Aminiya:
2025-11-03@06:21:38 GMT

Gwamnatin Kano ta karɓi rahoton binciken Kwamishinan da ya yi belin Danwawu

Published: 4th, August 2025 GMT

Gwamnatin Kano ta karɓi rahoton kwamitin bincike da ta kafa domin gano haƙiƙanin gaskiya kan zargin da ake yi wa Kwamishinan Sufuri na jihar, Ibrahim Ali Namadi da shiga sha’anin belin wani da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi.

Shugaban kwamitin, Barista Aminu Hussain, ne ya miƙa rahoton ga Sakataren Gwamnatin Kano, Alhaji Umar Farouk Ibrahim, a ranar Litinin, inda ya bayyana cewa sun gudanar da cikakken bincike na adalci, tare da tuntubar dukkan masu ruwa da tsaki.

WAEC ta saki sakamakon jarabawar 2025 Za a mayar da gidan yarin da ya haura shekara 100 zuwa gidan tarihi a Kano

Babu dai cikakken bayanin abin da rahoton ya ƙunsa, to sai dai matakin da gwamnati za ta ɗauka ne zai fayyace abin da kwamitin ya gano a binciken nasa.

“Mun tattauna da shi kansa kwamishinan, wanda ya gabatar mana da bayanai har a rubuce. Haka kuma, mun ga cewa akwai buƙatar mu tattauna da Abubakar Umar Sharada, mai taimaka wa Gwamna kan sha’anin siyasa, da kuma Musa Ado Tsamiya, mataimakin gwamnan kan kula da magudanan ruwa,” in ji Barista Hussain yayin miƙa rahoton.

Ya ce kwamitin ya yi zurfin nazari tare da neman shawara daga hukumomi da dama ciki har da Hukumar Tsaro ta SSS, da takwararta ta hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi NDLEA da kuma Kungiyar Lauyoyi ta Nijeriya (NBA), domin tabbatar da sahihancin rahoton da kwamitin ya fitar.

“Mun samu duk kwafin takardun da suka shafi batun a hukumance kamar yadda doka ta tanada. Mun yi amfani da duk wata shaida da ke akwai kuma mun tsaya kan gaskiya da adalci a yayin bincikenmu,” in ji shi.

Barista Hussain ya yaba wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa yadda ya bar kwamitin ya gudanar da aikin sa ba tare da tsoma baki ba, yana mai cewa hakan alama ce ta gaskiya da kiyaye doka da oda a tafiyar da mulki.

“Muna godiya ga Gwamna saboda yadda ya bai wa kwamitin dama ya yi aikinsa ba tare da wani tsoro ko son rai ba,” ya ƙara da cewa.

Da yake karɓar rahoton a madadin gwamnati, Sakataren Gwamnatin, Alhaji Umar Farouk Ibrahim, ya yaba wa kwamitin bisa irin ƙwazon da suka nuna.

“Zan fara da miƙa godiya ta musamman ga shugaban kwamitin, Barista Aminu Hussain, da sauran mambobin kwamitin bisa jajircewa da ƙwarewa da kuka nuna a wannan muhimmin aiki da ya ɗauki hankalin jama’a,” in ji shi.

Ya kara da cewa, “Duk da cewa akwai matsin lamba da aka riƙa fuskanta daga bangarori daban-daban, kwamitin ya tsaya kai da fata a kan gaskiya.

“Kowa ya shaida cewar wannan kwamitin ya yi aiki da amana. Kuma ba tare da bata lokaci ba, zan miƙa wannan rahoto ga Mai Girma Gwamna domin ya duba ya kuma ɗauki matakin da ya dace.”

Dalilin binciken

Ana iya tuna cewa a watan Yulin da ya gabata ne rahotanni suka bayyana cewa Kwamishinan Sufuri na Kano, Ibrahim Namadi, ya tsaya a matsayi mai karbar belin wani da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi — Sulaiman Aminu Danwawu — a kotu.

