Xi Da Prabowo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Indonesiya
Published: 13th, April 2025 GMT
A yau Lahadi ne shugaban kasar Sin Xi Jinping da shugaban kasar Indonesia, Prabowo Subianto suka yi musayar taya juna murnar cika shekaru 75 da kulla huldar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu. Inda shugaba Xi ya ce, yana dora matukar muhimmanci kan raya dangantakar dake tsakanin Sin da Indonesia, kuma a shirye yake ya yi amfani da bikin cika shekaru 75 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu, a matsayin wata dama ta yin aiki tare da shugaba Prabowo, wajen kara zurfafa hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare, da karfafa hadin gwiwa a batutuwan da suka shafi bangarori daban daban bisa manyan tsare-tsare, da ci gaba da inganta al’ummar Sin da Indonesiya mai kyakkyawar makomar bai daya daga dukkan fannoni, kuma bisa yanayin sabon zamani, da kafa misali na hadin kai da amincewa da juna tsakanin manyan kasashe masu tasowa, da zama abin koyi na ci gaban hadin gwiwar bai daya ga kasashe masu tasowa, ta yadda za su ba da gudummawa tare wajen ci gaban dan Adam.
A nasa bangaren, Prabowo ya bayyana fatan bangarorin biyu za su ci gaba da zurfafa hadin gwiwa tare da tabbatar da zumunci a tsakanin al’ummomin kasashen biyu, ta yadda za su ba da gudummawa mai kyau ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Motar tifa ta murƙushe ɗalibai biyu har lahira a Bayelsa
Wasu mutum biyu da ake zargin ɗaliban jami’a ne a Jihar Bayelsa sun mutu bayan wata mota ƙirar tifa ta murƙushe su lokacin da suke kan babur mai ƙafa uku a kan hanyar Tombia zuwa Ammassoma.
Daily Trust ta samu rahoton cewa haɗarin wanda ya afku a ranar Talata, ya kuma sa wasu fasinjojin da ke cikin babur ɗin sun samu munanan raunuka.
Akwai buƙatar samar da sauyin zaman lafiya mai ɗorewa — Maryam Bukar An kama mai babur ɗauke da ƙoƙunan kan mutane a OgunA cewar wasu mazauna yankin, haɗarin ya afku ne a kusa da wani lanƙwasa mai haɗarin gaske a kan babbar hanyar, sakamakon rashin kyan hanyar da kuma gudun wuce ƙima.
Sun ce babbar motar tifa na gangarowa kan tudu cikin sauri lokacin da ta ƙwacewa direban ta kuma afka kan babur ɗin.
Wani ɗan kasuwa mai suna Godspower Okolo, ya shaida wa manema labarai cewa direban tifa ɗin yana tafiya da sauri, kuma a lokacin da ya yi yunƙurin karkatar da motar abin ya citura.
Ya ce, “Keke (Babur mai ƙafa uku) ba ta da damar kaucewa hatsarin, domin kuwa tifa ɗin ta riga ta yi kusa da shi, mun yi ta ƙorafin yadda direbobin manyan motocin dakon kaya suke yi a wannan hanyar tsawon shekaru, amma babu abin da ya canza.
“Haɗarin ya sa babur ɗin ya lalace ba tare da an gane fasinjojin cikin ba, wasu masu jinƙai ne suka garzaya wurin da lamarin ya faru, inda suka kwashe waɗanda suka tsira daga haɗarin tare da kai waɗanda suka jikkata zuwa cibiyar lafiya ta tarayya da ke Yenagoa, daga baya aka kwashe gawarwakin waɗanda suka mutu zuwa ɗakin ajiye gawa na kusa.
“Wannan lamarin ya sake sabunta kiraye-kirayen a tsaurara matakan tsaro, ya kamata hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) da rundunar ’yan sanda ta jihar su ƙara yin sintiri, da ɓullo da na’urorin hana gudu, da kuma gudanar da binciken ababan hawa kan manyan motoci,” in ji shi.
Kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Bayelsa, DSP Musa Muhammad, ya tabbatar da faruwar haɗarin, inda ya ƙara da cewa ana ci gaba da gudanar da bincike domin gano musabbabin haɗarin motar.