Kwamandan rundunar sojojin kasa ta Iran ya bayyana cewa: Nan ba da jimawa ba za a yaye labulen ire-iren makamai na musamman da Iran ta mallaka

Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran Birgediya Janar Kiomars Heidari ya yi nuni da shirin rufe kan iyakar kasar da ke gabashin Iran, yana mai cewa: Wannan ba kawai wata katanga ba ce mai tsayin mita 4, saboda an tanadar da ita ce da nau’o’in makamai masu kwaloluwar ci gaba na zamani a duniya, wannan shiri an gudanar da shi ne tsawon shekaru hudu kuma za a kammala shi nan da shekaru uku masu zuwa.

Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran ya jaddada haka ne a wani taron manema labarai da ya gudanar a yau Lahadi cewa, yana mai cewa; An bullo da sauye-sauye ne ga tsarin rundunar sojojin kasa baki daya, don ba da damar wuce tsohon tsari saboda kai wa ga tsari na zamani da zai iya tunkarar kalubalen da ake fuskanta a yau.

Birgediya Janar Haidari ya yi jawabi kan muhimman sauye-sauye a cikin tsari da makaman da sojojin kasa suka samar, yana mai cewa, “Sun mayar da bukatu na yau da kullum zuwa wani rundunar kai hari cikin gaggawa mai saurin mayar da martani.

Ya kara da cewa, “Wannan runduna ta mallaki karfin motsawa 100%, da karfin kai hari 100%, da kuma juriya 100%. Don cimma wannan buri, suna bukatar makamai na musamman wadanda ke dauke da wadannan siffofi guda biyu.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

Bayan hukunci, kwamitin gudanarwa karkashin shugabancin Damagum ta dakatar da sakataren jam’iyyar na kasa, Sanata Samuel Anyanwu da mashawarcin shari’a na kasa, Kamaldeen Ajibade da sakataren shirye-shirye na kasa, Umar Bature na tsawon wata guda saboda zargin ayyukan da ke goyon bayan abin da ya saba wa jam’iyya.

Bayan awanni 24, Anyanwu da magoya bayansa sun hadu a Abuja suka sanar da dakatar da Damagum da dukkan mambobin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar.

Sun kuma bayyana sunan mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na Arewa ta tsakiya, Abdulrahman Mohammed, a matsayin sabon mukaddashin shugaban jam’iyya kasa.

Yayin da bangarorin biyu suke kalubalantar junansu, bangaren da Damagum ke jagoranta ya samu umurnin alkalin babban kotun Jihar Oyo, Ladiran Akintola, wanda ya umartar PDP da ta ci gaba da gudanar da taron babban taronta na kasa.

Saboda haka, yayin da Damagum wanda gwamnoni da mambobin kwamitin amintattu da shugabannin jihohi ke goyon baya ke shirin taron, Wike da Anyanwu da wasu sun dage cewa taron ba zai gudana ba.

A sa’ilin da yake magana da ‘yan jarida a ranar Lahadi, wani jami’i a ofishin PDP mai masaniya kan rikicin, ya ce za a taru da wakilai sama da 3,000 a Ibadan don zaben sabbin shugabanni na jam’iyyar.

Ya ce, “Fiye da wakilai 3,000 ne za su raba gardama, kuma ka da ka manta cewa akwai manyan mukamai da za a zaba.

“Lokacin da ka ji mutane waɗdanda abin da suke sha’awa kawai shi ne hallaka jam’iyya suna cewa ba a gudanar da tarukan jam’iyya a wasu jihohi ba, don haka wadannan jihohin ba su da ‘yancin zabe, karya ne dukkaninsu ne saboda har yanzu muna da tsoffin mambobi a wadannan jihohin.”

Wata majiyar wadda take tare da Damagum, ta ce taron zai gudana saboda umarnin Alkali Akintola wanda shi ne mafi girman hukuncin kotu guda biyu da suka bayar.

Ya kara da cewa, “Akwai umarnin kotu guda biyu daga kotunan da ke sauraron shari’ar. A doka, jam’iyya na da ‘yanci ta zabi wanne daga cikin umarnin za ta bi, yayin da wasu lauyoyi ke cewa umarnin karshe (ko na baya-bayan nan) shi ne mafi inganci tun da an bayar da shi daga babban kotun.”

Ya ce bayan an dakatar da Anyanwu daga shugabancin jam’iyya, an ganshi a matsayin mai jagorantar wata kungiya mai batanci, yana kara da cewa, “Duk wanda ke mai da hankali ga kungiyar yana yin hakan ne saboda dalilai na siyasa.

“A bisa tsarin kundin tsarin mulkin PDP, taron kwamitin gudanarwa yana gudana ne bisa umarnin shugaban jam’iyya na kasa, kuma shugaban jam’iyyar na kasa a wannan yanayin shi ne Umar Damagum.

“Dangane da abin da ke sama, daga cikin mambobin kwamitin gudanarwa guda 17 da suka rage, 14 ne suka gana a ranar 1 ga Nuwamba, 2025, suka dakatar da Anyanwu, Bature, Ajibade, da mataimakin mai ba da shawara na kasa a harkokin shari’a, Okechukwu Onuoha.”

Ya yi kira ga kafofin watsa labarai da su daina kiran bangaren da Wike ke jagoranta a matsayin wata bangare na jam’iyyar. Yana bayyana cewa dole ne a gudanar da babban taron jam’iyyar na kasa, kuma dole ne mambobi su fita a filin taron a wuri daya da rana daya, ba abin da Wike da magoya bayansa za su iya yi.

A halin yanzu, Sanata Anyanwu ya ce taron Ibadan ba zai gudana ba. Ya kara da cewa idan wasu shugabannin jam’iyya suka ci gaba da gudanar da shi, INEC ba za ta sa ido a kai ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tambarin Dimokuradiyya Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya November 7, 2025 Tambarin Dimokuradiyya Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta October 17, 2025 Tambarin Dimokuradiyya 2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara October 17, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  An Amince Da  Sauye-sauye A Tsarin Mulkin Kasar Benin
  • Gwamnatin Gombe ta bai wa alƙalai da Khadi-Khadi kyautar sabbin motoci 16
  • AU ta sake nanata cewa “Babu kisan kare dangi a arewacin Najeriya
  • Ma’ariv: Netanyahu Yana Tsoron Hukuncin  Da Kotu  Za Ta Yanke Akansa
  • Babu Janar ɗin da ISWAP ta kama a Borno — Sojoji
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje
  • ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027
  • Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar
  • Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci
  • Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya