Iran Zata Yaye Labulen Ire-Iren Makamanta Na Musamman Da Ta Mallaka Domin Kare Kai
Published: 13th, April 2025 GMT
Kwamandan rundunar sojojin kasa ta Iran ya bayyana cewa: Nan ba da jimawa ba za a yaye labulen ire-iren makamai na musamman da Iran ta mallaka
Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran Birgediya Janar Kiomars Heidari ya yi nuni da shirin rufe kan iyakar kasar da ke gabashin Iran, yana mai cewa: Wannan ba kawai wata katanga ba ce mai tsayin mita 4, saboda an tanadar da ita ce da nau’o’in makamai masu kwaloluwar ci gaba na zamani a duniya, wannan shiri an gudanar da shi ne tsawon shekaru hudu kuma za a kammala shi nan da shekaru uku masu zuwa.
Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran ya jaddada haka ne a wani taron manema labarai da ya gudanar a yau Lahadi cewa, yana mai cewa; An bullo da sauye-sauye ne ga tsarin rundunar sojojin kasa baki daya, don ba da damar wuce tsohon tsari saboda kai wa ga tsari na zamani da zai iya tunkarar kalubalen da ake fuskanta a yau.
Birgediya Janar Haidari ya yi jawabi kan muhimman sauye-sauye a cikin tsari da makaman da sojojin kasa suka samar, yana mai cewa, “Sun mayar da bukatu na yau da kullum zuwa wani rundunar kai hari cikin gaggawa mai saurin mayar da martani.
Ya kara da cewa, “Wannan runduna ta mallaki karfin motsawa 100%, da karfin kai hari 100%, da kuma juriya 100%. Don cimma wannan buri, suna bukatar makamai na musamman wadanda ke dauke da wadannan siffofi guda biyu.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku
Amurka ta bayyana dalilin sabunta manufofin, tare da lura da cewa “an tsara sharuddan bizar Amurka da ka’idoji domin kare tsarin shige da fice na Amurka.”
Ofishin jakadancin ya kara da cewa “wadannan ka’idoji sun dogara ne kan ma’aunin fasaha da tsaro na duniya.”
A cewar ofishin jakadancin Amurka yana aiki tare da hukumomin Nijeriya domin cimma wadannan matakan.
Sanarwar ta ce “Tawagar Amurka tana aiki tare da gwamnatin Nijeriya domin tabbatar da cewa Nijeriya za ta iya cika sharuddan.”
Misalin wannan sabon tsari ya hada da “Takardun tafiye-tafiye masu aminci: tabbatar da cewa kasashe suna ba da amintattun takaddun balaguro tare da ingantattun bayanan matafiyi, Kada aikin gudanar da Bisa ya wuce lokacin da aka dauka:.”
Duk da sabbin takunkumin, ofishin jakadancin ya sake jaddada alakar diflomasiyya da Nijeriya.
Sanarwar ta kara da cewa, “Amurka na mutunta dangantakarta da Nijeriya da dadewa, kuma tana ci gaba da jajircewa wajen fadada hadin gwiwarmu bisa mutunta juna, da muhimman batutuwan tsaro, da damar tattalin arziki, tare da tabbatar da tsaron kasashen biyu.”
Har ila yau, ofishin jakadancin ya nuna goyon bayansa ga sauye-sauyen da Nijeriya ke ci gaba da yi, inda ta ce, “Mun yaba da kokarin da hukumomin shige da fice da na tsaro na gwamnatin Nijeriya ke yi na ganin sun cika ka’idoji kyawawan ayyuka na kasa da kasa.”
An shawarci matafiya na Nijeriya da su bi ka’idojin bizar.
“An bukaci matafiya ‘yan Nijeriya da su mutunta tare da kiyaye sharuddan bizarsu, kuma su tabbatar da ingantattun takaddun balaguro, kuma na zamani.”
Ofishin jakadancin ya karkare da jaddada huldarsa da jama’a da gwamnatin Nijeriya.
“Amurka ta kasance amintacciya a cikin zurfafa dangantakar jama’a da Nijeriya ta hanyar kasuwanci, ilimi da mu’amalar al’adu.
“Muna fatan ci gaba da hadin gwiwa a dukkan matakai tare da jama’ar Nijeriya da jami’an gwamnati don tabbatar da tafiya cikin aminci da doka tsakanin Amurka da dukkan kasashe,” in ji ta.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp