Kwamandan rundunar sojojin kasa ta Iran ya bayyana cewa: Nan ba da jimawa ba za a yaye labulen ire-iren makamai na musamman da Iran ta mallaka

Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran Birgediya Janar Kiomars Heidari ya yi nuni da shirin rufe kan iyakar kasar da ke gabashin Iran, yana mai cewa: Wannan ba kawai wata katanga ba ce mai tsayin mita 4, saboda an tanadar da ita ce da nau’o’in makamai masu kwaloluwar ci gaba na zamani a duniya, wannan shiri an gudanar da shi ne tsawon shekaru hudu kuma za a kammala shi nan da shekaru uku masu zuwa.

Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran ya jaddada haka ne a wani taron manema labarai da ya gudanar a yau Lahadi cewa, yana mai cewa; An bullo da sauye-sauye ne ga tsarin rundunar sojojin kasa baki daya, don ba da damar wuce tsohon tsari saboda kai wa ga tsari na zamani da zai iya tunkarar kalubalen da ake fuskanta a yau.

Birgediya Janar Haidari ya yi jawabi kan muhimman sauye-sauye a cikin tsari da makaman da sojojin kasa suka samar, yana mai cewa, “Sun mayar da bukatu na yau da kullum zuwa wani rundunar kai hari cikin gaggawa mai saurin mayar da martani.

Ya kara da cewa, “Wannan runduna ta mallaki karfin motsawa 100%, da karfin kai hari 100%, da kuma juriya 100%. Don cimma wannan buri, suna bukatar makamai na musamman wadanda ke dauke da wadannan siffofi guda biyu.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hisbah ta kama matashi yana ‘baɗala’ da Akuya a Kano

Hukumar Hisbah a Jihar Kano ta cika hannu da wani matashi da aka gani a wani yanayi mai kamanceceniya da baɗala da wata Akuya, lamarin da ya janyo cece-kuce a dandalin sada zumunta.

Matashin, Shamsu Yakubu mai shekaru 24 da ke zaune a Ƙaramar Hukumar Dawakin Tofa ta Kano, ya shiga hannu ne bayan ɓullar wani bidiyonsa a dandalan sada zumunta musamman TikTok yana tsotsar farjin wata Akuya.

Majalisa ta gayyaci Kantoman Ribas, Ibok-Ete Ibas An naɗa mace ta farko mai magana da yawun rundunar sojin Nijeriya

A cikin bidiyon da wani yake ɗaukarsa wanda ya yaɗu sosai a soshiyal midiya, an hasko matashin a wannan yanayin mai kama da baɗala tare da Akuyar.

Sai dai yayin da yake amsa tambayoyin mahukunta, matashin ya yi iƙirarin aikata hakan da nufin neman suna domin samun ɗaukaka ta dandalin sada zumunta.

Wannan lamari da ya fusata mazauna yankin ya sanya suka yi yunƙurin ɗaukar mataki a hannunsu, amma aka yi sa’a wani jami’in Hisbah ya tari hanzarinsu kuma aka cafke shi.

A yayin shan titsiye, matashin ya musanta zargin da ake yi masa, yana rantsuwa da Allah cewa bai tsotsi Akuyar ba.

“Na rantse da Allah ban tsotsi Akuyar ba, bakina kawai na kai kusa da wurin,” a cewarsa.

Matashin ya kuma bayyana cewa wannan shi ne karon farko da ya aikata irin wannan lamari yana mai nadamar cewa ba zai ƙara ba.

Sai dai duk da ya musanta cewa ba ya ta’ammali da miyagun ƙwayoyi ko kayan maye, Hukumar Hisbah ta umarci a yi masa gwajin ƙwaƙwalwa.

Da yake martani kan lamarin, Mataimakin Kwamandan Hisbah, Sheikh Aminuddeen Abubakar, ya yi Allah wadai yana mai cewa wannan abun kunya ya saɓa wa tarbiyya da koyarwar addinin Islama

“Abun takaici ne mutum ɗan Musulmi ya faɗa wannan abun kunya domin neman suna,” in ji Sheikh Aminuddeen.

Haka kuma, ya ce za a kai Akuyar Asibitin Dabbobi domin duba lafiyarta.

Sheikh Aminuddeen ya gargaɗi masu ƙoƙarin neman suna da wallafe-wallafen hofi marasa kan gado.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Tace Yarjeniya Da Amurka Mai Yuwa Ne Idan Da Gaske Take
  • Rundunar ‘Yansanda Ta Tuhumi Jami’anta Da ‘Yan Kasar Sin Ke Raba Wa Kudi A Wani Bidiyo Da Ke Yawo
  • Gwamnatin Trayya Zata Zamantar da Kayayyakin Watsa Labaran ta
  • Hukumar NSCDC ta tura jami’an tsaro 415 domin aikin Easter a Zamfara.
  • Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ta Bada Tabbacin Tsaro A Bukin Ista
  • Jagora: Iran a shirye take domin aiki kafada da kafada tare da  Saudiyya
  • AGILE: Gwamnatin Kaduna da Bankin Duniya Na Sauya Rayuwar ’Ya’ya Mata Ta Hanyar Ilimi
  • Majalisar Kasa Ta Rasha Ta Amince Da Yarjeniyar Dangantaka Ta Musamman Tsakanin Iran Da Kasar
  • Iraki Ce Zata Amfana Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka: Inji Sayyed Ammar Hakim
  • Hisbah ta kama matashi yana ‘baɗala’ da Akuya a Kano