaya Na Kawo Karshen Yaki A Ukraine Ya Karato Ba Tare Da Alamun Karewarsa Ba August 4, 2025 Sojojin Somaliya Sun halaka Mayakan Kungiyar Al-Shabab Fiye Da Hamsin A Kudu Maso Yammacin Mogadishu August 4, 2025 Pakisatan: Iran Ce Madogara Ga Al-ummar Musulmi August 4, 2025 Wakilin Hukumar FAO A Iran Yace Sauyin Yanayi Ya shafi Dukkan Yankin August 4, 2025 Malamai A Najeriya Suna Goyon Bayan Iran A Yadda Take Fuskantar HKI August 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Iran Ko Da Zata Sake Tattaunawa Da Amurka Zata Kasance Dauke Da Makamai Cikin Shirin
Mashawarcin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ya bayyana cewa: Za su koma shawarwari da Amurka ne yayin da suke dauke da makamai a hannu
Mai baiwa ministan harkokin wajen Iran shawara Sa’ed Khatibzadeh, ya jaddada cewa: Iran ba za ta sake amincewa da Amurka kan duk wata tattaunawa da za ta iya yi ba, yana mai cewa makomar yankin ba kamar yadda Amurka da Isra’ila suke zato ba.
A ziyararsa ta farko da ya kai kasar China bayan hare-haren da Amurka da yahudawan sahayoniyya suka kai kan kasar Iran a baya-bayan nan, Khatibzadeh ya yi wata fitacciyar hira da gidan talabijin na Phoenix, inda ya tattauna muhimman batutuwa da suka hada da ci gaban Shirin makamashin nukiliyar Iran, dangantakar shiyya da kasa da kasa, da makomar shawarwari, da dambaruwar yankin, da kuma yiwuwar barkewar wani babban rikici.
Khatibzadeh ya yi ishara da manufofin gwamnatocin Amurka da yahudawan sahayoniyya yana mai cewa: A kodayaushe ana samun karuwar tashin hankali, musamman ma a yayin da bangaren da ke adawa da gwamnatin Amurka da yahudawan sahayoniyya suke, Iran a kodayaushe tana neman zaman lafiya kuma ba ta kaddamar da wani yaki ba tsawon karnonin da suka gabata.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Rahotonni Sun Bayyana Cewa; Agajin Jin kai Da Ake Wurga Ta Sama A Gaza Tamkar Digon Ruwa Ne August 4, 2025 Wa’adin Da Shugaban Amurka Ya Gindaya Na Kawo Karshen Yaki A Ukraine Ya Karato Ba Tare Da Alamun Karewarsa Ba August 4, 2025 Sojojin Somaliya Sun halaka Mayakan Kungiyar Al-Shabab Fiye Da Hamsin A Kudu Maso Yammacin Mogadishu August 4, 2025 Pakisatan: Iran Ce Madogara Ga Al-ummar Musulmi August 4, 2025 Wakilin Hukumar FAO A Iran Yace Sauyin Yanayi Ya shafi Dukkan Yankin August 4, 2025 Malamai A Najeriya Suna Goyon Bayan Iran A Yadda Take Fuskantar HKI August 4, 2025 Shugaban Kasar Lebanon Ya Yi Alkawalin Adalci Ga Wadanda Feshewar Beirut Ta Shafa August 4, 2025 Iran Ta Ce Ba Wani Ma’aikacin Hukumar IAEA A Kasar A Halin Yanzu August 4, 2025 Pezeshkian ya yaba da irin goyon bayan da Pakistan ta baiwa Iran a lokacin yaki August 4, 2025 Bloomberg: FBI ta cire sunan Trump daga Fayilolin badakalar Epstein August 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci