Kwamandan rundunar sojojin kasa ta Iran ya bayyana cewa: Nan ba da jimawa ba za a yaye labulen ire-iren makamai na musamman da Iran ta mallaka

Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran Birgediya Janar Kiomars Heidari ya yi nuni da shirin rufe kan iyakar kasar da ke gabashin Iran, yana mai cewa: Wannan ba kawai wata katanga ba ce mai tsayin mita 4, saboda an tanadar da ita ce da nau’o’in makamai masu kwaloluwar ci gaba na zamani a duniya, wannan shiri an gudanar da shi ne tsawon shekaru hudu kuma za a kammala shi nan da shekaru uku masu zuwa.

Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran ya jaddada haka ne a wani taron manema labarai da ya gudanar a yau Lahadi cewa, yana mai cewa; An bullo da sauye-sauye ne ga tsarin rundunar sojojin kasa baki daya, don ba da damar wuce tsohon tsari saboda kai wa ga tsari na zamani da zai iya tunkarar kalubalen da ake fuskanta a yau.

Birgediya Janar Haidari ya yi jawabi kan muhimman sauye-sauye a cikin tsari da makaman da sojojin kasa suka samar, yana mai cewa, “Sun mayar da bukatu na yau da kullum zuwa wani rundunar kai hari cikin gaggawa mai saurin mayar da martani.

Ya kara da cewa, “Wannan runduna ta mallaki karfin motsawa 100%, da karfin kai hari 100%, da kuma juriya 100%. Don cimma wannan buri, suna bukatar makamai na musamman wadanda ke dauke da wadannan siffofi guda biyu.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi

Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya bayyana cewa jami’an tsaro sun gano wurin da ’yan bindiga suka tsugunar da ɗalibai mata 25 da suka sace daga makarantar kwana ta Maga da ke Jihar Kebbi.

A wani taron manema labarai a Birnin Kebbi, Matawalle ya ce a halin yanzu an tsananta aikin leƙen asiri da tsare-tsare, tare da bayyana cewa ba da jimawa ba za a kuɓutar da ɗaliban cikin nasara, idan komai ya tafi yadda ake so.

An rufe makarantun Filato saboda matsalar tsaro Fiye da yara miliyan 400 na fama da talauci a duniya — UNICEF

Ya nemi goyon bayan al’umma, yana mai cewa, “Haɗin kan jama’a na da matuƙar muhimmanci domin ganin an kammala wannan aiki lafiya lau, tare da dawo da yaran cikin iyayensu ba tare da wata matsala ba.”

A ranar Litinin da ta gabata ne ’yan bindiga suka kai mummunan hari makarantar ta Maga, inda suka yi awon gaba da ɗalibai mata 25, lamarin da ya tayar da hankalin al’umma musamman ma iyayen yaran.

Ministan ya ce tun bayan faruwar lamarin, Gwamnatin Tarayya ta tura ƙarin jami’an tsaro, ciki har da rundunar sojin sama da ta ƙasa, waɗanda ke aiki tare domin gano hanyar shiga ba tare da hallaka ko jikkata ɗaliban ba.

Ya ce, “Mun gano wurin da aka tsare yaran kuma da Yardar Allah za mu ceto su nan ba da jimawa ba. A yanzu haka muna a matakin ɗaukar tsattsauran mataki cikin hikima, domin tabbatar da cewa babu wata illa da za ta same su.”

“Ina kira ga al’ummar Kebbi da su ci gaba da haƙuri da kuma bayar da haɗin kai ga jami’an tsaro. A irin wannan lamari, bayanan sirri daga jama’a na da matuƙar muhimmanci,” in ji shi.

Tinubu ya bai wa Ministan Tsaro umarnin tarewa a Kebbi

A bayan nan ne Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya umarci Ƙaramin Ministan Tsaron da ya koma Jihar Kebbi da aiki sakamakon sace ɗaliban da wasu ’yan bindiga suka yi a jihar.

Tinubu ya umurci Matawalle, wanda tsohon Gwamnan Jihar Zamfara ne, da ya zauna a Kebbi domin sa ido kan dukkan matakan tsaro da ake ɗauka domin kuɓutar da ɗaliban da aka sace.

A cewar mai magana da yawun fadar shugaban ƙasa, Bayo Onanuga wanda ya bayyana umarnin a cikin wata sanarwa da yammacin Alhamis, ana sa ran Matawalle zai isa Birnin Kebbi da safiyar Juma’a.

“Yana da ƙwarewa sosai wajen fuskantar ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane a lokacin da yake gwamnan Jihar Zamfara daga 2019 zuwa 2023,” in ji sanarwar.

“A ranar 26 ga watan Fabrairu, 2021, ’yan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai mata 279 masu shekaru tsakanin 10 da 17 a makarantar kwana ta GGSSS Jangebe, Jihar Zamfara. ’Yan bindigar sun saki dukkan waɗanda suka yi garkuwar da su a ranar 2 ga watan Maris, 2021.”

Aminiya ta ruwaito cewa, shi ma dai Shugaba Tinubu ya ɗage tafiyarsa da aka tsara zuwa Johannesburg, Afirka ta Kudu, da Luanda a ƙasar Angola, domin ci gaba da samun rahotannin tsaro kan satar ɗaliban na Kebbi da kuma harin da aka kai wa masu ibada a cocin Eruku da ke Jihar Kwara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An  Cimma Yarjejeniya A Karshen Taron Kare Muhalli Na Duniya A Kasar Brazil
  • An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi
  • Iran Ta Sanar Da Nada Janar Jahanshashi A Matsayin Kwamandan Dakarun Rudunar Sojin Kasa
  • ’Yan sanda sun daƙile harin ’yan bindiga, sun ceto mutum 25 a Zamfara
  • Rundunar Sojan Iran Tana Cikin Shirin Mayar Da Martani Akan Kowace Barazana
  • Duniyarmu A Yau: Sabon Kuduri Mai Yin Allawadai Da Iran A Hukumat IAEA
  • Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya
  • Rundunar Hadin Gwiwa na Faɗaɗa Bincike Don Ceto Daliban da Aka Sace a Neja
  • Araqchi: Iran Ta Shirya Tsaf Fiye Da Kowanne Lokacin  Musamman Bayan Yakin Kwanaki 12
  • Za a aurar da marayu 200 a Zamfara