Kwamandan rundunar sojojin kasa ta Iran ya bayyana cewa: Nan ba da jimawa ba za a yaye labulen ire-iren makamai na musamman da Iran ta mallaka

Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran Birgediya Janar Kiomars Heidari ya yi nuni da shirin rufe kan iyakar kasar da ke gabashin Iran, yana mai cewa: Wannan ba kawai wata katanga ba ce mai tsayin mita 4, saboda an tanadar da ita ce da nau’o’in makamai masu kwaloluwar ci gaba na zamani a duniya, wannan shiri an gudanar da shi ne tsawon shekaru hudu kuma za a kammala shi nan da shekaru uku masu zuwa.

Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran ya jaddada haka ne a wani taron manema labarai da ya gudanar a yau Lahadi cewa, yana mai cewa; An bullo da sauye-sauye ne ga tsarin rundunar sojojin kasa baki daya, don ba da damar wuce tsohon tsari saboda kai wa ga tsari na zamani da zai iya tunkarar kalubalen da ake fuskanta a yau.

Birgediya Janar Haidari ya yi jawabi kan muhimman sauye-sauye a cikin tsari da makaman da sojojin kasa suka samar, yana mai cewa, “Sun mayar da bukatu na yau da kullum zuwa wani rundunar kai hari cikin gaggawa mai saurin mayar da martani.

Ya kara da cewa, “Wannan runduna ta mallaki karfin motsawa 100%, da karfin kai hari 100%, da kuma juriya 100%. Don cimma wannan buri, suna bukatar makamai na musamman wadanda ke dauke da wadannan siffofi guda biyu.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

ECOWAS ta jaddada aniyar kare dimokuraɗiyya da inganta tsaro a yammacin Afirka

Ƙungiyar Bunƙasa Tattalin Arziƙin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), ta yi alƙawarin kare dimokuraɗiyya da kuma inganta tsaro a yankin Yammacin Afirka.

Wannan alƙawarin na zuwa ne a dai-dai lokacin da yankin ke fuskantar matsalolin tsaro da na juyin mulki.

Yadda aka yi bikin naɗa Rarara sarkin wakar ƙasar Hausa a Daura Jirgin sama ya yi hatsari yayin sauka a Kano

An yanke wannan shawara ne a taron shugabannin ƙasashen ECOWAS karo na 68, wanda aka gudanar a Abuja a ranar Lahadi.

Shugaba Bola Tinubu, wanda Mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ya wakilta, ya yi kira ga ƙasashen ECOWAS da su zauna lafiya tare da haɗa kai.

Ya yi gargaɗi ncewa ƙungiyar tana samun rauni idan ƙasashe suka rabu.

Ya ce ƙasashen Yammacin Afirka ba wai waje ɗaya suka haɗa ba, face suna da tarihi, al’adu da gwagwarmaya iri ɗaya da ta haɗa su.

Shugaba Tinubu, ya bayyana cewa duk da cewa rashin jituwa na iya faruwa tsakanin ƙasashe, bai kamata hakan ya karya zumunci da makomar ƙasashen yankin ba.

Ya zayyano matsalolin da yankin ke fuskanta, kamar ta’addanci, rikice-rikice, tsattsauran ra’ayi, juyin mulki, laifukan ƙetare iyaka, yawaitar makamai, barazana a Intanet, sauyin yanayi, ƙarancin abinci da sauransu.

Ya ce waɗannan matsaloli ba su da iyaka, kuma ƙasa ɗaya ba za ta iya magance su ba.

Tinubu ya tarbi shugabannin ECOWAS zuwa Abuja, inda ya yi fatan taron zai ƙara amincewa da juna, ƙarfafa haɗin kai, tare da sake ɗora ECOWAS bisa ginshiƙan adalci da makoma ɗaya.

A yayin taron, ECOWAS ta kuma mayar da hankali kan bunƙasar tattalin arziƙi ta hanyar kamfanoni masu zaman kansu.

Shugaban Hukumar ECOWAS, Dokta Omar Alieu Touray, ya sanar da kafa Majalisar Kasuwanci ta ECOWAS.

An naɗa fitaccen ɗan kasuwan Najeriya, Alhaji Aliko Dangote, a matsayin shugaban farko na wannan majalisa.

Shugaban ƙasar Saliyo kuma Shugaban ECOWAS, Julius Maada Bio, ya bayyana taron a matsayin mai muhimmanci.

Ya ce yankin Yammacin Afirka na fuskantar manyan ƙalubale na tsaro, dimokuraɗiyya da tattalin arziƙi, kuma shawarwarin da za a yanke za su shafi sama da mutum miliyan 400.

Ya kuma bayyana cewa an yi murnar cikar ECOWAS shekaru 50 da kafuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ECOWAS ta jaddada aniyar kare dimokuraɗiyya da inganta tsaro a yammacin Afirka
  • Buɗe cibiyar horas da sabbin sojoji a Kudu zai taimaka — Janar Shaibu
  • Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman
  • ’Yan sanda sun ba da tabbacin isasshen tsaro a zaɓen ƙananan hukumomin Borno
  • Farfesa na Farko a fannin Ilimi a Arewa, Adamu Baikie, ya rasu yana da shekara 94
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare
  • Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”
  • Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su