Iran Zata Yaye Labulen Ire-Iren Makamanta Na Musamman Da Ta Mallaka Domin Kare Kai
Published: 13th, April 2025 GMT
Kwamandan rundunar sojojin kasa ta Iran ya bayyana cewa: Nan ba da jimawa ba za a yaye labulen ire-iren makamai na musamman da Iran ta mallaka
Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran Birgediya Janar Kiomars Heidari ya yi nuni da shirin rufe kan iyakar kasar da ke gabashin Iran, yana mai cewa: Wannan ba kawai wata katanga ba ce mai tsayin mita 4, saboda an tanadar da ita ce da nau’o’in makamai masu kwaloluwar ci gaba na zamani a duniya, wannan shiri an gudanar da shi ne tsawon shekaru hudu kuma za a kammala shi nan da shekaru uku masu zuwa.
Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran ya jaddada haka ne a wani taron manema labarai da ya gudanar a yau Lahadi cewa, yana mai cewa; An bullo da sauye-sauye ne ga tsarin rundunar sojojin kasa baki daya, don ba da damar wuce tsohon tsari saboda kai wa ga tsari na zamani da zai iya tunkarar kalubalen da ake fuskanta a yau.
Birgediya Janar Haidari ya yi jawabi kan muhimman sauye-sauye a cikin tsari da makaman da sojojin kasa suka samar, yana mai cewa, “Sun mayar da bukatu na yau da kullum zuwa wani rundunar kai hari cikin gaggawa mai saurin mayar da martani.
Ya kara da cewa, “Wannan runduna ta mallaki karfin motsawa 100%, da karfin kai hari 100%, da kuma juriya 100%. Don cimma wannan buri, suna bukatar makamai na musamman wadanda ke dauke da wadannan siffofi guda biyu.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Farfesa na Farko a fannin Ilimi a Arewa, Adamu Baikie, ya rasu yana da shekara 94
Allah Ya yi wa Farfesa Adamu Baikie, wanda ya kasance Farfesa na farko a fannin Ilimi daga Arewacin Najeriya, rasuwa.
Farfesa Adamu Bakie ya rasu yana da shekaru 94 ne a daren Jumma’a a gidansa da ke Zariya, Jihar Kaduna.
Babban ɗansa, Manjo Muhammad Adamu (Ritaya), ya tabbatar da rasuwar, inda ya ce za a sanar da jama’a cikakkun bayanai da lokacin da za a gudanar da jana’izarsa daga baya.
Baikie ya shahara sosai wajen gina fannin ilimi a Najeriya, inda ya yi aiki a manyan makarantu da dama.
Kotu ta sa ranar yanke hukunci a Shari’ar Abba Kyari da NDLEA Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kantaYa taɓa zama Shugaban Jami’a a wasu jami’o’in Najeriya, kuma ya jagoranci wata jami’a a Kudancin Afirka a lokacin aikinsa.
An haifi Farfesa Adamu Baikie ne a Wusasa, Zariya a 1931 saidai ya girma ne Sabon garin Kano, inda ya yi karatun firamare kafin daga baya ya dawo makarantar middle a Zaria a shekarar 1948.
Ya zama farfesa na farko a ɓangaren ilmi daga Arewacin Najeriya a 1971.
Ana kallon da a matsayin jigo wajen kafa tsare-tsaren koyar da malamai, tare da samar da gudummawar da ta ɗore a bangaren ilimi na Najeriya.
Ya rasu ya bar ’ya’ya biyar.