A yau Lahadi ne shugaban kasar Sin Xi Jinping da shugaban kasar Indonesia, Prabowo Subianto suka yi musayar taya juna murnar cika shekaru 75 da kulla huldar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu. Inda shugaba Xi ya ce, yana dora matukar muhimmanci kan raya dangantakar dake tsakanin Sin da Indonesia, kuma a shirye yake ya yi amfani da bikin cika shekaru 75 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu, a matsayin wata dama ta yin aiki tare da shugaba Prabowo, wajen kara zurfafa hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare, da karfafa hadin gwiwa a batutuwan da suka shafi bangarori daban daban bisa manyan tsare-tsare, da ci gaba da inganta al’ummar Sin da Indonesiya mai kyakkyawar makomar bai daya daga dukkan fannoni, kuma bisa yanayin sabon zamani, da kafa misali na hadin kai da amincewa da juna tsakanin manyan kasashe masu tasowa, da zama abin koyi na ci gaban hadin gwiwar bai daya ga kasashe masu tasowa, ta yadda za su ba da gudummawa tare wajen ci gaban dan Adam.

 

A nasa bangaren, Prabowo ya bayyana fatan bangarorin biyu za su ci gaba da zurfafa hadin gwiwa tare da tabbatar da zumunci a tsakanin al’ummomin kasashen biyu, ta yadda za su ba da gudummawa mai kyau ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Cinikin Kasashen Waje na Iran Ya Zarce Dala Biliyan 76.5

Cinikin kasashen waje na kasar Iran a cikin watanni takwas na farko na bana ya kai tan 131,540, wanda darajarsa ta kai dala biliyan 76.5. kwatankwacin tagomashi na kashi 1.53% idan aka kwatanta da bara warhaka.

Bayanin da aka samu daga hukumar kwastam ta Iran ya ce: “A wannan lokacin, an fitar da tan 105,231,000 na kayayyaki daban-daban, wadanda darajarsu ta kai dala biliyan 37, zuwa kasashe daban-daban.

Wannan adadi yana wakiltar karuwar kashi 1.17% idan aka kwatanta da wannan lokacin a shekarar da ta gabata.

A daya bangaren kuma ” Iran ta kara fitar da kayayyaki zuwa ga Kungiyar Tattalin Arziki ta Eurasia (EAEU), kimanin shekaru biyu bayan yarjejeniyar cinikayyar ‘yanci da aka sanya wa hannu tsakanin Tehran da kungiyar ta fara aiki a watan Disamba na 2023, a cewar sabbin bayanai daga Hukumar Kwastam ta Iran (IRICA).

A cewar alkaluman da aka fitar a ranar Asabar, fitar da kayayyaki daga Iran zuwa ga Kungiyar Tattalin Arziki ta Eurasia wadda Rasha ke jagoranta ya kai dala biliyan 1.46 a cikin watanni takwas da suka wuce a ranar 21 ga Nuwamba, 2025, wanda ya nuna karuwar kashi 11% idan aka kwatanta da wannan lokacin a bara.

 Yawan kayayyakin da aka fitar shi ma ya karu da kashi 10%, inda ya kai tan biliyan 3.888 a wannan lokacin.

Jigilar kayayyaki zuwa Rasha ta karu da kashi 12% a darajar kayayyaki da kuma kashi 9% a girman kayayyaki, yayin da fitar da kayayyaki zuwa Belarus ya karu da fiye da kashi 50% tsakanin Afrilu da Nuwamba, a cewar wannan bayanai.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Najeriya :  Sojoji sun kubutar da yan mata 12 da mayakan ISWAP November 30, 2025 An sake zabar Eto’o a matsayin Shugaban Hukumar kwallon kafa ta Kamaru   November 30, 2025 Shugaban Najeriya Ya Mika Sunaye Sabbin Jakadun Kasar su 32 Ga Majalisa Domin Tantancewa November 30, 2025 Hizbullah Ta Bukaci Shugaban Cocin Katolika Na Duniya Yayi Tir Da Hare-haren Isra’ila November 30, 2025 Iran: Kalaman Da Trump Yayi Na Rufe Sararin Samaniyar Kasar Venuzuwela Ya Sabama Doka. November 30, 2025 Shugaban Pakistan Yayi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Laifukan Yaki Da HKI Ke Tafkawa November 30, 2025 MDD Ta Bukaci Isra’ila Da ta Kawo Karshen Mamayar Da Tayi wa Yankunan Falasdinawa November 30, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 163 November 29, 2025 Iran A Shirye Take Ta Maida Martani Mai Kan Kan Duk Wata Barazanar Tsaro   November 29, 2025 Iran Ta Kakkabo Jiragen Yakin HKI Fiye Da 196 A Yakin Kwanaki 12 November 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a
  • Hamas : Isra’ila na jinkirta aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta
  • An Yi Ganawa A Tsakanin Ministocin Harkokin Wajen Turkiya
  • Mutum 6 sun jikkata a rikici manoma da makiyaya a Jigawa
  • Cinikin Kasashen Waje na Iran Ya Zarce Dala Biliyan 76.5
  • Muna buƙatar taimakon ƙasashen waje kan tsaro a Najeriya — Obasanjo
  • Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe
  • Portugal ta lashe Kofin Duniya na ’yan ƙasa da shekaru 17 a karon farko
  • Palasdinu: Kwamandoji Biyu Na Rundunar “Sarayal-Quds” Sun Yi Shahada A Yammacin Kogin Jordan
  • Limamin Tehran: Hadin Kai Ne Sakamakon Imani Da Ayyukan Kwarai Ne