Iran Zata Yaye Labulen Ire-Iren Makamanta Na Musamman Da Ta Mallaka Domin Kare Kai
Published: 13th, April 2025 GMT
Kwamandan rundunar sojojin kasa ta Iran ya bayyana cewa: Nan ba da jimawa ba za a yaye labulen ire-iren makamai na musamman da Iran ta mallaka
Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran Birgediya Janar Kiomars Heidari ya yi nuni da shirin rufe kan iyakar kasar da ke gabashin Iran, yana mai cewa: Wannan ba kawai wata katanga ba ce mai tsayin mita 4, saboda an tanadar da ita ce da nau’o’in makamai masu kwaloluwar ci gaba na zamani a duniya, wannan shiri an gudanar da shi ne tsawon shekaru hudu kuma za a kammala shi nan da shekaru uku masu zuwa.
Kwamandan rundunar sojin kasa ta Iran ya jaddada haka ne a wani taron manema labarai da ya gudanar a yau Lahadi cewa, yana mai cewa; An bullo da sauye-sauye ne ga tsarin rundunar sojojin kasa baki daya, don ba da damar wuce tsohon tsari saboda kai wa ga tsari na zamani da zai iya tunkarar kalubalen da ake fuskanta a yau.
Birgediya Janar Haidari ya yi jawabi kan muhimman sauye-sauye a cikin tsari da makaman da sojojin kasa suka samar, yana mai cewa, “Sun mayar da bukatu na yau da kullum zuwa wani rundunar kai hari cikin gaggawa mai saurin mayar da martani.
Ya kara da cewa, “Wannan runduna ta mallaki karfin motsawa 100%, da karfin kai hari 100%, da kuma juriya 100%. Don cimma wannan buri, suna bukatar makamai na musamman wadanda ke dauke da wadannan siffofi guda biyu.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Olisa Metuh ya sauya sheƙa zuwa APC, ya ce PDP ta manta da shi
Tsohon mai magana da yawun jam’iyyar PDP na ƙasa, Olisa Metuh, ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC mai mulki.
Ya ce ya yanke wannan shawara ne saboda PDP ta kasa goyon bayansa lokacin da yake cikin matsaloli.
Sojoji sun ceto ’yan mata 12 da ISWAP suka sace a Borno ’Yan bindiga sun sace amarya da ƙawenta 14 a SakkwatoMetuh, ya daina shiga harkokin siyasa kusan shekaru uku da suka wuce, ya amma ya dawo siyasa ne ta hanyar sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki.
Ya bayyana hakan ne a lokacin bikin cikarsa shekaru 60 a duniya, wanda ya gudana a Abuja.
Manyan ’yan siyasa da dama sun halarci taron, ciki har da gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma, tsohon shugaban Majalisar Dattawa, Anyim Pius Anyim, da tsoffin gwamnonin Abiya, Ebonyi da Imo.
Da yake magana da ’yan jarida bayan taron, Metuh, ya ce yana son ya taimaka wajen ci gaban Najeriya ta hanyar komawa APC.
Ya ce Najeriya na fuskantar ƙalubale, kuma yana son ya bayar da gudummawarsa a aikace.
Ya ce: “Lokacin da na shiga matsala, ban ga jam’iyyata ba. Na kasance a kotu tare da iyalina kawai.
“Amma Shugaba Tinubu, wanda nake suka a kai a kai, shi ne ya turo Femi Gbajabiamila ya zo ya duba ni ya kwantar min da hankali.”
Ya ce yana yi wa PDP fatan alheri, amma zai ci gaba da rayuwarsa ba tare da ita ba.
Haka kuma ya bayyana cewa har yanzu akwai jagorori masu ƙarfi a tsagin ’yan adawa, don haka Najeriya ba za ta zama ƙasa mai jam’iyya guda ɗaya ba.
Metuh, ya ƙara da cewa Shugaba Tinubu ya sha yi masa tayin shiga APC, amma ya ƙi amincewa.
A cewarsa: “Shugaban ƙasa ya so na jam’iyyarsa tun 2015. Har bayan da na daina siyasa a 2022, ya sake gayyata ta, amma na ki. Yanzu da na koma siyasa, ina son na taimaka wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya.”