A yau Lahadi ne shugaban kasar Sin Xi Jinping da shugaban kasar Indonesia, Prabowo Subianto suka yi musayar taya juna murnar cika shekaru 75 da kulla huldar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu. Inda shugaba Xi ya ce, yana dora matukar muhimmanci kan raya dangantakar dake tsakanin Sin da Indonesia, kuma a shirye yake ya yi amfani da bikin cika shekaru 75 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu, a matsayin wata dama ta yin aiki tare da shugaba Prabowo, wajen kara zurfafa hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare, da karfafa hadin gwiwa a batutuwan da suka shafi bangarori daban daban bisa manyan tsare-tsare, da ci gaba da inganta al’ummar Sin da Indonesiya mai kyakkyawar makomar bai daya daga dukkan fannoni, kuma bisa yanayin sabon zamani, da kafa misali na hadin kai da amincewa da juna tsakanin manyan kasashe masu tasowa, da zama abin koyi na ci gaban hadin gwiwar bai daya ga kasashe masu tasowa, ta yadda za su ba da gudummawa tare wajen ci gaban dan Adam.

 

A nasa bangaren, Prabowo ya bayyana fatan bangarorin biyu za su ci gaba da zurfafa hadin gwiwa tare da tabbatar da zumunci a tsakanin al’ummomin kasashen biyu, ta yadda za su ba da gudummawa mai kyau ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC ta tsare Malami kan binciken kuɗaɗen Abacha

Hukumar EFCC ta tsare tsohon Antoni-Janar na Tarayya, Abubakar Malami, saboda binciken da ya shafi dawo da wani ɓangare na kuɗaɗen Abacha.

Hukumar ta kira Malami a makon da ya gabata, inda ta yi masa tambayoyi kan wani bincike da ta ke inda ta sake shi daga bisani, amma yanzu ta tsare shi.

Real Madrid  za ta ɓarje gumi da Manchester City a Santiago Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro

Malami ya ce bai aikata komai ba, kuma ba shi da alaƙa da abin da ake zargi.

A cikin wata sanarwa, ya ce: “Ba a taɓa zargina, gayyata ko bincikena game da tallafa wa ta’addanci ba. Duk wani yunƙuri na danganta ni da irin wannan laifi ƙarya ne.”

Ya ƙara da cewa rahotannin kafofin yaɗa labarai ke watsawa sun yi masa mummunar fassara.

“Ba daidai ba ne a ce aikina na gwamnati ya zama hujja ta tallafa wa ta’addanci. A lokacin aikina, na yi aiki tuƙuru wajen ƙarfafa yaƙi da ta’addanci, ba goyon bayansa ba.”

EFCC ba ta fitar da wata sanarwa kan tsare Malami ba.

Haka kuma bai wallafa komai a shafukan sada zumunta ba tsawon kwanaki huɗu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5 
  • EFCC ta tsare Malami kan binciken kuɗaɗen Abacha
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • Ganawa A Tsakanin Mataimakan Ministocin Waje Na Kasashen Saudiyya, China Da Minista Arakci Na Iran
  • Saudiya da Qatar Zasu Gina Layin Dogo Mai Sauri Tsakanin Kasashen Biyu
  • Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan  Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko  Da  ‘Yan Ta’adda
  •  Kasashen Iran Da Turkiya Za Su Bunkasa Alakarsu A Fagen Ilimi Da Musayar Fasaha
  • Kasashen Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Duk Wani Rikici
  • Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima Ya Isa Abidjan Wajen Rantsar da Shugaba Ouattara
  • Sabon Fada Ya Barke A Tsakanin Thailand Da Cambodia