Iran Zata Yaye Labulen Ire-Iren Makamanta Na Musamman Da Ta Mallaka Domin Kare Kai
Published: 13th, April 2025 GMT
Kwamandan rundunar sojojin kasa ta Iran ya bayyana cewa: Nan ba da jimawa ba za a yaye labulen ire-iren makamai na musamman da Iran ta mallaka
Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran Birgediya Janar Kiomars Heidari ya yi nuni da shirin rufe kan iyakar kasar da ke gabashin Iran, yana mai cewa: Wannan ba kawai wata katanga ba ce mai tsayin mita 4, saboda an tanadar da ita ce da nau’o’in makamai masu kwaloluwar ci gaba na zamani a duniya, wannan shiri an gudanar da shi ne tsawon shekaru hudu kuma za a kammala shi nan da shekaru uku masu zuwa.
Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran ya jaddada haka ne a wani taron manema labarai da ya gudanar a yau Lahadi cewa, yana mai cewa; An bullo da sauye-sauye ne ga tsarin rundunar sojojin kasa baki daya, don ba da damar wuce tsohon tsari saboda kai wa ga tsari na zamani da zai iya tunkarar kalubalen da ake fuskanta a yau.
Birgediya Janar Haidari ya yi jawabi kan muhimman sauye-sauye a cikin tsari da makaman da sojojin kasa suka samar, yana mai cewa, “Sun mayar da bukatu na yau da kullum zuwa wani rundunar kai hari cikin gaggawa mai saurin mayar da martani.
Ya kara da cewa, “Wannan runduna ta mallaki karfin motsawa 100%, da karfin kai hari 100%, da kuma juriya 100%. Don cimma wannan buri, suna bukatar makamai na musamman wadanda ke dauke da wadannan siffofi guda biyu.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jonathan ya dawo Najeriya bayan juyin mulki ya ritsa da shi a Guinea-Bissau
Tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya dawo Najeriya bayan juyin mulkin sojoji ya ritsa da shi a ƙasar Guinea-Bissau inda ya je sa ido kan zaben ƙasar.
Jonathan ya isa filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja da yammacin Alhamis, kusan kwana biyu bayan sojoji sun karɓi mulki a ƙasar da ke yammacin Afirka.
Ya kamata ’yan majalisar Najeriya su koma zaman wucin gadi – Ndume An janye ’yan sanda 11,566 daga yi wa manyan mutane rakiya – EgbetokunYa isa filin jirgin sama na Abuja a cikin jirgin gwamnatin Guinea-Bissau, inda tawagar magoya baya da jami’an gwamnati suka tarbe shi.
Tsohon shugaban kasar ya je Guinea-Bissau ne don sa ido kan zaben shugaban kasa da na majalisar dokoki a matsayin shugaban tawagar sa ido ta dattawan Afirka ta Yamma.
Tawagarsa, tare da ta Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) da Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), suna ci gaba da aikinsu lokacin da sojoji suka yi juyin mulki a Guinea-Bissau.
Wannan lamari ya bar tsohon shugaban kasar tare da sauran mambobin tawagar masu sa ido cikin rashin tabbas da damuwa kan lafiyar su.
Sai dai ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta bayyana cewa tsohon shugaban kasa yana cikin koshin lafiya kuma ya bar Guinea-Bissau.
“Tsohon shugaban kasa Goodluck Ebele Jonathan yana cikin koshin lafiya kuma ya fita daga Guinea-Bissau,” in ji mai magana da yawun ma’aikatar, Kimiebi Ebienfa.
“Ya tafi ne da jirgi na musamman tare da mambobin tawagarsa, ciki har da Ibn Chambas.”
Sojojin Guinea-Bissau sun ƙwace iko da ƙasar a ranar Laraba, inda suka dakatar da tsarin zaben ƙasar tare da rufe iyakokinta, kwanaki bayan gudanar da zaben shugaban kasa da na majalisar dokoki.
Bayan juyin mulkin, shugaban ofishin soja na fadar shugaban kasa, Janar Denis N’Canha, ya ce kwamitin da ya ƙunshi dukkan sassan sojoji, ya karɓi jagorancin ƙasar har zuwa lokacin da za a bayar da sanarwa ta gaba.
Sojojin sun kuma kama shugaban kasar Umaro Embalo, wanda ake ganin zai iya lashe zaben na ranar Lahadi.
Kwana ɗaya bayan juyin mulkin, sojojin sun nada shugaban hafsoshin rundunar sojoji, Janar Horta N’Tam, a matsayin sabon shugaban ƙasar na na riƙon ƙwarya.
Zai jagoranci ƙasar na tsawon shekara guda.