Bayanai sun ce a watan Mayun da ya gabata ne aka kama Danwawu a unguwar Tudun Yola da ke Kano, sannan aka mika shi ga hukumar NDLEA.

An gurfanar da shi gaban Kotun Tarayya a Kano a ranar 28 ga Mayu bisa tuhuma kan mallakar da kuma mu’amala da haramtattun ƙwayoyi.

A ranar 16 ga Yuli, wata kotu a Kano ta bayar da belin Danwawu bisa sharadin biyan Naira miliyan uku da kuma samun kwamishina mai ci a matsayin wanda tsaya masa, inda Kwamishina Namadi ya gabatar da rantsuwar cewa shi ne zai tsaya masa, lamarin da ya janyo zazzafar suka daga jama’a.

Daga bisani, a ranar 25 ga Yuli, Namadi ya janye matsayin nasa na mai tsaya masa da hujjar kare mutuncinsa, yana mai cewa bai da wata alaƙa ta kusa ko ta nesa da Danwawu, sai dai kawai ya yarda ne saboda wasu abokai na kusa sun nemi alfarma a madadinsa.

Wannan batun dai ya janyo zazzafar muhawara a ciki da wajen jihar, inda wasu ke ganin bai kamata mutum mai matsayi irin na kwamishina ya karɓi belin mutumin da ake zargi da taimakawa wajen assasa ta’ammali da miyagun ƙwayoyi a jihar.

Lamarin da ya sa wasu ke ta kiraye-kirayen sauke shi daga muƙaminsa.

A nasa martanin, Gwamna Abba Kabir Yusuf wanda ya amsa kiraye-kirayen jama’a ya kafa wani kwamitin mutum bakwai ƙarƙashin jagorancin Barista Aminu Hussain, domin bincikar gaskiyar lamari da ba da shawarar matakin da ya dace.

Abba ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na yaƙi da safarar da shan miyagun ƙwayoyi, tare da nanata cewa gwamnati ba za ta lamunci duk wani hawan ƙawara da wani jami’in gwamnati zai yi wa doka ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ibrahim Ali Namadi Jihar Kano Sulaiman Aminu Danwawu miyagun ƙwayoyi kwamitin ya

এছাড়াও পড়ুন:

Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka

Wasu lauyoyi biyu a Najeriya sun gargaɗi Gwamnatin Tarayya da ta yi taka-tsantsan wajen yin hulɗa da ƙasar Amurka, inda suka ce maganganun Amurka a kan Najeriya abun ruɗarwa ne 

Babban lauyan nan, Cuf Okoi Obono-Obla, wanda tsohon mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara ne, ya zargi Amurka da son raba kan ’yan Najeriya da sunan kare Kiristoci.

Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 

Ya ce iƙirarin cewa ana yi wa Kiristoci kisan gilla a Najeriya ƙarya ne face nufin tayar da hankali da kawo rikici.

“Najeriya ba ta taɓa zama barazana ga zaman lafiyar duniya ba,” in ji Obono-Obla.

“Idan Amurka, inda ake yawan harbe mutane a coci-coci, ba ta gayyaci sojojin ƙetare su shigo musu ba, to kamata ya yi ta bar Najeriya ta magance nata matsalolin.”

Ya yi gargaɗin cewa duk wani yunƙurin Amurka na yin katsa-landan cikin harkokin Najeriya zai zama take doka da tauye ikon ƙasa.

Shi ma Barista Leonard Anyogo, kuma shugaban ƙungiyar ‘Good Governance Advocacy International’, ya shawarci Najeriya da ta bi hanyoyin diflomasiyya wajen mayar wa Amurka martani ba da faɗa ba.

“Ya kamata mu tattauna, ba mu yi fada ba,” in ji Anyogo.

“Najeriya ta nemi haɗin kai da Amurka a fannin tsaro da diflomasiyya domin kare muradunta.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
  • Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda