Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya amince da ware Naira Biliyan 20 a karin kasafin kudin da aka yi domin ci gaba da gyaran gine-ginen makarantu a fadin jihar.

A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Ilimi na jihar, Dr. Lawal Olohungbebe, ya fitar, ya ce wannan sabon tsarin zai kara karfi wajen cigaban gyaran makarantun gwamnati.

Sanarwar ta bayyana cewa tuni aka fara aikin, inda aka  zayyana yadda gine-ginen za su kasance, kuma sauran abubuwa za su biyo baya da zaran an amince da karin kasafin kudin.

Sanarwar ta kara da cewa wannan ba wani aiki ne mai zaman kansa ba, illa wata sabuwar babbar gudummawa daga gwamnati don kara habaka aikin da take yi tun da farko.

Ta kara da cewa gwamnatin ta gyara sama da ajujuwa 1,254 banda wasu muhimman ayyukan gyara da aka gudanar a wurare daban-daban.

Gwamnatin ta bayyana jin dadinta kan aiwatar da ayyukan gyaran makarantu na SUBEB-UBEC tun daga shekarar 2014.

Sanarwar ta ce wannan sabuwar gudummawar za ta hada da dakunan gwaje-gwaje da wuraren tsafta a makarantun da ke sassa daban-daban na jihar, domin cike gibi tare da kara karfafa ayyukan da SUBEB ke yi.

“Duk da irin manyan ayyukan da muka gudanar, muna sane da cewa har yanzu akwai gibin da ake bukatar cikewa, kuma wannan ne dalilin da ya sa Mai Girma Gwamna ya amince da wannan sabon matakin na musamman don rage gibin da ke cikin gine-ginen makarantu,” In ji sanarwar.

 

Ali Muhammad Rabi’u

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara Makarantu

এছাড়াও পড়ুন:

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Bugu da ƙari, Hukumar ta NPA ta bayyana cewa, tana kan ƙoƙarin inganta kayan aiki Tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar, wanda ta zuba dala biliyan daya, domin fara gyaran Tashoshin Jiragen Ruwa ta Tin Can Island tare da yin ayyukan kwakwarima, a Tashoshin Jiragen Ruwa na, Apapa, Riɓers, Onne, Warri da kuma Kalaba.

Ita kuwa a na ta ɓangaren, Kwalejin ta MAN ta bayyana cewa, nauyin da aka ɗora mata na gudanar da ayyukan ta, son yi daidai da ƙoƙarin ƙasar nan ke ci gaba da yi, na ƙara haɓaka tattalin arzikin ƙasar, mussaman wajen yaye haziƙai kuma ƙwararrun ɗirebobin Jiragen Ruwa da ƙasar nan ke buƙata.

Shugaban Hukumar ta NPA darka Abubakar dantsho, a jawabinsa ewabinsa a taron shekara- shekara na ƙasa na shekarar 2025 na  ƙungiyar ƴanjarida da ke dauko rahotabin da suka shafi fannin ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa wato AMJON ta gudanar a dakin taro na otel ɗin Sheraton Hotel da ke a, Ikeja a jihar LegasLegas, ya bayyana cewa, Hukumar ta NPA,  na kan gudanar da aikin fadada Sabbin Tashoshin Jiragen Ruwa na Snake Island, Badagry ɗeep Seaport, Ondo ɗeep Seaport da kuma ta,  Burutu wadanda daukacin aikin, a yanzu suka kai matakin kammalawakammalawa

dantsho wanda  Babbar Manajar  huɗda da Juma’a a Hukumar ta NPA Hadiza Usman Shu’aibu ta wakilce shi a wajen taron ya bayyana cewa, Hukumar ta NPA, ta mayar da hankali wajen ganin tana ƙara daga nartabar kayan aikinta da ke a daukacin Tashoshin Jiragen Ruwa na ƙasar,mussaman ta hanyar sanya masu kayan aiki na zamani, domin a rinƙa Kula da saukar Jiragen Ruwa da ƙara janyo masu zuba hannun jari, a fannin.

Shugaban ya ci gaba da cewa, a yanzu haka, Nijeriya ta samu samar shiga cikin ƙungiyar ƙasa da ƙasa ta Kula da tsara Tashoshin Jiragen Ruwa wato IPCSA wanda ya samar da cewa, wannan shigar ta Nijeriya cikin ƙungiyar, zai bai wa Nijeriya damar wanzar da tsarin NSW wanda aka samar da shi, bisa nufin saita ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa da kuma rage ƙalubalen da ake fuskanta ta hada-hadar kasuwanci.

Kazalika, dantsho ya bayyana cewa, Hukumar ta NPA, ta samu nasarar rage ƙalubalen cunkodon ababen hawa da ake fuskanta a  Tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Shirin Dashe Itatuwa Don Yaki da Matsalolin Muhalli
  • Gwamnan Jihar Kwara Ya Hori Sabbin Matasa Masu Yiwa Kasa Hidima Akan Kishin Kasa
  • Gwamnatin Sakkwato Za Ta Kashe fiye da Naira Miliyan 200 Wajen Gyara Tashar Talabijin Ta Kasa NTA
  • Gwamna Abdulrazaq Ya Duba Titi Mai Tsawo Kilomita 49
  • Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙura
  • IRGC Tace Bata Amince Da Kasashen Biyu A Kan Kasar Falasdinu Ba
  • Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12
  • Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50
  • Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa