Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-04@03:17:33 GMT

An Zargin Akantan jihar Nasarawa Da Shiga Harkokin Siyasa

Published: 5th, August 2025 GMT

An Zargin Akantan jihar Nasarawa Da Shiga Harkokin Siyasa

Kungiyar masu fafutukar tabbatar da zaman lafiya da kishin kasa reshen jihar Nasarawa ta kalubalanci kungiyar tabbatar da gaskiya da rikon amana da shugabanci na gari (NS-TA&G), da su tabbatar da zargin nuna son kai wajen sauke nauyin da babban Akanta Janar na jihar, Ahmed Musa Mohammed ke yi.

 

Ko’odinetan kungiyar na jiha Abimiku Dangana Solomon ne ya bayyana hakan a lokacin da yake mayar da martani ga wani jawabi da Mista Lazarus Salaki, ko’odinetan kungiyar NS-TA&G2 na jihar ya yi a wani taron manema labarai da aka gudanar a garin Lafia babban birnin jihar.

 

Mista Abimiku Dangana ya ce, hukuncin da kotun koli ta yanke na baya-bayan nan bai hana masu rike da mukaman gwamnati da ma’aikatan gwamnati shiga harkokin siyasa da shiga jam’iyyun siyasa ba.

 

Kungiyar ta kuma bayyana cewa, shari’ar INEC  da Ahmed Musa inda mai shari’a Ayoola da Justice Mohammad Uwais suka jaddada cewa dokokin ma’aikatan ba za su iya maye gurbin tanadin tsarin mulki ba.

 

“Muna kalubalantar Hukumar NS-TA&G2 da ta ba da shaidar nuna fifiko na musamman da ake zargin an yi mata ko kuma an yi kasa a gwiwa wajen sauke nauyin da Akanta Janar na Jiha ke yi.

 

Idan za a iya tunawa wata kungiyar da abin ya shafa a karkashin Mista Lazarus Salaki, ta yi kira ga Mista Musa Ahmed Mohammed, Akanta Janar na Jihar Nasarawa ya yi murabus, bisa zarginsa da hannu a harkokin siyasa yayin da yake rike da wani mukami mai muhimmanci.

 

Kungiyar ta kuma bayar da misali da umarnin da tsohon sakataren gwamnatin jihar, Mohammed Uban-doma Aliyu ya bayar a ranar 16 ga Afrilu, 2024, inda ya umurci duk masu rike da mukaman siyasa masu burin shiga zabe da su yi murabus ko kuma su dakatar da harkokin siyasa har sai Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa INEC ta bayyana matsayarta.

 

Mista Lazarus Salaki ya yi zargin cewa, duk da wannan umarnin, wasu da aka nada sun ci gaba da yakin neman zabe da kuma gudanar da taron siyasa yayin da suke kan mukamansu.

 

COV/Aliyu Muraki/Lafia.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: nasarawa

এছাড়াও পড়ুন:

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

 

Ban da haka, shugaban na Sin ya ce, kasarsa na son yin kokari tare da bangarori daban daban, wajen aiwatar da ra’ayin raya kasa na kirkiro sabbin fasahohi, da tabbatar da daidaito, da kare muhalli, da bude kofa, gami da haifar da alfanu ga kowa, ta yadda za a kafa wata al’ummar bai daya ta yankin Asiya da na tekun Pasifik.

 

Duk a wajen taron, yayin wani bikin mika damar karbar bakuncin taron kungiyar APEC, shugaba Xi Jinping ya sanar da cewa, kasar Sin za ta karbi bakuncin kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar APEC karo na 33, wanda ake sa ran gudanar da shi a birnin Shenzhen na kasar Sin a watan Nuwamba na shekarar 2026. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka October 31, 2025 Daga Birnin Sin Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Likitocin Kasar Sudan: Rundunar RSF Tana Garkuwa Da Dubban Fararen Hula A Al-Fasha
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
  • Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A