Rundunar sojin kasar Sin (PLA) ta yi sintiri a yankin tekun kudancin Sin daga ranar 3 zuwa 4 ga wata.

Kakakin rundunar PLA ta kudancin kasar Tian Junli ya bayyana a yau Litinin cewa, kasar Sin ta dauki matakin ne biyo bayan matakan Philippines na sanya kasashen dake wajen yankin cikin abun da ta kira da sintirin hadin gwiwa, wanda ke neman lalata zaman lafiya da kwanciyar hankalin yankin.

A cewarsa, dakarun rundunar ta kudancin kasar za su ci gaba da kasancewa cikin shirin ko-ta-kwana da kare ikon kasar kan yankunanta da muradunta na teku ba tare da yin kasa a gwiwa ba, yana mai cewa za a dakile duk wani matakin soja dake nemen tada hankali da rikici a yankin. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An kama dilallan ƙwaya 28 a cikin barikin sojoji a Kaduna

Sojoji sun kama wani gungun dillalan miyagun ƙwayoyi 28 a cikin Babban Barikin Sojoji na Jaji da ke Jihar Kaduna.

Dilolin ƙwayar da aka kama sun haɗa da mata 11 da maza 18, lamarin da ya haifar da fargaba gane da yaɗuwar ɗabi’ar ta’ammali da miyagun ƙwayoyi a tsakanin iyalan sojoji da fararen hula da ke makwabtaka da su.

Kakakin Cibiyar Horas da Mayaƙan Ƙasa da aka barikin, Kyaftin Olusegun Abioye, ya bayyana cewa sojoji sun gano cibiyar dilolin ƙwayar ne a unguwanni Railway da Unguwar Lauya da ke cikin harabar barikin na Jaji.

Ya ƙara da cewa an kama shugabannin masu fataucin miyagun ƙwayoyi guda aƙalla guda 15 a waɗannan unguwanni biyu, kuma an miƙa duk waɗanda aka kama ga Hukumar Yaƙi da Ta’ammali da Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA).

NAJERIYA A YAU: Yadda Talauci Ke Hana Shayar Da Yara Nonon Uwa Zalla A Najeriya Sojoji sun ceto malamin Jami’a da aka sace a Taraba

Ya bayyana haka ne a yayin rangadin da ya jagoranci manema labarai yana mai ƙaryata labaran da ke cewa sojoji sun rusa unguwannin biyu.

Kyaftin Olusegun Abioye ya ƙara da cewa duk da cewa yankunan irinsu Unguwar Alasan da Unguwar da Unguwar Alhaji da Unguwar Aboki, da ke cikin harabar barikin suna taimaka wa sojoji da wasu ayyuka; amma duk da haka suna addabar al’ummar barikin sojojin da wasu matsaloli.

Ya bayyana cewa unguwanni sun riga sun haɗe da barikin sojojin wanda babbar cibiyar horon soji ce, kuma kusancin nasu kan jefa mazaunansu cikin mummunan haɗari a lokacin da sojoji ke atisayen amfani manyan makamai.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet
  • Kasar Iran Ko Da Zata Sake Tattaunawa Da Amurka Zata Kasance Dauke Da Makamai Cikin Shirin
  • Wakilin Hukumar FAO A Iran Yace Sauyin Yanayi Ya shafi Dukkan Yankin
  • Rasha da China sun fara wani gagarumin atisayen soji na hadin gwiwa a tekun Japan
  • An kama dilallan ƙwaya 28 a cikin barikin sojoji a Kaduna
  • Iran Ta Jaddada Cewa: Karfin Makamai Masu Linzami Da Jiragen Sama Marasa Matuka Ciki Suna Nan Cikin  Shiri
  • Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin
  • Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya
  • Iran ta yi gargadi game da makirce-makircen Isra’ila na kawo cikas ga tsaron yankin