Xi Da Prabowo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Indonesiya
Published: 13th, April 2025 GMT
A yau Lahadi ne shugaban kasar Sin Xi Jinping da shugaban kasar Indonesia, Prabowo Subianto suka yi musayar taya juna murnar cika shekaru 75 da kulla huldar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu. Inda shugaba Xi ya ce, yana dora matukar muhimmanci kan raya dangantakar dake tsakanin Sin da Indonesia, kuma a shirye yake ya yi amfani da bikin cika shekaru 75 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu, a matsayin wata dama ta yin aiki tare da shugaba Prabowo, wajen kara zurfafa hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare, da karfafa hadin gwiwa a batutuwan da suka shafi bangarori daban daban bisa manyan tsare-tsare, da ci gaba da inganta al’ummar Sin da Indonesiya mai kyakkyawar makomar bai daya daga dukkan fannoni, kuma bisa yanayin sabon zamani, da kafa misali na hadin kai da amincewa da juna tsakanin manyan kasashe masu tasowa, da zama abin koyi na ci gaban hadin gwiwar bai daya ga kasashe masu tasowa, ta yadda za su ba da gudummawa tare wajen ci gaban dan Adam.
A nasa bangaren, Prabowo ya bayyana fatan bangarorin biyu za su ci gaba da zurfafa hadin gwiwa tare da tabbatar da zumunci a tsakanin al’ummomin kasashen biyu, ta yadda za su ba da gudummawa mai kyau ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Jonathan ya dawo Najeriya bayan juyin mulki ya ritsa da shi a Guinea-Bissau
Tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya dawo Najeriya bayan juyin mulkin sojoji ya ritsa da shi a ƙasar Guinea-Bissau inda ya je sa ido kan zaben ƙasar.
Jonathan ya isa filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja da yammacin Alhamis, kusan kwana biyu bayan sojoji sun karɓi mulki a ƙasar da ke yammacin Afirka.
Ya kamata ’yan majalisar Najeriya su koma zaman wucin gadi – Ndume An janye ’yan sanda 11,566 daga yi wa manyan mutane rakiya – EgbetokunYa isa filin jirgin sama na Abuja a cikin jirgin gwamnatin Guinea-Bissau, inda tawagar magoya baya da jami’an gwamnati suka tarbe shi.
Tsohon shugaban kasar ya je Guinea-Bissau ne don sa ido kan zaben shugaban kasa da na majalisar dokoki a matsayin shugaban tawagar sa ido ta dattawan Afirka ta Yamma.
Tawagarsa, tare da ta Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) da Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), suna ci gaba da aikinsu lokacin da sojoji suka yi juyin mulki a Guinea-Bissau.
Wannan lamari ya bar tsohon shugaban kasar tare da sauran mambobin tawagar masu sa ido cikin rashin tabbas da damuwa kan lafiyar su.
Sai dai ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta bayyana cewa tsohon shugaban kasa yana cikin koshin lafiya kuma ya bar Guinea-Bissau.
“Tsohon shugaban kasa Goodluck Ebele Jonathan yana cikin koshin lafiya kuma ya fita daga Guinea-Bissau,” in ji mai magana da yawun ma’aikatar, Kimiebi Ebienfa.
“Ya tafi ne da jirgi na musamman tare da mambobin tawagarsa, ciki har da Ibn Chambas.”
Sojojin Guinea-Bissau sun ƙwace iko da ƙasar a ranar Laraba, inda suka dakatar da tsarin zaben ƙasar tare da rufe iyakokinta, kwanaki bayan gudanar da zaben shugaban kasa da na majalisar dokoki.
Bayan juyin mulkin, shugaban ofishin soja na fadar shugaban kasa, Janar Denis N’Canha, ya ce kwamitin da ya ƙunshi dukkan sassan sojoji, ya karɓi jagorancin ƙasar har zuwa lokacin da za a bayar da sanarwa ta gaba.
Sojojin sun kuma kama shugaban kasar Umaro Embalo, wanda ake ganin zai iya lashe zaben na ranar Lahadi.
Kwana ɗaya bayan juyin mulkin, sojojin sun nada shugaban hafsoshin rundunar sojoji, Janar Horta N’Tam, a matsayin sabon shugaban ƙasar na na riƙon ƙwarya.
Zai jagoranci ƙasar na tsawon shekara guda.